Aminiya:
2025-09-24@12:41:43 GMT

An kama mutum 78 da makamai da kwayoyi a Kano

Published: 9th, May 2025 GMT

An kama mutane 78 tare da kwace tulin miyagun kwayoyi da makamai da kayan sata a wani samame da ’yan sanda suka kai kwanan nan domin ayyukan laifi a Jihar Kano.

A yayin samamen, an kama gawurtaccen dillalin miyagun kwayoyi, Sulaiman Danwawu, da wasu haramtattun kwayoyi bayan an taba kama shi a shekarar 2022.

Daga cikin sauran wadanda aka kama har da wani da ake zargin dan fashi da makami ne da bindigogi biyu da harsasai.

Kwamishinan ’yan sanda, Ibrahim Adamu Bakori, ya sanar a taron ’yan jarida da ya gudana a hedikwatar rudunar da ke Bompai a ranar Juma’a cewa aikin kamen ya yi daidai da umarnin Shugaban ’Yan Sanda na Kasa kan a aiwatar da ingantattun matakai domin dakile ayyukan laifi.

Nijeriya ta soke ba da tallafin karatu a ƙetare Yadda yara 5 suka mutu a cikin motar da aka yi watsi da ita Yadda rashin wutar lantarki ke ajalin rayuka a manyan asibitoci

Ya bayyana cewa hnyoyin da rundunarsa ta yi amfani da su sun hada da sintiri na sa’o’i 24, kai samame bisa bayanan sirri, da kuma hadin gwiwa da al’umma.

Tsakanin 23 ga Afrilu zuwa 9 ga Mayu, ’yan sanda sun kama mutane biyar bisa zargin fashi da makami, bakwai bisa zargin sayar da miyagun kwayoyi, da wasu bisa zargin satar shanu, damfara, sata, da kuma ‘yan daba.

Kayayyakin da aka kwato sun hada da bindigogi, miyagun kwayoyi, motoci, babura mai kafa uku, babura, muggan makamai, kudin jabu, dabbobi, da kayan lantarki.

Kwamishina Bakori ya jaddada alakar da ke tsakanin safarar miyagun kwayoyi da aikata laifuka masu hadari, yana mai cewa kama mutanen da kwace kayayyakin sun nuna irin nasarar da ake samu wajen rage irin wadannan laifuka.

Ya bukaci al’umma da su ba da goyon baya ta hanyar bayar da sahihan bayanai domin tabbatar da zaman lafiya a Kano.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda kwayoyi miyagun kwayoyi

এছাড়াও পড়ুন:

An ƙona al’aurar ’yar shekara 5 saboda fitsarin kwance a Bauchi

Ana zargin wata matar aure, Rabi Nuhu da ke garin Magama Gumau a ƙaramar hukumar Toro ta Jihar Bauchi, da cin zarafin wata yarinya ’yar shekara biyar ta hanyar ƙone mata al’aura, saboda zargin tana yawan yin fitsarin kwance.

Wakilinmu ya gano cewa yarinyar marainiya ce wadda mahaifiyarta ta rasu kusan shekara ɗaya da ta gabata, inda take zaune tare da mahaifinta, Mohammed Umar, da matarsa.

CBN ya rage kuɗin ruwa zuwa kashi 27 cikin 100 Mahara sun kashe ɗan sanda sun ɗauke bindigarsa a Taraba

Wani mai fafutukar kare haƙƙin bil’adama a garin, Kabiru Abdulkadir, ya bayyana cewa sai bayan kwana biyar da ƙonewar ta faru ne al’amarin ya bayyana.

“Don guje wa matsala, mahaifin yarinyar ya sayi wata katifa ta daban domin ta riƙa kwanciya a kai, amma duk da haka matar tasa ba ta daina azabtar da yarinyar ba,” in ji Kabiru.

Aminiya ta ruwaito cewa, lamarin ya bayyana ne lokacin da yarinyar ta roƙi kawunta ya saya mata katifa, inda ta shaida masa cewa mamanta ta ƙona al’aurarta saboda yawan fitsarin kwance, dalili ke nan da ya yi wa ’yan sanda ƙorafi.

Kazalika, ana zargin cewa duk lokacin da matar ta samu sabani da mijinta, sai ta huce fushi a kan yarinyar.

Da yake jawabi, mahaifin yarinyar, Mohammed Umar, wanda ke aiki da wani gidan talabijin, ya tabbatar da cewa matarsa ta kan yi ƙorafi kan yawan fitsarin kwancen yarinyar, abin da ya sa ya saya mata katifa ta daban.

Umar ya ce: “A farko, da na ga ƙuna a jikinta, matata ta shaida min wai shayi mai zafi ne ya zubo a jikinta. A lokacin na gaskata hakan, har sai da na lura da ciwon yana ƙaruwa.”

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi, CSP Mohammed Wakil, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa rahoto ya iso ofishin su da misalin ƙarfe 3:00 na ranar 13 ga Satumba, 2025.

Wakil ya ce yarinyar ta sami ƙonuwa a ƙasan cikinta, cinyoyinta, da kuma al’aurarta.

Ya ƙara da cewa, kwamishinan ‘yan sanda na jihar, Sani Omolori Aliyu, ya bayar da umarnin a gaggauta kama matar tare da miƙa ta zuwa sashen manyan laifuka domin gudanar da cikakken bincike.

Ya bayyana cewa da zarar an kammala binciken, za a gurfanar da ita a gaban kotu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kama Tsohon Ɗan Wasan Super Eagles, Victor Ezeji, Kan Zargin Aikata Zambar ₦39.8m
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutum 4,383, Sun Ceto 1,138 Daga Hannun Mahara Cikin Wata 3
  • Kotun Indiya ta daure dan Najeriya shekara 10 kan safarar miyagun kwayoyi
  • An kama ɗan sandan bogi a Kano
  • An yi wa sojoji ɗaurin rai da rai kan sayar wa ’yan ta’adda makamai a Borno
  • An Kama Ɗansandan Bogi A Kano
  • An ƙona al’aurar ’yar shekara 5 saboda fitsarin kwance a Bauchi
  • ’Yan sanda sun kama mutum 4 kan kai wa Lakurawa babura a Kebbi
  • Hisbah ta kama masu safarar mata zuwa Saudiyya a Kano
  • ’Yan sanda sun kama mutane 5 kan zargin satar abincin yara a Borno