Aminiya:
2025-06-16@01:36:01 GMT

Gwamnan Filato ya kori kwamishinoni 5

Published: 30th, January 2025 GMT

Gwamnan Jihar Filato, Caleb Mutfwang, ya kori kwamishinoni guda biyar daga muƙamansu.

Wannan ma cikin wata sanarwa da Sakataren Gwamnatin Jihar, Architect Samuel Jatau, ya fitar da yammacin ranar Alhamis.

Ɓarayin dabobbi sun shiga hannu, an ƙwato awaki 85 a Gombe Ana biyan wasu kuɗi don kare gwamnatin Tinubu — El-Rufai

Sanarwar ta bayyana cewa sauke kwamishinonin na daga cikin matakan da gwamnatin jihar ta ɗauka, sai dai ba a bayyana dalilin korarsu ba.

Sanarwar ta bayyana cewa korar kwamishinonin ba zai rasa nasaba da gudanar da aikinsu yadda ya kamata ba, musamman ganin yadda suka kwashe shekara guda wajen gudanar da ayyukansu.

A cewar wata majiya, gaza yin aiki yadda ya kamata ne ya sa aka cire su daga muƙamansu.

Kwamishinonin da aka sauke sun haɗa da: Chrysanthus Dawam, wanda ke riƙe da ma’aikatar kasafin ku6di da tsara tattalin arziƙi, Noel Nkup, wanda ke jagorantar ma’aikatar matasa da wasanni.

Ragowar sun haɗa da Jamila Tukur, Kwamishinar ma’aikatar yawon buɗe ido, Obed Goselle, wanda ke kula da ma’aikatar kimiyya da ƙere-ƙere, da Sule Musa, wanda ke jagorantar ma’aikatar ciniki da masana’antu.

Wannan mataki ya ɗauki hankalin al’umma, musamman mazauna jihar, inda ake ta hasashe kan yadda sauke kwamishinoni guda biyar zai shafi gudanar da ayyukan gwamnatin jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamna Calen Kwamishinoni

এছাড়াও পড়ুন:

NiMet Ta Yi Hasashen Tsawa Da Ruwan Sama Na Tsawon Kwanaki A Arewa

“A yankin Arewa ta Tsakiya, ana sa ran za a yi tsawa da sanyin safiya a sassan jihohin Benuwe, Filato, Neja, Babban Birnin Tarayya, da Jihar Nasarawa.

 

“A washegari, ana hasashen tsawa da ruwan sama a wasu sassan babban birnin tarayya, Neja, Nasarawa, Benuwe, Kwara, Kogi, da Filato.

 

“A yankin Kudu, ana sa ran samun hadari tare da yiwuwar samun ruwan sama a sassan jihohin Enugu, Ebonyi, Cross River, Legas, Akwa Ibom, Ribas, da Bayelsa,” in ji NiMet.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mataimakin Gwamnan Sakkwato bai karɓi shanun tallafin layya ba — Hukumar Zakka
  • Kakakin Gwamnatin Iran Ta Ce daga Yau Lahadi Wuraren Fakewa A Bude Suke Sa’o’I 24 A Tehran
  • NiMet Ta Yi Hasashen Tsawa Da Ruwan Sama Na Tsawon Kwanaki A Arewa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
  • Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai
  • DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
  • Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya