Wasu ma’aikatan lafiya biyu sun rasu, wasu da dama sun jikkata bayan motarsu ta taka bom a kan hanyar Damboa zuwa Maiduguri a Jihar Borno.
Ana zargin mayakan Boko Haram ne suka dasa bom din a wani hari da kungiyar ta kai a kan babbar hanyar a ranar Litinin.
Shaidu sun bayyana cewa, wadanda suka mutun suna zaune ne a gaban motar jigilar mangoro, kirar Toyota Hiace da ta dauko su daga Damboa zuwa Maiduguri.
Sun kara da cewa tashin bom din ya haifar da sabuwar damuwa game da lafiyar matafiya a kan hanyar.
Yadda ISWAP ta kashe sojoji ta kwashe makamai a sansanin soji a Borno ’Yan bindiga sun yi awon gaba da mutum 5 a Filato Ya kashe abokinsa saboda hula a KanoWata majiya a karamar hukumar Damboa ta tabbatar da cewa mamatan jami’an Hukumar Ilimi na Karamar Hukumar Damboa ne.
Tuni jami’an tsaro suka killace yankin, yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike domin gano ainihin yadda lamarin ya kasance.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram Damboa zuwa Maiduguri Ma aikatan Lafiya
এছাড়াও পড়ুন:
An gano wasu bama-bamai 56 da ISWAP suka binne a Borno
Dakarun rundunar sojin ‘Operation Haɗin Kai’ sun ce dakarunsu sun kai ga nasarar gano wasu bama-bamai guda 56 da ake zargin mayaƙan ISWAP ne suka binne a kan gadar Marte zuwa Dikwa da ke Jihar Borno.
Sojojin sun kuma daƙile wani harin da ka iya zama wani babban harin da zai haifar da mummunan ɓarnar rayuka da dukiyoyi.
Sojoji sun kashe ’yan ta’adda da ƙwato makamai a Borno Kotu ta umarci a mayar da Sanata Natasha majalisaMajiyoyin da ke da alaƙa da rundunar ta OPHK ta tabbatar da a ranar Juma’a cewa, aka gano bama-baman a wani samame da sojojin na runduna ta 24 da ke Dikwa, Jihar Borno suka yi.
A cewar majiyar, ’yan tada ƙayar bayan sun sanya bama-baman ne a kan gadar da dabarar da nufin yin ɓarna mai yawa tare da daƙile zirga-zirgar sojoji da fararen hula a kan hanyar.
Majiyar ta ce, “Sojojin da ke aiki da sahihan bayanan sirri, sun gano na’urorin kafin su tarwatse.
Ya ƙara da cewa, nan take aka tura tawagar da ke kawar da bama-bamai (EOD) zuwa wurin domin taimakawa wajen tabbatar da tsaron na’urorin don kwance su kafin su kaiga tashi.
Hotunan farmakin sun nuna wasu bama-bamai da aka gano a jikin wasu muhimman sassan gadar da ta haɗa manyan garuruwa biyu a Arewacin Borno.
Majiyoyin sun ce saurin shiga tsakani da sojojin suka yi ne ya daƙile wani mummunan harin ta’addanci, wanda ake iya kaiwa jami’an tsaro, al’ummomin farar hula da masu ayyukan jin ƙai a yankin.
Ana ci gaba da sa ido a yankin, yayin da ake ci gaba da aikin share sauran abubuwan fashewa a yankin da zarar an gano su.
Don haka rundunar ta OPHK ke kira ga jama’a musamman masu abubuwan hawa da su riƙa yin taka tsantsan gami da lura akan waɗannan hanyoyin tare da kai rahoton duk wani abu da suke zargi ga jami’an rundunar don magance shi akan lokaci kafin ya kai ga haddasa mummunan lamari.