An zabi Comrade Isma’il Ibrahim Dutse na ma’aikatar yada labarai a matsayin sabon shugaban kungiyar ‘yan jaridu NUJ ta kasa reshen jihar Jigawa ba tare da hamayya ba.

A lokacin da yake sanar da sakamakon zaben, mataimakin shugaban kungiyar na kasa mai kula da shiyya ta daya wato Zone A, Comrade Tukur Umar Muhammad ya ce an kuma zabi Nura Sani Bello da Najib Umar da Aminu Umar Shuwajo ba tare da hamayya ba.

Tukur ya ce Aisha Abba Ahmed ta kamfanin dillancin labarai na kasa NAN dake Dutse ta samu nasara da yawan kuri’u 46, shi kuma Abdullahi Mukhtar ya sami kuri’u 34, yayin da Larai Musa na NTA ta sami kuri’u 14.

Tukur Umar, ya bayyana Aisha Abba Ahmed a matsayin wacce ta sami nasara a zaben da ta zamo sakatariyar kungiyar NUJ a jihar Jigawa.

Kazalika, Auwal Muhammad Kazaure ya samu nasara da kuri’u 69 akan Habibu Yusuf Adamu Babura wadda ya sami kuri’u 27.

 

 

A don haka, Mataimakin Shugaban na NUJ ya bayyana Auwal Muhammad Kazaure a matsayin ma’ajin kungiyar.

Sakataren kungiyar na shiyyar Zone A, Comrade Abdulrazak Bello Kaura ne ya rantsar da sabbin shugabannin nan take.

A jawabinsa, sabon shugaban kungiyar NUJ reshen jihar Jigawa, Isma’il Ibrahim Dutse ya bayyana zaben sa ba tare da hamayya ba a matsayin wani babban karimci da aka nuna masa.

Ya kuma yabawa masu ruwa da tsaki ciki har da Gwamna Umar Namadi bisa gudummawar da su ka bayar wajen samun nasarar zaben da aka gudanar cikin kwanciyar hankali da lumana.

Wakilinmu ya aiko mana da rahoton cewar, wadanda su ka halarci taron, sun hada da kwamishinan yada labarai, al’adu da matasa, Alhaji Sagir Musa Ahmed, da tsoffin shugabannin kungiyar, Alhaji Sabo Abdullahi Guri da Alhaji Mati Ali da wakilan sakataren Gwamnati da na shugaban ma’aikata da kuma Shugaban gidan Radiyon Tarayya Horizon FM, Dr Musa Idris Barnawa.

Kungiyar dai ta gudanar da taro karo na 8 wanda ya wakana a sakatariyar kungiyar da ke Dutse, babban birnin jihar.

Bayan kammala zaben, Shugabannin Kungiyar ta kasa, sun kai ziyarar ban girma gidan gwamnatin jihar domin gabatar da sabbin shugabannin kungiyar na jihar ga babban jami’in yada labarai na Gwamnan Jihar, Hamisu Mohammed Gumel.

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

Saraki, shi ne zai jagoranci kwamitin sai kuma ƴan kwamitin da suka haɗa da gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare; gwamnan jihar Filato, Caleb Muftiwang da kuma gwmanan jihar Enugu, Peter Mba.

 

Sauran ƴan kwamitin sun haɗa da Sanata Seriake Dickson da Sanata Ibrahim Dankwambo da tsohon gwamnan jihar Abia, Chif Okezie Ikpeazu.

 

Waɗanda suka halarci taron sun haɗa da gwamnonin Enugu da Zamfara da Adamawa da Taraba da Osun da Oyo.

 

Ministan babban birnin tarayya Abuja kuma tsohon gwamnan jihar Ribas, Nyeson Wike shima ya je taron sai kuma tsohon gwamnan jihar Kaduna, Ahmed Maƙarfi.

 

Suma ƴan jam’iyyar irin su Sanata Aminu Waziri Tambuwal da Sule Lamido da Samuel Ortom da Gabriel Suswan da Seriake Dickson da Sam Egwu da Liyel Imoke da Achike Udenwa da Olagunsoye Oyinlola da Adamu Muazu da kuma Idris Wada duka sun halarci taron.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisa ta yi watsi da kudurin dokar mulkin karba-karba
  • Shugaban Kungiyar Hizbulla Ya Ce Cewa Kungiyarsa Ba Zata Taba Mika Kai Ga Bukatun HKI Ba
  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Matsayin Kasarsa Na Rashin Sallama Hakkinta Na Makamashin Nukiliya
  • Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Matsayin Kasarsa Na Tattaunawa Da Amurka
  • Shugaba Tinubu Ya Rantsar Da Sabbin Kwamishinonin Hukumar INEC
  • Hajjin 2025: Rukunin Farko Na Alhazan Jihar Kwara Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
  •  Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 
  • 2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC
  • Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu