Leadership News Hausa:
2025-06-27@05:24:52 GMT

He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

Published: 13th, May 2025 GMT

He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

Mataimakin firaminsitan kasar Sin He Lifeng, ya gana da babbar jami’ar hukumar kula da cinikayya ta duniya (WTO) Ngozi Okonjo-Iweala, a daren jiya Lahadi a Geneva.

Yayin ganawar tasu, He ya ce, kamata ya yi mabambantan bangarori su daidaita bambancin ra’ayi da takaddama bisa shawarwari, kuma cikin adalci karkashin ka’idar WTO.

Haka kuma, a hada hannu wajen kiyaye manufar daidaita harkoki tsakanin mabambantan bangarori da yin ciniki cikin ’yanci, don gudanar tsarin sana’o’i da na samar da kayayyaki a duniya yadda ya kamata. Ya ce Sin za ta ci gaba da taka rawa cikin kwaskwarimar da za a yiwa WTO a dukkan fannoni, kuma tana goyon bayan WTO ta bayar da gudunmawa a matsayin mai ba da tabbaci ga raya ciniki a duniya, da kiyaye muradun kasashe masu tasowa har da kara ba da gudunmawa a bangaren tinkarar tarin kalubalen duniya.

A nata bangare, Iweala ta ce, dole ne mambobin WTO su kare tsarin ciniki tsakanin mabambantan bangarori bisa tushen bude kofa da ka’idar hukumar, da ma kara tuntubar juna da ingiza hadin gwiwarsu a bangaren ciniki a duniya, ta yadda WTO za ta bayar da karin gudunmawa wajen hanzarta yin ciniki cikin ’yanci da dunkulewar harkokin ciniki a duniya. (Amina Xu)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa

Firaministan kasar Sin Li Qiang ya ce, kasarsa a shirye take ta rarraba fasahohinta na ainihi, da dabarunta na kirkire-kirkire tare da sauran sassan kasa da kasa. Li Qiang ya bayyana hakan ne cikin jawabinsa na bude taron shekara-shekara, na sabbin jagorori karo na 16, wato dandalin tattalin arzikin duniya na lokacin zafi na Davos a takaice, wanda aka bude yau Laraba a birnin Tianjin na kasar Sin.

Li ya kara da cewa, Sin na da karfin gwiwa, da ikon wanzar da ci gaban tattalin arzikinta, tana kuma kara kaimin zama kasa mai babban matsayin samun kudin shiga, yayin da ake kara daga matsayin sayayya bisa kyakkyawan yanayi a kasar, wadda ita ce ta biyu a girman kasuwar sayayya a duniya.

Firaministan na Sin ya kuma yi kira ga kasashen duniya, da su aiwatar da managartan matakan bunkasa hadin gwiwa a fannonin raya tattalin arziki da cinikayya. Ya ce hakan na nufin rungumar matakai na hakika, don kare tsarin cinikayya cikin ’yanci, da cudanyar mabanbantan sassa, da goya baya ga daidaitaccen tsarin raya tattalin arzikin duniya. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sheikh Dahiru Bauchi ya cika shekara 101 a duniya
  • Gwamnatin Katsina ta amince da ƙidayar almajirai, makarantun Islamiyya
  • Gwamnatin Katsina ta amince da ƙidayar almajirai da makarantun Islamiyya
  • Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara
  • Gwamnatin Neja ta rufe Jami’ar IBB bayan ɓarkewar rikici
  • Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa
  • Shawarar Gudanar Da Harkokin AI Na Duniya Na Jagorantar Ci Gaban Wayewar Kan Dan Adam Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani
  • Nazarin CGTN: Neman Kashe Kaso 5 Na GDP Kan Tsaro Ya Nuna Rashin Dabara Na NATO
  • Bello Turji ya kashe ’yan sa-kai sama da 40 a Zamfara
  • Bejjo Turji ya kashe ’yan sa-kai sama da 40 a Zamfara