Leadership News Hausa:
2025-05-14@21:09:47 GMT

An Harbe Mutumin da Ya Ƙona Al-Ƙur’ani A Sweden

Published: 30th, January 2025 GMT

An Harbe Mutumin da Ya Ƙona Al-Ƙur’ani A Sweden

Mista Momika ya yi zanga-zanga da dama da ke nuna ƙin jinin Musulunci, lamarin da ya haddasa bore a ƙasashe da dama.

A lokacin da ya ƙona Al-ƙur’ani, an yi bore a ofishin jakadancin Sweden da ke Bagadaza, inda aka kori jakadan ƙasar daga birnin.

Gwamnatin Sweden ta ce ta ba shi izinin yin zanga-zangar, bisa hujjar cewa yana da ‘yancin faɗar albarkacin baki, kamar yadda dokar ƙasar ta tanada.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Salwan Momika

এছাড়াও পড়ুন:

Zabe Babu Hamayya: Isma’il Dutse Ya Karbi Ragamar NUJ Jigawa

An zabi Comrade Isma’il Ibrahim Dutse na ma’aikatar yada labarai a matsayin sabon shugaban kungiyar ‘yan jaridu NUJ ta kasa reshen jihar Jigawa ba tare da hamayya ba.

A lokacin da yake sanar da sakamakon zaben, mataimakin shugaban kungiyar na kasa mai kula da shiyya ta daya wato Zone A, Comrade Tukur Umar Muhammad ya ce an kuma zabi Nura Sani Bello da Najib Umar da Aminu Umar Shuwajo ba tare da hamayya ba.

Tukur ya ce Aisha Abba Ahmed ta kamfanin dillancin labarai na kasa NAN dake Dutse ta samu nasara da yawan kuri’u 46, shi kuma Abdullahi Mukhtar ya sami kuri’u 34, yayin da Larai Musa na NTA ta sami kuri’u 14.

Tukur Umar, ya bayyana Aisha Abba Ahmed a matsayin wacce ta sami nasara a zaben da ta zamo sakatariyar kungiyar NUJ a jihar Jigawa.

Kazalika, Auwal Muhammad Kazaure ya samu nasara da kuri’u 69 akan Habibu Yusuf Adamu Babura wadda ya sami kuri’u 27.

 

 

A don haka, Mataimakin Shugaban na NUJ ya bayyana Auwal Muhammad Kazaure a matsayin ma’ajin kungiyar.

Sakataren kungiyar na shiyyar Zone A, Comrade Abdulrazak Bello Kaura ne ya rantsar da sabbin shugabannin nan take.

A jawabinsa, sabon shugaban kungiyar NUJ reshen jihar Jigawa, Isma’il Ibrahim Dutse ya bayyana zaben sa ba tare da hamayya ba a matsayin wani babban karimci da aka nuna masa.

Ya kuma yabawa masu ruwa da tsaki ciki har da Gwamna Umar Namadi bisa gudummawar da su ka bayar wajen samun nasarar zaben da aka gudanar cikin kwanciyar hankali da lumana.

Wakilinmu ya aiko mana da rahoton cewar, wadanda su ka halarci taron, sun hada da kwamishinan yada labarai, al’adu da matasa, Alhaji Sagir Musa Ahmed, da tsoffin shugabannin kungiyar, Alhaji Sabo Abdullahi Guri da Alhaji Mati Ali da wakilan sakataren Gwamnati da na shugaban ma’aikata da kuma Shugaban gidan Radiyon Tarayya Horizon FM, Dr Musa Idris Barnawa.

Kungiyar dai ta gudanar da taro karo na 8 wanda ya wakana a sakatariyar kungiyar da ke Dutse, babban birnin jihar.

Bayan kammala zaben, Shugabannin Kungiyar ta kasa, sun kai ziyarar ban girma gidan gwamnatin jihar domin gabatar da sabbin shugabannin kungiyar na jihar ga babban jami’in yada labarai na Gwamnan Jihar, Hamisu Mohammed Gumel.

 

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ta Iran Ya Jaddada Bukatar Hukunta Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Aiwatar Da Kisan Kiyashi Kan Falasdinawa A Gaza
  • Majalisar Dattawa ta buƙaci a tura ƙarin sojoji zuwa Borno da Yobe
  • Mali : An rushe dukkan jam’iyyun siyasa a hukumance
  • Iran ta yi Allah wadai da harin da Isra’ila ta kai kan sansanonin ‘yan gudun hijirar Falasdinu
  • Zabe Babu Hamayya: Isma’il Dutse Ya Karbi Ragamar NUJ Jigawa
  •  Falasdinawa Da Dama Sun Yi Shahada A Yau Talata
  • Bom ya kashe jami’an ilimi 2 a Borno
  • Yadda ISWAP ta kashe sojoji ta kwashe makamai a sansanin soji a Borno
  • ’Yan bindiga sun yi awon gaba da mutum 5 a Filato