An kama mutum 78 da makamai da kwayoyi a Kano
Published: 9th, May 2025 GMT
An kama mutane 78 tare da kwace tulin miyagun kwayoyi da makamai da kayan sata a wani samame da ’yan sanda suka kai kwanan nan domin ayyukan laifi a Jihar Kano.
A yayin samamen, an kama gawurtaccen dillalin miyagun kwayoyi, Sulaiman Danwawu, da wasu haramtattun kwayoyi bayan an taba kama shi a shekarar 2022.
Daga cikin sauran wadanda aka kama har da wani da ake zargin dan fashi da makami ne da bindigogi biyu da harsasai.
Kwamishinan ’yan sanda, Ibrahim Adamu Bakori, ya sanar a taron ’yan jarida da ya gudana a hedikwatar rudunar da ke Bompai a ranar Juma’a cewa aikin kamen ya yi daidai da umarnin Shugaban ’Yan Sanda na Kasa kan a aiwatar da ingantattun matakai domin dakile ayyukan laifi.
Nijeriya ta soke ba da tallafin karatu a ƙetare Yadda yara 5 suka mutu a cikin motar da aka yi watsi da ita Yadda rashin wutar lantarki ke ajalin rayuka a manyan asibitociYa bayyana cewa hnyoyin da rundunarsa ta yi amfani da su sun hada da sintiri na sa’o’i 24, kai samame bisa bayanan sirri, da kuma hadin gwiwa da al’umma.
Tsakanin 23 ga Afrilu zuwa 9 ga Mayu, ’yan sanda sun kama mutane biyar bisa zargin fashi da makami, bakwai bisa zargin sayar da miyagun kwayoyi, da wasu bisa zargin satar shanu, damfara, sata, da kuma ‘yan daba.
Kayayyakin da aka kwato sun hada da bindigogi, miyagun kwayoyi, motoci, babura mai kafa uku, babura, muggan makamai, kudin jabu, dabbobi, da kayan lantarki.
Kwamishina Bakori ya jaddada alakar da ke tsakanin safarar miyagun kwayoyi da aikata laifuka masu hadari, yana mai cewa kama mutanen da kwace kayayyakin sun nuna irin nasarar da ake samu wajen rage irin wadannan laifuka.
Ya bukaci al’umma da su ba da goyon baya ta hanyar bayar da sahihan bayanai domin tabbatar da zaman lafiya a Kano.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda kwayoyi miyagun kwayoyi
এছাড়াও পড়ুন:
Najeriya ta tura sojoji domin samar da zaman lafiya a Gambia
Najeriya ta tura sojojinta 197 domin zuwa aikin tabbatar da tsaro da wanzar da zaman lafiya a kasar Gambia.
Dakarun na Najeriya waɗanda tuni suka kammala samun horo, za sai yi aikin wanzar da zaman lafiya a Gambia be a ƙarƙashin rundunar Ƙungiyar Tattalin Arzikin Yammacin Afirka (ECOWAS) da sunan (ECOMIG).
Shugaban Ayyuka na Rundunar Sojin Ƙasa ta Najeriya, Manjo-Janar Uwem Bassey, ya buƙaci sojojin da su kasance masu nuna nuna ƙwarewa da jarumta a yayin gudanar da ayyukansu a ƙasar Gambia.
Ya yi wannan kira ne a jawabinsa a wurin bikin yaye sojojin a Barikin Sojoji na Jaji da ke Jihar Kaduna, kafin tafiyarsu.
Yadda Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ila An sallami ƙarin ma’aikata 639 a tashar Muryar AmurkaManjo-Janar Bassey ya buƙaci sojojin da su guji nuna son kai, su mutunta hakkokin ɗan Adam da kuma dokoki da al’adun al’ummar Gambia.
Ya gargaɗe su game da cin zarafi musamman na jinsi, tare da cewa duk sojan aka samu da laifi zai gamu da tsauraran matakan ladabtarwa.
Bassey ya bayyana cewa Najeriya tana da dogon tarihi na bayar da gudummawa ga ayyukan wanzar da zaman lafiya na ƙasar da ƙasa, inda sojojinta ke samun karɓuwa a duniya saboda jaruntakarsu, da ƙwarewarsu.
Sojojin Najeriya sun taka muhimmiyar rawa wajen dawo da zaman lafiya a rikice-rikicen da aka samu a faɗin Afirka da ma duniya, ciki har da Lebanon da Yugoslavia da Laberiya, Saliyo, da Sudan, inda suka ci gaba da samun yabo saboda jaruntakarsu da ƙwarewarsu.