Masana sun ƙalubalanci sojoji kan maharan ƙasashen waje
Published: 9th, May 2025 GMT
Masana harkokin masana tsaro sun nuna rashin amincewarsu da iƙirarin sojojin Najeriya cewa baƙi daga ƙasashen waje ne ke kai yawancin hare-haren da ake kaiwa al’ummomin ƙasar, musamman a jihohin Filato da Benue.
Wannan ƙalubalen ya fito ne bayan wata sanarwa da Hedikwatar Tsaro ta yi a ranar Alhamis, cewa yawancin hare-haren da ake kai wa manoma da kashe-kashe a sassan kasar, makiyaya ne ’yan kasashen waje suka fi aikatawa.
Daraktan Ayyukan Yada Labarai na Tsaro, Manjo-Janar Markus Kangye, ya bayyana haka ne lokacin da yake amsa tambayoyin manema labarai game da hare-haren a kan manoman.
Wani kwararre a kan sha’anin tsaro, Jackson Lekan, ya ce bayanan Manjo-Janar Kanye ya nuna laifi da kuma gazawar hukumomin da ke da alhakin tsaron iyakokin Najeriya da masu tara bayanan sirri.
Yadda matsalar wutar lantarki ke ajalin rayuka a manyan asibitoci NAJERIYA A YAU: Abin ya sa aka kasa kawo ƙarshen Tamowa a Arewa Maso Gabas An gurfanar da mutum 10 kan yi wa nakasasshiya fyaɗe a Kadunan kashe mutane da yawa tare da raba wasu dubbai da gidajensu a jihohin Filato da Benue a sakamakon hare-hare da makiyaya ɗauke da makamai suka kai a kwanakin baya.
Manjo-Janar Kangye ya ce duk da cewa ana magana da Hausa a sassa daban-daban na Afirka, amma abu mai sauƙi ne a gane waɗanda ba ’yan Najeriya ba ne. Ya ce, “idan aka ji su suna magana, za a iya gane ’yan ƙasa ne ko baƙi.”
Ya bayyana cewa sun kama wasu daga cikin ’yan ta’addan, kuma yadda suke magana da kamanninsu da ma gashin kansu, yana nuna cewa ba ’yan Najeriya ba ne.
Y amince cewa yawancin masu aikata ta’addanci a Najeriya baƙi ne, duk da cewa akwai ’yan ƙasar a cikinsu. Ya ƙara da cewa yawancin tashin hankalin da ake ji a wasu sassan ƙasar nan, galibi waɗanda suka shigo ƙasar ta bayan fage ne ke aikata su.
Ya yi kira ga hadin gwiwa tsakanin hukumomin tsaro don tabbatar da an yi ɗauki bayanan duk wanda ya shigo Najeriya.
Masana sun ɗiga ayar tambayaSai dai, wasu masana tsaro sun nuna shakku game da wannan iƙirarin.
Dakta Kabiru Adamu, Shugaban Kamfanin Beacon Consult, ya amince cewa sojojin Najeriya suna fuskantar matsin lamba sosai saboda ƙaruwar hare-hare da kuma yadda ake bibiyar su daga kafafen yada labarai da manyan jami’an gwamnati.
Ya ce wannan matsin lamba zai iya shafar ƙarfin guiwar sojoji da kuma yadda suke gudanar da ayyukansu, wanda zai iya kai su ga bayar da irin wannan sanarwa don nuna cewa suna samun ci gaba tare da ɗora alhakin ga wasu.
Ya yi nuni da yarjejeniyar ECOWAS kan zirga-zirgar dabbobi da makiyaya, yana mai cewa duk da manufarta ta sauƙaƙa zirga-zirga, ana ganin ta a matsayin hanyar da ’yan bindiga za su iya shigowa kasar ba tare da an san su ba.
Kabiru Adamu ya yi kira da a sake duba yadda ake aiwatar da wannan yarjejeniya tare da samar da hanyoyin da za a iya bibiyar masu shigowa ƙasar.
Ya kuma jaddada matsalar iyakar Najeriya da ba ta da tsaro, yana mai kira da a inganta haɗin gwiwa da ƙasashe makwabta tare da saka hannun jari a yankunan kan iyaka.
Wani tsohon kwamandan sojin sama, Dakta Musa Salmanu, ya ce zai ɗauki maganar kakakin hedikwatar tsaro da muhimmanci, amma ya nuna damuwa cewa idan ’yan kasashen waje ne ke kai hare-haren, hakan na nufin Najeriya na fuskantar wani nau’i na mamayewa.
Ya yi tambayoyi game da ko waɗannan mutane ne suka zo da kansu ko kuma wasu ƙasashe ne ke ɗaukar nauyinsu.
Ya jaddada cewa ko ’yan Najeriya ne ko baƙi, babban abin da ya kamata a fi mayar da hankali a kai shi ne yadda za a dakatar da barnar da suke yi.
Ya kuma yi kira da a magance tushen matsalar rikicin makiyaya da manoma da sauran matsalolin tsaro a sassan Najeriya.
Wani tsohon ɗan majalisa, Destiny Enabulele, ya zargi shugabannin Najeriya da rashin jajircewar magance matsalar rashin tsaro.
Ya yi tambaya game da yadda ake kashe kuɗaɗen da aka ware don tsaro, yana mai cewa har sai an samu jajircewar yaƙar rashin tsaro, ba za a samu mafita ba.
Ya kuma yi kira ga jami’an shige da fice da na kwastam da su koma kan iyakokin kasar don gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.
Wani masanin tsaro, Jackson Lekan Ojo, ya musanta iƙirarin sojojin, yana mai cewa hakan ya nuna gazawar hukumomin iyaka da na leƙen asiri na ƙasar.
Ya ce ya kamata a hukunta waɗanda ke da alhakin tsaron iyakokin Najeriya, yana mai bayyana ikirarin a matsayin “uzuri maras tushe,” da ke nuna halin ko-in-kula na sojoji da sauran jami’an tsaro.
Ya yi kira da a fatattaki waɗannan mutane, a kama su ko kuma a mayar da su kasashensu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan ta adda hare hare Makiyaya Tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Farfesa Bamaiyi ya bayyana ainihin aikin IAR a matsayin habaka nau’ikan dimbin amfanin gona da kuma jure fari wadanda suka dace da bukatun noma a Nijeriya.
Ya bayyana masarar TELA a matsayin wata sabon salo da kirkira ta zamani a kimiyyance domin magance matsalolin da ake ci gaba da addabar amfanin gona, kamar kwari da canjin yanayi.
Aikin “Masarar TELA bai takaita kan inganci da wadatar abinci ba, har ma tana ba da kariya ga rayuwar manoma, da inganta noman da kuma magance ainihin illar da tsutsotsi ke haifarwa, gami da juriya a yayin fari,” in ji shi.
Shi ma da yake jawabi a yayin ziyarar, Farfesa Muyideen Oyekunle, wani masani a fannin tsirrai kuma daya daga cikin jagorori masu bincike kan aikin masarar Tela, ya gano yadda akre bunkasa wannan noma tun a farkon shekarar 2019.
Ya jaddada cewa bayan shekaru masana kimiyya, tantance hadarin, da kuma bin ka’ida, sun tabbatar da cewa masara ba ta da wata illa ga dan’Adam da muhalli.
“Bincikenmu ya tabbatar da cikakkiyar hujja akan haka, kuma ya yi daidai da ka’idojin aminci na duniya. Abubuwan da ke tattare da GMOs ba a ma fara bayyana shi ba.
TELA maize ta samu duk wani bincike da ya dace a ce an yi domin kare lafiyar halittu, kuma muna da yakinin cewa ba ta da wata illa ga lafiyar dan’Adam,” in ji Farfesa Oyekunle.
Wata kwararriya daga Cibiyar, Farfesa Memuma Abdulmalik, wadda ta tabbatar da hakan, ta bayyana cewa an samar da TELA maide ne domin noman masara mai inganci tare da kawar da duk wani nau’i na kwari da kuma fari.
A cewarta, wadannan gyare-gyaren ba sa canza tsarin abinci mai gina jiki ko amincin amfanin gona.
“Manufar inganta kwayoyin halittar TELA maize ita ce kare amfanin gona daga kamuwa da tsutsotsi dake addabai tsirrai da kuma sanya jurewar fari. Bayan wannan babu abu abu mai cutarwa ga masarar ko kuma haifar da wani hadari ga muhalli,” in ji ta.
A nasa bangaren, Farfesa Shehu Ado ya bayyana cewa daga cikin amfanin masarar TELA maize, yana matukar rage bukatar magungunan kashe kwari, wadanda galibi ke haifar da illa ga lafiya da muhalli fiye da amfanin gona.
Ya kara da cewa, “Ta hanyar rage dogaro ga magungunan noma masu cutarwa, masara ta TELA maize na ba da gudummawa ga tsarin noma mai dorewa kuma wanda ya dace da muhalli,” in ji shi.
Masanan sun kuma yi nuni da cewa, bayanai marasa tushe da ake yadawa game da GMOs ya haifar da koma-baya ga sabbin ayyukan noma da za su ceto rayuka a Nijeriya. Sun bukaci kafafen yada labarai da su rika gaggauta yada sahihan bayanai masu alaka da kimiyya.
Masarar TELA maize, wadda aka samar a karkashin gidauniyar TELA ta fasahar noma ta Afrika wato (AATF) tare da hadin gwiwar IAR da sauran masu ruwa da tsaki, na ci gaba da gudanar da gwaje-gwajen gonaki da yawa, kuma a halin yanzu an amince da noman a yankuna da dama a Nijeriya.
Yayin da ake ci gaba da muhawarar jama’a game da kayan amfanin gonar, kungiyar IAR ta sake jaddada aniyarta ta tabbatar da gaskiya, aminci, da samar da mafita wadanda ke karfafa wa manoma domin tabbatar da an samar da isasshen abinci a kasa.
Nijeriya na iya tanadin Naira Biliyan 900 duk shekara ta hanyar TELA Maize – IAR
Cibiyar Binciken Aikin Noma ta Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya ta bayyana cewa Nijeriya za ta iya yin tanadin sama da Naira biliyan 900 a duk shekara ta hanyar amfani da irin masarar TELA da aka samar ta hanyar kwayoyin halitta.
A cewar cibiyar, daga cikin irin gudunmawar da masarar TELA za ta bayar, akwai rage dogaro da magungunan kashe kwari da ake shigowa da su daga waje da ake amfani da su don yakar kwari masu lalata amfani kamar farin Dan go.
Babban daraktan hukumar ta IAR, Farfesa Ado Adamu Yusuf, ya bayyana irin gagarumar fa’idar da masara ta TELA ke samarwa a fannin tattalin arziki da noma, sannan ya jaddada bukatar a gaggauta gyara kura-kuran da jama’a ke yi game da amfanin gonakin fasahar kere-kere.
A cewarsa, Nijeriya na kashe sama da Naira biliyan 900 (kimanin Dalar Amurka miliyan 600) a duk shekara wajen shigo da magungunan kashe kwari don magance kwarin masara kamar farin Dan go, ban da kudin aikace-aikace.
Ya lura cewa bullo da masarar TELA mai jure kwari da jure fari (SAMMAZ 72T zuwa 75T) zai rage kashe kudaden da ake yi sosai, tare da habaka amfanin gona, da kuma adana ajiyar waje.
Muhimman fa’idodin masarar TELA da aka bayyana a yayin ziyarar sun haɗa da: jurewar kwari, jure fari, ƙara yawan amfanin gona da kuma samar da abinci.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp