Aminiya:
2025-11-08@20:12:59 GMT

Gidauniya ta yi wa masu cutar gwaiwa dubu 12 tiyata kyauta a Katsina

Published: 10th, May 2025 GMT

Gidauniyar attajirin ɗan kasuwar nan na Jihar Katsina, Alhaji Dahiru Mangal, ta yi wa masu fama da cutar gwaiwa da taruwar ruwa a wasu sassan jiki fiye da 12,300 tiyata kyauta.

Da yake yi wa wakilin bayani, Malam Husaaini Kabir, mamba a kwamitin amintattu na gidauniyar ne ya tabbatar da hakan a Katsina, a lokacin ƙaddamar da aikin kashi na biyu.

Za a faɗaɗa Gasar Kofin Duniya ta Mata zuwa ƙasashe 48 — FIFA Sauya sheƙa bayan cin moriyar jam’iyya butulci ne — Kwankwaso

Kabir ya bayyana cewa gidauniyar tana gudanar da aikin tiyatar da bayar da magani kyauta a duk bayan watanni uku tun lokacin da aka kafa ta a shekarar 2013.

Ya ƙara da cewa, “majinyata masu rauni tsakanin 500 zuwa 600 ne ke cin gajiyar aikin tiyatar gwaiwar da na rage ruwan kyauta a jihar.

“Wannan shiri ba wai yana taimaka wa mutanen garin Katsina ne kawai ba, yana kuma tallafa wa mazauna ƙauyukan jihar da kuma yankunan da ke makwabtaka da su.

“Manufarmu ita ce rage nauyin biyan kuɗin kiwon lafiya ga mutane masu ƙaramin ƙarfi waɗanda ke gwagwarmaya don biyan buƙatun yau da kullun,” in ji shi.

Kabir ya buƙaci sauran ƙungiyoyi da masu hannu da shuni da su tallafawa irin wannan shiri, musamman don taimaka wa ƙoƙarin gwamnati a fannin kiwon lafiya.

Ya jaddada mahimmancin aikin tare don tunkarar ƙalubalen kiwon lafiya a cikin al’ummomin da ba a yi musu hidima ba.

Wasu da suka ci gajiyar shirin sun yaba da shirin tare da ƙarfafa gwiwar gwamnati, ƙungiyoyi masu zaman kansu, da masu hannu da shuni da su yi koyi da hakan.

Sun bayyana cewa sun jure yanayin da suke ciki na tsawon shekaru amma ba za su iya yin tiyatar ba saboda matsalar tattalin arziki.

Aminiya ta ruwaito cewa gidauniyar ta kuma bayar da maganin ido da tiyata kyauta ga marasa lafiyar idon a jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gidauniyar Mangal Gwaiwa Jihar Katsina Tiyata

এছাড়াও পড়ুন:

Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko

Sunana Lawan Isma’il (Lisary), Rano, A Jihar Kano:

Haduwa da kawayen banza da kuma kuntatawa da wasu malaman suke nuna musu, saboda kin amincewa da su na bukatun da suke nema a wajensu. Da yawa iyayen ba sa tsayawa su saurari matsalolin ‘ya’yansu kan abin da ke damunsu a makaranta, da kuma rashin bibiyar karatunsu da abokansu. Iyaye su tabbatar da suna bawa yara kudi da kayan abincin da zai ishesu idan a makarantun kwana suke, sannan su tabbatar da tarbiyyar malaman da za su kai yaran nasu.

Sunana Aisha Isah Gama (Mai Waka), Jihar Kano:

A gaskiya abin da ke janyo wa baya wuce gurba tattun abokai, har da lefin malamai saboda malami ne za ka ga ya kulla soyayya da daliba, kin ga matsala ta farko kenan, sai mu’amala da kawaye marasa tarbiyya, za ki ga baki ragi ‘yar ki da komai ba, amma kawaye sun bata ta. Shawara iyaye mu kula da ‘ya’yanmu, mu ja su a jiki su zama abokan mu, mu rika tunawa kiwo Allah ya ba mu kuma zai tsayar damu ya yi mana tambaya akan kiwon da ya bamu, mu raba su da kawaye.

Sunana Hauwa Abubakar Sarki, daga Suleja, Jihar Neja:

Sautari malamai su ne silar lalacewar dalibai akowane makaranta, daga na islamiyar har na bokon. Ka ga malami ya rasa wacce zai yi soyayya da ita sai dalibar sa, duk da ba haramun bane, amma ba sa bin hanyar da ya dace wajan neman soyayyar daliban nasu. Malamai su ne silar lalacewar wasu daga cikin dalibai, daga lokacin da malami ya nuna kwadayi akan abin hannun dalibar sa walau surar da Allah yayi mata ko kuma abun hannuta (kudi) babu magnar tarbiyya a nan wajan. Sautari babu kyau, saboda duk inda aka ce malami to fa matsayin uba yake ga dalibansa. Su ma kuma dalibai su kasance masu kamu kai da nuna kyakkyawan tarbiyya a duk inda suke.

Sunana Hafsat Sa’eed:

Sai dai in ba tarbiyya suka samu tun farko ba,idan har sun samu tarbiyya, kuma an magance musu matsalolin da ba za su ga wani abu su yi sha’awa ba, ba na tunanin yaro zai lalace. Amma rashin hakan yaro na iya shiga cikin wani yanayi. Wasu kuma akwai tarbiyyar amma sakamakon haduwa da kawaye sai su canja, domin kawa tana iya canja kawa a lokaci daya. Amma akwai wadanda jarrabawa ce, idan Allah ya jarabce ka babu yadda za ka yi sai ka karba ka yi ta addu’a.

Sunana Muktari Sabo Jahun A Jihar Jigawa:

Na farko dai akwai matsalar Tarbiyya wadda ita ce tushen komai, sannan kuma da rashin gata ga wasu, wasu kuma neman abin duniya ne yake kai su ga lalacewa. Munanan abokai kan iya bata abokansu, haka kuma rashin bibiyar iyaye akan lamarin ‘ya’yansu har sai sun fada wani hali. Iyaye su sa hankali da lura akan yaransu, kuma su dage da yi musu addu’a, kuma su san su waye abokan ‘ya’yansu.

Sunana Fatima Nura kila, Jihar Jigawa:

Abin da yake janyo wa mafiya yawa shi ne, san zuciya, kusan shi ne kaso 70% na lalacewar dalibai mata a makarantu. Yana faruwa ne mata sun dau karya sun dorawa rayuwarsu, wata iyayenta rufin asiri gare su, za ta ce sai ta yi abin da kawarta ta yi, bayan samun iyayen kowanne daban. Shawarar ita ce, a kodayaushe mu mata mu daina kallan saman mu, a kodayaushe mu rika kallon kasan mu, hakan shi ne zai sa mana wadatar zuci.

Sunana Hassana Sulaiman, Hadejia, A Jihar Jigawa:

Daga cikin abin da ke kawo lalacewar dalibai musamman ma mata a makarantun boko da kuma islamiyya cikin al’umma, wani lokacin rashin sanin su kansu ne da iyayen basu fiya duba da lamuran yaran nasu matan ba. Dalilin lalacewar wasu daga cikin dalibai a wannan lokacin bai huce na kawaye ba. Saboda kawaye suna taka muhimmiyar rawa wani lokacin fiye ma da iyayensu. Ya kamata iyaye musamman mata, su zama kawaye ga ‘ya’yan nasu dan ta haka ne ‘ya’yan nasu matan za su iya sakin jiki da su suna zaman fira tare a hakan iyayen za su fahimci su waye ne ma yaransu, kuma wani abu ne a ransu wanda za su iya basu shawarar yadda za a magance matsalar maimakon lalacewar su ta sanadiyyar kawaye.

Sunana Hassana Yahaya Iyayi, Jihar Kano:

Yawanci soyayya da malamai ke yi da dalibai shi yake jawo wa. Kin ga kawaye sune kan gaba wajen canja wa yara dalibai tarbiyya da kuma ita soyayyar da malaman ke shinfidawa da yaran. Iyaye dai su rika kulawa da tarbiyyar ‘ya’yansu dan kuwa amana ce Allah ya dora a hannunsu.

Sunana Nabila Dikko, Argungu, Jihar Kebbi:

Lalacewar ɗalibai mata na yawaita ne saboda rashin kulawar iyaye, rinjayar abokai marasa tarbiyya da amfani da kafafen sada zumunta ba tare da iyaka ba. Wasu suna da kamun kai saboda tarbiyyar gida, wasu kuma babu. Shawara, iyaye su kula da ‘ya’yansu, dalibai kuma su tsare mutuncinsu, su mayar da hankali ga karatu.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Taskira Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu October 19, 2025 Taskira Tsokaci A Kan Mata Masu Tsananin Kishi October 12, 2025 Taskira Illolin Da Ke Tattare Da Mallaka Wa Kananan Yara Wayar Hannu October 4, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko
  • Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna
  • Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Ta Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Ayyukan Cigaban Jihar Jigawa
  • Ma’aikacin jinya ya kashe marasa lafiya 10 saboda aiki ya masa yawa
  • Sama da gidaje 8,000 za su samu wutar lantarki daga hasken rana a Gombe
  • Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026
  • Kwalara ta kashe mutum 10 a Ƙaramar Hukumar Adamawa
  • An kama mutum 2 kan sukar shugaban karamar hukuma a Kano
  • Masu Sa Ido na Tarayyar Afirka: Zaben Tanzania Ya Keta Ka’idojin Demokradiyya
  • NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Cutar Basir