Kungiyar Hamas Ta Amince Ta Saki Fursinan Yaki Wanda Yake Da Jinsiyar Amurka Da HKI
Published: 12th, May 2025 GMT
Kungiyar Hamas wacce take iko da yankin Gaza, ta bada sanarwan cewa a shirye take ta saki fursina mai suna Edan Alexander wanda yake da jinsiyar Amurka da HKI don bude kofa ga tattaunawar tsagaaita wuta a gaza da kuma bude kofar rafa don samar da kayakin abicni a gaza.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Jami’an kungiyar tana fadar haka a jiya Lahadi.
Khalil Al-Hayya shugaban kungiyar ya bayyana cewa Hamas ta amince da hakan ne bayan wata tattaunawa da Amurka kan batun. Ya kuma kara da cewa kungiyar tana son a fara tattaunawa da gaske tsakaninta da HKI ta hanyar masu shiga tsakani, don kawo karshen yakin da kuma ficewar sojojin yahudawa gaba daya daga Gaza. Da kuma bude kofar Rafa don shigowar kayakin agaji da abinci cikin yankin.
Khalil Al-Hayya ya kara da cewa hamas ta yadda a hada wata tawaga wacce zata gudanar da harkokin shugabanci a yankin.
A wani labarin kuma an tabbatar da cewa Falasdinawa kimani 109,000 ne suka yi shahada a zirin Gaza, tun ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023.
Binciken da aka guddanar ya nuna cewa sojojin yahudawna sun kashe falasdinawa akalla tsaknain 77,00-109.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Axios: Majalisar ministocin Isra’ila ta amince da sabon shiri na mamaye birnin Gaza
Majalisar ministocin Haramtacciyar Kasar Isra’ila ta amince da kudirin firaminista Benjamin Netanyahu na mamaye birnin Gaza, wanda ke zama matakin farko na wani gagarumin farmakin soji da ka iya kaiwa ga mamaye daukacin zirin Gaza, a cewar wani babban jami’in Isra’ila.
Matakin ya biyo bayan tattaunawa sama da sa’o’i 10 da aka shafe ana yi tare da nuna wani gagarumin shiri na ci gaba da kai hare-haren Isra’ila kan Gaza.
Jami’an Amurka sun ce shugaba Trump ya zabi kada ya shiga cikin lamarin, inda ya zabi barin Isra’ila ta yanke shawarar kanta.
A wani bangare na sabon farmakin da ke tafe, ana sa ran dakarun haramtacciyar kasar Isra’ila (IOF) za su ba da umarnin kwashe Falasdinawa kimanin miliyan 1 da ke zaune a birnin Gaza da yankunan da ke kewaye da su a halin yanzu.
A cikin wata sanarwa, ofishin Netanyahu ya bayyana cewa IOF za ta mallaki birnin Gaza, yayin ake ci gaba da fuskantar matsalar jin kai da Rashin abinci da Ruwan sha gami da maguguna da sauran kayayyakin bukatar rayuwa a dauakcin yankin zirin Gaza.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Kira taron Gaggawa Na Kungiyar Kasashen Musulmi August 8, 2025 Iraniyawa Miliyon 1.2 Ne Suka Shiga Iraki Ta Kofar Shiga Na Mehran August 8, 2025 Ansarullah Ta Yi Gargadi Ga Amurka Da HKI Kan Kara Tada Hankali A Yakin August 8, 2025 Hizbullah Da Amal Sun Yi Tir da Shirin Kwance Damarar Hizbullah August 8, 2025 Jirgin Daukar Marasa Lafiya Ya fadi A kasar kenya Ya Kuma Kashe Akalla mutane 6 August 8, 2025 Araqchi: Hari Kan Cibiyoyin Makamashin Nukiliyar Kasar Iran Ba Zai Taba Canza Matsayinta Ba August 7, 2025 Manjo Janar Mousawi: Martanin Iran Nan Gaba Zai Kasance Mafi Muni Kan Makiya August 7, 2025 Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Jaddada Shirinsu Na Tunkarar Duk Wata Barazana August 7, 2025 Hare-Haren Sojojin Mamayar Isra’ila Kan Gaza Sun Janyo Shahadan Falasdinawa Masu Yawa August 7, 2025 Human Rights Watch Ta Ce: Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Rusa Makarantu Fiye Da 500 A Gaza August 7, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci