Iran Da Japan Sun Kara Zurfafa Dankon Zumunci Da Ke Tsakaninsu
Published: 14th, May 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya tattauna da mataimakin ministan harkokin wajen kasar Japan na farko Hiroyuki Namazu a nan birnin Tehran a jiya Talata inda bangarorin biyu suka tattauna al-amuran da suka shafi kasashen biyu na harkokin kasuwanci da kuma wasu bangarori, sannan tare da tattauna irin sauye-sauyen da ake samu a yankin da kuma abinda ya zama lazimi ga kasashen biyu su yi a wannan halin.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa kasashen biyu sun kara jaddada bukatar kasashen su karfafa dangantaka da ke tsakaninsu.
Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Japan ya fada a taron kwamitin hadin guiwa na kasashen biyu kan cewa kasar Japan ta zabi zurfafa dangantaka da kasar Iran duk tare da matsalin lambar da Washington takeyi na nisansar kasar ta Iran.
Hamazu ya kammala da cewa Japan tana son fadada dangantakar tattalin arziki da JMI wanda suka hada da kasuwancin a bangarori daban-daban. Haka ma a bangaren tsaro da ya shafi yankin Asia gaba daya. Wannan dai yana faruwa ne a dai-dai lokacinda Washington ta kara kababawa kasar Iran sabbin takunkuman tattalin arziki a ranar litinin da ta gabata.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025
Kasashen Kenya da Tanzaniya da kuma Uganda sun gabatar da kasafin kudin da ya mayar hankali kan zabuka da tattalin arzikin kasashen.
Galibi kasafin kudin kasahen Afirka kan mayar da hankali wajen cimmma muradunsu na tattalin arziki da ci gaba.
Kasafin kudin kasashen Afirka na 2025 na kunshe da muradun ci gaba da bunkasar abubuwan more rayuwa da kuma ingantuwar al’amuran yau da kullum a kasashen.
Kunshin kasafin kudin kasashen Afirka na 2025 ya ware gagarumin kaso a fannin inganta abubuwan more rayuwa da ayyukan kyautata rayuwar al’umma da kuma bunkasa tattalin arzikin kasashen.
Kowace shekara kasashen Afirka na ware makudan kudade a kasafin kudadensu.
A wannan makala mun zakulo kuku kasashen Afirka 10 da suka fi girman kasafin kudi, kuma mun yi kiyasin da Dala domin samun saukin lissafi.
Afirka ta Kudu – (Dala biliyan 141.4)Kasar Afirka ta Kudu ce kan gaba wajen ware makudan kudade a kasafin kudi a Afirka a 2025.
A wannan shekara kasar ta ware Dala biliyan 141.4 a matsayin kasafin kudiinta.
Kasafin kudin ya fifita fannin abubuwan more rayuwa da ayyukan bunkasa rauyuwar jama’a da ci gaban tattalin arziki.
Algeria – (Dala biliyan 126)Kasar Algeria ce ke matsayi na biyu a yawan kasafin kudi a nahiyar Afirka a 2025. Kasar – wadda ke arewacin Afirka – ta ware Dala biliyan 126 a kasafin kudinta, inda tafifita fannnonin makamashi da tsaro.
Masar – (Dala biliyan 91)Masar ce ta uku cikin jerin, mai adadin kudi har Dala biliyan 91, inda ta ware kaso mai yawa zuwa fannonin ilimi da lafiya da ayyukan da za su amfani jama’a.
Morocco – (Dala biliyan 73)Kasar Morocco – da ita ma ke yankin arewacin Afirka ta kasance a mataki na hudu.
Morocco ta ware Dala biliyan 73 a kasafin kudinta na shekarar 2025.
Angola – (Dala biliyan 37.847)Angola – arzikin man fetur – ce a matsayi na biyar cikin jerin kasashen Afirka da suka fi karfin kasafin kudi.
Kasar – wadda ke yankin kudancin Afirka – ware Dala biliyan 37.847 domin kasafin kudinta na shekarar da muke ciki.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp