He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala
Published: 13th, May 2025 GMT
Mataimakin firaminsitan kasar Sin He Lifeng, ya gana da babbar jami’ar hukumar kula da cinikayya ta duniya (WTO) Ngozi Okonjo-Iweala, a daren jiya Lahadi a Geneva.
Yayin ganawar tasu, He ya ce, kamata ya yi mabambantan bangarori su daidaita bambancin ra’ayi da takaddama bisa shawarwari, kuma cikin adalci karkashin ka’idar WTO.
A nata bangare, Iweala ta ce, dole ne mambobin WTO su kare tsarin ciniki tsakanin mabambantan bangarori bisa tushen bude kofa da ka’idar hukumar, da ma kara tuntubar juna da ingiza hadin gwiwarsu a bangaren ciniki a duniya, ta yadda WTO za ta bayar da karin gudunmawa wajen hanzarta yin ciniki cikin ’yanci da dunkulewar harkokin ciniki a duniya. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
An Yi Allah Wadai Da Hana Amfani Da Hijabi A Jami’ar LandMark, Omu-Aran Kwara
Kungiyar Muslim Media Watch Group ta Najeriya ta yi Allah-wadai da wata sanarwa da ake zargin Bishop David Oyedepo kan amfani da hijabi da daliban Musulman Jami’ar Landmark ta Omu-Aran ta Jihar Kwara suka yi.
A cikin wata sanarwa dauke da sa hannun wakilinta na kasa Sheikh Abu Sheriff, kungiyar ta yi Allah wadai da Bishop David Oyedepo da take hakkin dalibai musulmi da ma’aikatan cibiyar da ke da hakkin dan Adam kamar yadda sashe na 38 na kundin tsarin mulkin Najeriya ya tabbatar.
A cewarsa a cikin wani faifan bidiyo da aka yada sosai, Oyedepo ya yi kira ga iyaye da masu kula da Musulmai da su janye ‘ya’yansu mata idan suka dage ba za ayi amfani da hijabi ba.
Kungiyar ta bayyana dokar hana amfani da hijabi a jami’ar Landmark Omu-Aran a matsayin ‘wani abin da ba za a lamunta dashi ba’ kuma tauye hakkin addini ne.
Ya yi nuni da cewa ba a daukar musulmi aiki a wannan jami’a, kuma idan aka dauki shi bisa kuskure, to ba za su barshi yin salloli sau 5 ko azumin watan Ramadan ba.
Kungiyar ta ci gaba da cewa haramta wa dalibai musulmi ‘yancin yin amfani da hijabi cin zarafi ne ga ‘yancin yin imani da ibadarsu.
Sanarwar ta bayyana cewa neman iyaye da su janye ‘ya’yansu saboda amfani da Hijabi yana tauye musu hakkinsu na dan Adam.
Kungiyar ta kuma yi kira ga ma’aikatar ilimi ta tarayya, NUC, NBTE da sauran su da su binciki duk masu take hakkin dan adam a cibiyoyin ilimi a fadin kasar nan.
REL/ALI MUHAMMAD RABIU