Aminiya:
2025-08-08@16:43:03 GMT

Masana sun ƙalubalanci sojoji kan maharan ƙasashen waje

Published: 9th, May 2025 GMT

Masana harkokin masana tsaro sun nuna rashin amincewarsu da iƙirarin sojojin Najeriya cewa baƙi daga ƙasashen waje ne ke kai yawancin hare-haren da ake kaiwa al’ummomin ƙasar, musamman a jihohin Filato da Benue.

Wannan ƙalubalen ya fito ne bayan wata sanarwa da Hedikwatar Tsaro ta yi a ranar Alhamis, cewa yawancin hare-haren da ake kai wa manoma da kashe-kashe a sassan kasar, makiyaya ne ’yan kasashen waje suka fi aikatawa.

Daraktan Ayyukan Yada Labarai na Tsaro, Manjo-Janar Markus Kangye, ya bayyana haka ne lokacin da yake amsa tambayoyin manema labarai game da hare-haren a kan manoman.

Wani kwararre a kan sha’anin tsaro, Jackson Lekan, ya ce  bayanan Manjo-Janar Kanye ya nuna laifi da kuma gazawar hukumomin da ke da alhakin tsaron iyakokin Najeriya da masu tara bayanan sirri.

Yadda matsalar wutar lantarki ke ajalin rayuka a manyan asibitoci NAJERIYA A YAU: Abin ya sa aka kasa kawo ƙarshen Tamowa a Arewa Maso Gabas An gurfanar da mutum 10 kan yi wa nakasasshiya fyaɗe a Kaduna

n kashe mutane da yawa tare da raba wasu dubbai da gidajensu a jihohin Filato da Benue a sakamakon hare-hare da makiyaya ɗauke da makamai suka kai a kwanakin baya.

Manjo-Janar Kangye ya ce duk da cewa ana magana da Hausa a sassa daban-daban na Afirka, amma abu mai sauƙi ne a gane waɗanda ba ’yan Najeriya ba ne. Ya ce, “idan aka ji su suna magana, za a iya gane ’yan ƙasa ne ko baƙi.”

Ya bayyana cewa sun kama wasu daga cikin ’yan ta’addan, kuma yadda suke magana da kamanninsu da ma gashin kansu, yana nuna cewa ba ’yan Najeriya ba ne.

Y amince cewa yawancin masu aikata ta’addanci a Najeriya baƙi ne, duk da cewa akwai ’yan ƙasar a cikinsu. Ya ƙara da cewa yawancin tashin hankalin da ake ji a wasu sassan ƙasar nan, galibi waɗanda suka shigo ƙasar ta bayan fage ne ke aikata su.

Ya yi kira ga hadin gwiwa tsakanin hukumomin tsaro don tabbatar da an yi ɗauki bayanan duk wanda ya shigo Najeriya.

Masana sun ɗiga ayar tambaya

Sai dai, wasu masana tsaro sun nuna shakku game da wannan iƙirarin.

Dakta Kabiru Adamu, Shugaban Kamfanin Beacon Consult, ya amince cewa sojojin Najeriya suna fuskantar matsin lamba sosai saboda ƙaruwar hare-hare da kuma yadda ake bibiyar su daga kafafen yada labarai da manyan jami’an gwamnati.

Ya ce wannan matsin lamba zai iya shafar ƙarfin guiwar sojoji da kuma yadda suke gudanar da ayyukansu, wanda zai iya kai su ga bayar da irin wannan sanarwa don nuna cewa suna samun ci gaba tare da ɗora alhakin ga wasu.

Ya yi nuni da yarjejeniyar ECOWAS kan zirga-zirgar dabbobi da makiyaya, yana mai cewa duk da manufarta ta sauƙaƙa zirga-zirga, ana ganin ta a matsayin hanyar da ’yan bindiga za su iya shigowa kasar ba tare da an san su ba.

Kabiru Adamu ya yi kira da a sake duba yadda ake aiwatar da wannan yarjejeniya tare da samar da hanyoyin da za a iya bibiyar masu shigowa ƙasar.

Ya kuma jaddada matsalar iyakar Najeriya da ba ta da tsaro, yana mai kira da a inganta haɗin gwiwa da ƙasashe makwabta tare da saka hannun jari a yankunan kan iyaka.

Wani tsohon kwamandan sojin sama, Dakta Musa Salmanu, ya ce zai ɗauki maganar kakakin hedikwatar tsaro da muhimmanci, amma ya nuna damuwa cewa idan ’yan kasashen waje ne ke kai hare-haren, hakan na nufin Najeriya na fuskantar wani nau’i na mamayewa.

