Iran Da Japan Sun Kara Zurfafa Dankon Zumunci Da Ke Tsakaninsu
Published: 14th, May 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya tattauna da mataimakin ministan harkokin wajen kasar Japan na farko Hiroyuki Namazu a nan birnin Tehran a jiya Talata inda bangarorin biyu suka tattauna al-amuran da suka shafi kasashen biyu na harkokin kasuwanci da kuma wasu bangarori, sannan tare da tattauna irin sauye-sauyen da ake samu a yankin da kuma abinda ya zama lazimi ga kasashen biyu su yi a wannan halin.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa kasashen biyu sun kara jaddada bukatar kasashen su karfafa dangantaka da ke tsakaninsu.
Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Japan ya fada a taron kwamitin hadin guiwa na kasashen biyu kan cewa kasar Japan ta zabi zurfafa dangantaka da kasar Iran duk tare da matsalin lambar da Washington takeyi na nisansar kasar ta Iran.
Hamazu ya kammala da cewa Japan tana son fadada dangantakar tattalin arziki da JMI wanda suka hada da kasuwancin a bangarori daban-daban. Haka ma a bangaren tsaro da ya shafi yankin Asia gaba daya. Wannan dai yana faruwa ne a dai-dai lokacinda Washington ta kara kababawa kasar Iran sabbin takunkuman tattalin arziki a ranar litinin da ta gabata.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Da Amurka Sun Fahinci Juna Sosai A Zagaye Na 4 A Tattaunawa A Mascat
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa tattaunawa ba kai tsaye ba tsakanin JMI da Amurka zagaye na hudu, yana tafiya kamar yadda ya dace. Kuma kasashen buyu sun kara fahintar ra’yin juna.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran da nakalto Aragchi yana fadar haka a wani hira da da ya gabatar bayan kammala zagaye na 4 na tattaunawar a jiya.
Ministan y ace bangarorin biyu sun tattauna babututuwan da suke da zurfi a cikin matsalolin da kasashen biyu suke son su warware, na farko gamsar da Amurka kan cewa shirin makamashin Nukliya na kasar Iran ban a tsaro bane. Da kuma maganar daukewa Iran takunkuman tattalin arzikin da aka dora mata.
Yace tattaunawar jiya yafi magana a kan bayanai masu zurfi kan wadanan matsaloli biyu da sannan babu batun magana ta sama sama.
Steve Witkoff mai bawa shugaban kasar Amurka shawara a kan al-amuran gabas ta tsakiya ne ya jagoranci tawagar Amurka kuma ministan harkokin wajen Omman ne mai kai kawo tsakanin bangarorin b iyu.
Tun ranar 12 ga watan Afrilu ne aka fara tattaunawa ba kai atsaye ba tsakanin Amurka da iran kan shirinta na makamashin nukliya ba kai tsaye ba. Bayan da Amurka ta rubutawa Iran wasika dangane da hakan.