Falasdinawa 1500 Ne Su Ka Zama Makafi Sanadiyyar Yaki
Published: 12th, May 2025 GMT
Shugaban Asibitin ido dake Gaza, Dr. Abdussalam Sabah, ya sanar da cewa, adadin Falasdinawan da su ka rasa ganinsu sanadiyyar yaki sun kai 1500.
Dr. Abdussalam ya kuma yi gargadin cewa da akwai wasu Falasdinawa da sun kai 4000 da suke fuskantar barazanar rasa idanunsu saboda rashin kayan aiki a asibiti da kuma magani.
Likitan na asibitin idanun Gaza, ya kara da cewa; Rashin kayan aiki a asibitin domin yin tiyatar ido, yana yin barazanar tsayuwar aikin asibitin baki daya.
Dr. Abdussalam ya kara da cewa; A halin yanzu almakashi 3 kadai ake da shi a asibitin, irin wanda ake amfani da shi domin yin tiyatar ido.
Da dama daga cikin masu lalurar idanun sun same ta ne sanadiyyar fashewar abubuwa masu karfi na hare-haren HKI dake da bukayuwa da kayan aiki na musamman.
Haka nan kuma ya ce, matukar kungiyoyin kasa da kasa ba su tsoma baki ba, to nan gaba kadan Asibitin zai sanar da durkushewarsa.
A wani labarin mai alaka da wannan, ma’aikatar kiwon lafiya ta Gaza ta sanar da cewa, da akwai karancin magunguna a yankin,kuma wadanda ma su ka saura suna ci gaba da yin kasa sosai.
Har ila yau ta ce, da akwai nau’oin da sun kai kaso 65% na magunguna da babu ko da kwaya daya da ya saura. Haka nan muhimman magununan da ake da bukatuwa da su a cikin yankin sun kare kakaf da kaso43%.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp