Tsohon shugaban kasar Sin marigayi Mao Zedong ya taba bayyana cewa, ” Idan an dauki mataki mai karfi wajen neman zaman lafiya, to, za a samu. Amma idan an nuna sassauci a kokarin neman tabbatar da zaman lafiya, to, ba za a samu biyan bukata ba. ” Wannan tunani ya sa kasar Sin nuna ra’ayin kin amincewa da matakin kasar Amurka na karbar karin harajin fito ba tare da wasiwasi ba.

Musamman ma ta la’akari da yadda kasar ba ta rasa “kati” a hannunta ba, inda karfin tattalin arzikinta, da manufar bude kofa da ta dauka, dukkansu suka kasance karfinta na tinkarar kalubale.

Sai dai, idan babu “kati” a hannu, yaya za a yi? Ga shi, abu na biyu da ya kamata mu lura da shi, shi ne, yayin da muke fuskantar matsin lamba daga kasar Amurka, kar mu yi kasa a gwiwa, maimakon haka ya kamata mu yi kokarin hadin gwiwa da abokan hulda.

Bayan da kasar Amurka ta kaddamar da yakin haraji, kasar Japan ita ce kasa ta farko da ta tura wakili zuwa kasar Amurka, don rokon a yafe mata harajin da aka kara. Amma ba ta samu komai ba, ta tashi a fankan-fayau balle ma a batun harajin kwastam mai matukar tsanani. Ganin haka ya sa kasar Japan ita ma ta dauki “kati”, ta fara wasa da shi, inda kasar ta sanar da cewa ba za ta taba hakuri da manufar haraji ta kasar Amurka ba. Kana jaridar Labarun Tattalin Arziki Na Kasar Japan ta wallafa wani bayani mai taken “Matakan Kasar Amurka Za Su Haifar Da Tsarin Cinikin Duniya Da Bai Kunshi Kasar Amurka Ba”.

A hakika, ana kan hanyar samun wani tsarin cinikin duniya, da bai shafi kasar Amurka ba, ko kuma ba zai tasirantu da Amurka ba. Idan mun lura da ayyukan da dimbin kasashen nahiyoyin Asiya, da Afirka, da Latin Amurka suke yi, da sanarwoyin kasashen BRICS, da na kungiyar kasashen Afirka ta AU, to, za mu san cewa, kasashe masu tasowa suna kokarin karfafa hadin kansu a fannin tattalin arziki da cinikayya, da daidaita tsare-tsaren samar da kayayyaki, ta yadda za su samu sabbin damammakin raya kansu, yayin da ake fuskantar daidaituwar yanayin tattalin arzikin duniya.

Haka zalika, wata shawara mafi muhimmanci ita ce, a yi watsi da burin zama abokiyar kasar Amurka.

Saboda Amurka na kallon moriyar kanta a gaba da komai. Don haka, idan wata kasa tana son zama abokiyar huldar kasar Amurka, to, wata rana za ta ga yadda kasar Amurka ta mai da ita tamkar abokiyar gaba. Wannan dabarar kasar Amurka ta sa Ukraine rasa albarkatun kasarta, kana kasar Canada ta zama “jiha ta 51 ta kasar Amurka” a idon Amurka din. Yayin da kasashen Turai, ko da yake suke son taimakon kasar Amurka wajen dakile tattalin arzikin Sin, sai dai duk da haka, kasar Amurka na son ganin yadda kasashen Turai su nuna sassauci, da zama wani bangaren da kasar Amurka za ta iya kwatar dukiyoyinsa yadda ta ga dama. (Bello Wang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: da kasar Amurka Da Kasar Amurka

এছাড়াও পড়ুন:

Batun Zuba Hannun Jari A Amurka Ne Babbar Ajandar Ziyarar Shugaba Donald Trump Zuwa Kasashen Larabawan Yankin Tekun Pasha

A yau Talata ne shugaban kasar Amurka Donald Trump ya isa kasar Saudiyya domin fara ziyarar aiki a karon farko tun da ya zama shugaban kasa.

Baya ga kasar Saudiyya shugaban kasar ta Amurka zai kuma kai Ziyara zuwa kasashen Qatar da Hadaddiyar Daular Larabawa da zummar bunkasa alaka  da larabawan yankin tekun Pasha kamar yadda majiyar bangarorin biyu take ambatawa.

Bugu da kari, kafafen watsa labarun Amurka sun ce, a yayin wannan ziyarar tashi, shugaban kasar Amurkan, zai yi kokarin samarwa kasarsa hannun jari da kasashen larabawa masu arziki za su zuba. Tun a baya dai Donald Trump ya bukacin ganin Saudiyya kadai ta kara yawan hannun jarinta a cikin Amurka da zai kai dala tiriliyan 1.

Kafar watsa labaru ta Axios ta ce; Babu wata ajanda a ziyarar ta Donald Trump zuwa kasashen larabawan da ta wuce ta kudi.”

Bugu da kari wani jami’in a yankin kasashen larabawan tekun pasha ya fada wa wannan kafar watsa labarun cewa; Kasuwanci shi ne babbar ajandar ziyarar Donald Trump.”

Yarima mai jiran gado na Saudiyya Muhammad Bin Salman ya yi alkawalin zuba hannun jari na dalar Amruka biliyan 600 a cikin shekaru 4 masu zuwa. Haka nan kuma Saudiyyar za ta sayi makamai na dala biliyan 100 daga Amurkan.

Ita ma kasar Qatar za ta zuba jarin dala biliyan 200 zuwa 300 a Amurka, kamar kuma yadda za ta sayi jiragen saman a kasuwanci da kudinsu zai kai dalar Amurka biliyan 2.

Ita kuwa Hadaddiyar Daular Larabawa ta yi alkawalin zuba hannun jari na dala tirliyan 1.4 a Amurka a cikin shekaru 10 masu zuwa.

A halin yanzu shugaban kasar ta Amurka ya cire batun kulla alaka a tsakanin Saudiyya da HKI daga cikin manufofin ziyarar tashi saboda yakin da ake ci gaba da yi a Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ta Iran Ya Isa Birnin Jakarta Na Kasar Indonesiya
  • Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci
  • ‘Duk da hauhawar farashi tattalin arzikin Nijeriya ya haɓaka’
  • Batun Zuba Hannun Jari A Amurka Ne Babbar Ajandar Ziyarar Shugaba Donald Trump Zuwa Kasashen Larabawan Yankin Tekun Pasha
  • Shugaban Amurka Na Kan Hanyarsa Ta Zuwa Kasar Saudiya
  • Burtaniya Ta Gabatar Da Sabbin Tsare-Tsare Na Shige Da Fice Da Kuma Bisar Shiga Kasar
  • Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu
  • Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a