Gidauniya ta yi wa masu cutar gwaiwa dubu 12 tiyata kyauta a Katsina
Published: 10th, May 2025 GMT
Gidauniyar attajirin ɗan kasuwar nan na Jihar Katsina, Alhaji Dahiru Mangal, ta yi wa masu fama da cutar gwaiwa da taruwar ruwa a wasu sassan jiki fiye da 12,300 tiyata kyauta.
Da yake yi wa wakilin bayani, Malam Husaaini Kabir, mamba a kwamitin amintattu na gidauniyar ne ya tabbatar da hakan a Katsina, a lokacin ƙaddamar da aikin kashi na biyu.
Kabir ya bayyana cewa gidauniyar tana gudanar da aikin tiyatar da bayar da magani kyauta a duk bayan watanni uku tun lokacin da aka kafa ta a shekarar 2013.
Ya ƙara da cewa, “majinyata masu rauni tsakanin 500 zuwa 600 ne ke cin gajiyar aikin tiyatar gwaiwar da na rage ruwan kyauta a jihar.
“Wannan shiri ba wai yana taimaka wa mutanen garin Katsina ne kawai ba, yana kuma tallafa wa mazauna ƙauyukan jihar da kuma yankunan da ke makwabtaka da su.
“Manufarmu ita ce rage nauyin biyan kuɗin kiwon lafiya ga mutane masu ƙaramin ƙarfi waɗanda ke gwagwarmaya don biyan buƙatun yau da kullun,” in ji shi.
Kabir ya buƙaci sauran ƙungiyoyi da masu hannu da shuni da su tallafawa irin wannan shiri, musamman don taimaka wa ƙoƙarin gwamnati a fannin kiwon lafiya.
Ya jaddada mahimmancin aikin tare don tunkarar ƙalubalen kiwon lafiya a cikin al’ummomin da ba a yi musu hidima ba.
Wasu da suka ci gajiyar shirin sun yaba da shirin tare da ƙarfafa gwiwar gwamnati, ƙungiyoyi masu zaman kansu, da masu hannu da shuni da su yi koyi da hakan.
Sun bayyana cewa sun jure yanayin da suke ciki na tsawon shekaru amma ba za su iya yin tiyatar ba saboda matsalar tattalin arziki.
Aminiya ta ruwaito cewa gidauniyar ta kuma bayar da maganin ido da tiyata kyauta ga marasa lafiyar idon a jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gidauniyar Mangal Gwaiwa Jihar Katsina Tiyata
এছাড়াও পড়ুন:
Trump ta ce Iran da Isra’ila sun amince da tsagaita wuta bayan harin Iran kan sansanonin Amurka
Shugaban Ƙasar Amurka Donald Trump ya ce an ƙulla yarjejeniyar tsagaita wuta gaba daya a yaƙin da ya ɓarke tsakanin Iran da Isra’ila.
Kafar yaɗa labarai ta the Guardian ta ƙasar Birtaniya ta ruwaito cewa Trump ya sanar da haka ne a shafinsa na sadar da zamunta, ’yan sa’o’i bayan hare-haren ramuwar gayya da Iran ta kai a sansanin sojin Amurka da ke ƙasar Qatar da Iran bayan hare-haren da Amirkan ta kai wa Iran.
Ya sanar cewa cikin awa shida na farko Iran za ta fara dakatar da kai hare-hare, daga bisani Isra’ila ta dakatar, wanda hakan zai kawo ƙarshen yaƙin ɗungurungum.
Sanarwar tasa na zuwa ne bayan tsohon Fira Ministan Rasha, babbar ƙawar Iran, Dimitry Medvedev na cewa ƙasashe masu ƙarfin makaman nukiliya na yi wa Iran tayin makaman nasu a yayin da yaƙin ke ƙara ƙamari.
Babu dalilin kai wa Iran farmaki — Putin Akwai ƙasashen da ke shirin bai wa Iran makaman nukiliya — RashaKazalika akwai yiwuwar babbar abokiyar gaban Amurka, wato Koriya ta Kudu na shirin taimaka wa Iran gyara tashoshin nukiliyan da hare-haren Amurka da Isra’ila suka shafa, da kuma gina sababbin masana’antun ƙera makamai masu linzami masu gudun walƙilya.
Hakan na zuwa ne kuma bayan Majalisar Dokokin Iran ta amince da ƙudirin rufe mashigar tekun Hormuz, matakin da Amurka ta buƙaci China ta sa baki Iran ɗin ta janye.
A gefe guda kuma Iran ta ci gaba da ruwan rokoki a kan Isara’ila, wadda ta fara kai wa cibiyoyin nukiliyar da na harkokin soji da fararen hula hari a ranar 13 ga watan nan na Yuni.