HausaTv:
2025-09-24@15:50:06 GMT

Hamas ta yi tir da Isra’ila kan rufe makarantun MDD  

Published: 9th, May 2025 GMT

Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa, Hamas, ta yi kakkausar suka kan rufe makarantu guda 6 na MDD da Isra’ila ta yi a yammacin gabar kogin Jordan, tare da bayyana hakan a matsayin keta dokokin kasa da kasa

 ranar Alhamis 8 ga watan Mayu, Hamas ta bayyana cewa harin da aka kai kan makarantun hukumar agaji ta MDD UNRWA da ke birnin Quds da aka mamaye, da kuma rufe su da aka yi bayan korar dalibai da malamai da aka yi, ya zama harin kai tsaye ga daukacin tsarin MDD da cibiyoyinta.

Sanarwar da kungiyar Hamas ta fitar ta ce, irin wadannan matakai na aikata laifuka wani bangare ne na yakin da gwamnatin Isra’ila ke yi da wanzuwar Falasdinu da kuma asalinsu.

Don haka kungiyar ta yi kira ga Majalisar Dinkin Duniya da dukkanin hukumomin kasa da kasa da abin ya shafa da su dauki matakai na gaggawa don kawo karshen cin zarafi da gwamnatin Isra’ila ke yi tare da tabbatar da mayar da yara Falasdinawa sama da 800 zuwa ajujuwa.

Tuni dai kwamishinan hukumar ta UNRWA Philippe Lazzarini ya yi Allah wadai da hare-haren da Isra’ila ke kai wa makarantun hukumar, yana mai tunatar da cewa wadannan cibiyoyi na da kariya ce ta Majalisar Dinkin Duniya, kuma rufe su cin zarafin yara ne da kuma ‘yancin samun ilimi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

NEF za ta ƙaddamar da taron zuba jari don bunƙasa Arewa

Kungiyar Dattawan Arewa (NEF) ta ce a karon farko za ta shirya taron zuba jari da samar da masana’antu na Arewacin Najeriya, wanda aka shirya gudanarwa a ranakun 29 da 30 ga watan Satumba a Abuja.

Taron wanda aka shirya tare da hadin gwiwar jihohin arewa 19 da kuma kamfanin raya yankin – NNDC, na da nufin mayar da yankin a matsayin wata cibiya ta samun bunkasar tattalin arziki da habaka masana’antu.

An gudanar da bikin ɗaga tutar Falasɗinu a Birtaniya CAC ta soma yi wa kamfanoni rijista da fasahar AI

Da yake magana a taron manema labarai da aka gudanar ranar Litinin a Abuja, kakakin kungiyar, Farfesa Abubakar Jika Jiddere, ya bayyana taron a matsayin “kira domin zaburar da tattalin arziki da kuma tsare-tsare na cika alkawarin Arewacin Najeriya.”

Ya ce an tsara taron ne a cikin watanni 18 da suka gabata domin kaddamar da wani shiri na kishin kasa wanda zai karfafa ayyukan ci gaba da bude sabbin kafofin damammanki ga yankin, Najeriya da abokan huldar kasa da kasa.

“Wannan taron ba na siyasa ba ne, yana mai da hankali kan tattalin arziki, kan damammaki, da kuma samar da wadata. Yana da zimmar nuna karfin Arewacin Najeriya da kuma gabatar da hangen nesa na ci gaba, kirkire-kirkire, da haɗin gwiwa. Daga yau, za mu bude sabon babi,” in ji Jiddere.

Da yake yin la’akari da irin gudunmawar da yankin ya bayar a tarihi, ya tuna cewa a shekarun 1960 zuwa farkon 1980, Arewacin Nijeriya ya ba da karfin tattalin arzikin kasa ta hanyar noma, masana’antu, da kasuwanci. “Dalarmu na gyada ya kai sararin sama; auduga, fatu, dabbobi, da ma’adanai masu ƙarfi suna tallafawa masana’antu,” in ji shi.

Duk da haka, ya ce rashin tsaro da rashin zuba jari sun rage ci gaban yankin, wanda ya haifar da rikice-rikice na albarkatu masu yawa da kuma abubuwan da ba a san su ba, “Wannan taron yana manufa juya akalar rikicin zuwa ga damammaki da kuma tabbatar da cewa Arewacin Najeriya ya samu kwarin gwiwa zuwa wani sabon zamani na ci gaba,” in ji shi.

Jiddere ya zayyana ginshiƙai masu mahimmanci guda biyar da yankin yake tutiya da su kamar albarkar ƙasa da noma, manyan ma’adanai, albarkatun ɗan adam, ababen more rayuwa, da masana’antu, waɗanda ke samun tallafi kamar ilimi, kiwon lafiya, gidaje, da fasaha.

Ya nanata cewa Arewacin Najeriya “yana da alaƙa da kasa-wata babbar hanyar shiga Nijar, Chadi, Kamaru, Benin, Mali, da Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya.”

Ya ƙalubalanci masu ruwa da tsaki da su yi nazari a kan abubuwan da ba za a iya amfani da su a yankin ba, yana mai tambaya, “Ta yaya yankin da ya samar da shugabanni da masu ƙirkire-ƙirkire a duniya, ’yan ƙato da gora irin su Alhaji Aliko Dangote da Amina Mohammed, har yanzu bai nuna cikakken ƙarfin tattalin arzikinsa ba?

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Guguwar Amincewa Da Kasar Falasdinu Ta Nuna Yadda Amurka Da Isra’ila Suka Zama Saniyar Waren Da Ba A Taba Gani Ba
  • Kotu ta hana NUPENG rufe Matatar Ɗangote
  • CORET Ta Yaba Da Nasarar Shirin Ciyarda Daliban Makarantun Makiyaya
  • NEF za ta ƙaddamar da taron zuba jari don bunƙasa Arewa
  • Kasar Sin Na Matukar Goyon Bayan Tabbatar Da Adalci Ga Falasdinawa Wajen Maido Da Hakkinsu Na Kasa
  • An gudanar da bikin ɗaga tutar Falasɗinu a Birtaniya
  • Hamas ta bukaci kasashen duniya da MDD su mayar da Isra’ila saniyar ware
  • CAC ta soma yi wa kamfanoni rijista da fasahar AI
  • An rufe sansanin NYSC da kasuwanni saboda rashin tsaro a Kwara
  • An kashe jami’an tsaro 53 a cikin mako biyu —Bincike