Wasu ma’aikatan lafiya biyu sun rasu, wasu da dama sun jikkata bayan motarsu ta taka bom a kan hanyar Damboa zuwa Maiduguri a Jihar Borno.
Ana zargin mayakan Boko Haram ne suka dasa bom din a wani hari da kungiyar ta kai a kan babbar hanyar a ranar Litinin.
Shaidu sun bayyana cewa, wadanda suka mutun suna zaune ne a gaban motar jigilar mangoro, kirar Toyota Hiace da ta dauko su daga Damboa zuwa Maiduguri.
Sun kara da cewa tashin bom din ya haifar da sabuwar damuwa game da lafiyar matafiya a kan hanyar.
Yadda ISWAP ta kashe sojoji ta kwashe makamai a sansanin soji a Borno ’Yan bindiga sun yi awon gaba da mutum 5 a Filato Ya kashe abokinsa saboda hula a KanoWata majiya a karamar hukumar Damboa ta tabbatar da cewa mamatan jami’an Hukumar Ilimi na Karamar Hukumar Damboa ne.
Tuni jami’an tsaro suka killace yankin, yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike domin gano ainihin yadda lamarin ya kasance.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram Damboa zuwa Maiduguri Ma aikatan Lafiya
এছাড়াও পড়ুন:
‘An Kashe Masu Zanga-zanga Akalla 500 a Tanzania’
Jami’an diflomasiyya a Tanzania sun ce akwai kwararan hujjoji da ke tabbatar da an kashe akalla mutum 500 a cikin kwana biyu da barkewar zanga-zangar kin amincewa da sakamakon zaben da aka gudanar a ranar Laraba.
Sai dai a wani bangaren kuma, alkalumman Yan’adawa sun zarta haka.
Wakiliyar BBC ta ce ministan harakokin wajen Tanzania Mahmoud Kombo Thabit ya musanta rahotannin, amma wani jagoran adawa John Kitoka ya ce ‘yansanda da wasu sojojin haya na kasashen waje ne suka aiwatar da kisan mutane cikin dare.
Majalisar Dinkin Dauniya ta yi kiran gudanar da bincike kan zargin amfani da karfin da ya wuce kima a kan masu zanga-zangar.
BBC