Ya yi tambayoyi game da ko waɗannan mutane ne suka zo da kansu ko kuma wasu ƙasashe ne ke ɗaukar nauyinsu.

Ya jaddada cewa ko ’yan Najeriya ne ko baƙi, babban abin da ya kamata a fi mayar da hankali a kai shi ne yadda za a dakatar da barnar da suke yi.

Ya kuma yi kira da a magance tushen matsalar rikicin makiyaya da manoma da sauran matsalolin tsaro a sassan Najeriya.

Wani tsohon ɗan majalisa, Destiny Enabulele, ya zargi shugabannin Najeriya da rashin jajircewar magance matsalar rashin tsaro.

Ya yi tambaya game da yadda ake kashe kuɗaɗen da aka ware don tsaro, yana mai cewa har sai an samu jajircewar yaƙar rashin tsaro, ba za a samu mafita ba.

Ya kuma yi kira ga jami’an shige da fice da na kwastam da su koma kan iyakokin kasar don gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.

Wani masanin tsaro, Jackson Lekan Ojo, ya musanta iƙirarin sojojin, yana mai cewa hakan ya nuna gazawar hukumomin iyaka da na leƙen asiri na ƙasar.

Ya ce ya kamata a hukunta waɗanda ke da alhakin tsaron iyakokin Najeriya, yana mai bayyana ikirarin a matsayin “uzuri maras tushe,” da ke nuna halin ko-in-kula na sojoji da sauran jami’an tsaro.

Ya yi kira da a fatattaki waɗannan mutane, a kama su ko kuma a mayar da su kasashensu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan ta adda hare hare Makiyaya Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana

Waɗannan bayanai duk suna ƙunshe ne a cikin jawaban da aka gudanar a gangamin wayar da kai game da wannan cuta, wanda ya gudana a Kaduna.

 

Lokacin da ta ke zantawa da manema labarai jim kaɗan bayan wannan gangami, Dr. Maimuna Lawal Garba, ƙwararriyar Likita a fannin hanci, kunni da maƙogwaro, ta fara bayanin ta ne da bayyana abubuwan da suke haddasa wannan cuta ta Kansar Maƙogwaro.

 

Ta ce, “Muna bai wa mutane shawara su kiyayi shan tabar sigari, barasa (giya). Haka kuma akwai yanayin aikin mutane, misali, masu aiki a wurin yankan katako, wannan ƙurar ta katako tana daga cikin abubuwan da za su iya sabbaba ma mutum kamuwa da wannan cuta.

 

“Haka kuma akwai (radiation), na’urar haske, idan ya shiga ƙwaƙwalwa zai iya haifar da wannan cuta. Haka kuma akwai yawan shekaru na tsufa, akwai kuma ƙwayar cutar HPF, ita ma tana sabbaba kamuwa da wannan cuta. Haka kuma idan mutum yana da gadon wannan cuta, shi ma zai iya zama musabbabin kamuwa.”

 

Shi kuwa Dr. Muhammad Sani, wanda ya ke shi ma Likita ne a wannan fanni na Hanci, Kunni da Maƙogwaro, cikin jawabin sa, ya ce, abin takaici ne ganin cewa wannan cuta ta Kansar Hanci, Kunne da Maƙogwaro tana ƙara yaɗuwa a duniya, musamman yankin Afrika, wanda kuma Nijeriya na ciki.

 

Da ya ke ƙarin haske, Dr. Usman Ibrahim Sani, wanda shi ma ƙwararren Likita ne a wannan fanni, ya bayyana cewa ba wai masu shan sigari da giya ne kawai suke kamuwa da wannan cuta ba, “zai iya faruwa da waɗanda ba sa mu’amala da waɗannan abubuawa, amma yana da kyau mutum ya garzaya asibiti tun abin na ɗan ƙarami, ta yadda zai fi sauƙin magancewa,”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro 
  • NAJERIYA A YAU: Shekara nawa shugabanni ke bukata don cika alkawuran zabe?
  • Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana
  • Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi
  • Yadda sabbin takunkuman Trump za su shafi tattalin arziƙin duniya
  • NAJERIYA A YAU: Mummunan Tasirin Rashin Bambance Zazzabin Lassa Kan Lafiyar Al’umma
  • Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi
  • Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa
  • Yadda ’yan bindiga suka sace Zamfarawa 150 a cikin kwana 4
  • Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu