HausaTv:
2025-06-24@10:45:57 GMT

Hamas ta yi tir da Isra’ila kan rufe makarantun MDD  

Published: 9th, May 2025 GMT

Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa, Hamas, ta yi kakkausar suka kan rufe makarantu guda 6 na MDD da Isra’ila ta yi a yammacin gabar kogin Jordan, tare da bayyana hakan a matsayin keta dokokin kasa da kasa

 ranar Alhamis 8 ga watan Mayu, Hamas ta bayyana cewa harin da aka kai kan makarantun hukumar agaji ta MDD UNRWA da ke birnin Quds da aka mamaye, da kuma rufe su da aka yi bayan korar dalibai da malamai da aka yi, ya zama harin kai tsaye ga daukacin tsarin MDD da cibiyoyinta.

Sanarwar da kungiyar Hamas ta fitar ta ce, irin wadannan matakai na aikata laifuka wani bangare ne na yakin da gwamnatin Isra’ila ke yi da wanzuwar Falasdinu da kuma asalinsu.

Don haka kungiyar ta yi kira ga Majalisar Dinkin Duniya da dukkanin hukumomin kasa da kasa da abin ya shafa da su dauki matakai na gaggawa don kawo karshen cin zarafi da gwamnatin Isra’ila ke yi tare da tabbatar da mayar da yara Falasdinawa sama da 800 zuwa ajujuwa.

Tuni dai kwamishinan hukumar ta UNRWA Philippe Lazzarini ya yi Allah wadai da hare-haren da Isra’ila ke kai wa makarantun hukumar, yana mai tunatar da cewa wadannan cibiyoyi na da kariya ce ta Majalisar Dinkin Duniya, kuma rufe su cin zarafin yara ne da kuma ‘yancin samun ilimi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran ta kama ’yan leƙen asirin Isra’ila 6
  • Amurka ta roƙi China ta sa baki kada Iran ta rufe mashigar tekun Hormuz
  • Mutum 2 sun mutu a ƙoƙarin ciro waya daga masai a Kano
  • Mutum 2 sun mutum a ƙoƙarin ciro wata daga masai a Kano
  • Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?
  • Gwamnatin Hong Kong Ta Gudanar Da Bikin Cika Shekaru Biyar Da Kafuwar Dokar Tsaron Kasa Ta Yankin
  • HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar ’yan ɗaurin auren da aka kashe a Filato
  • Amurka za ta gamu da fushinmu kan shigar wa Isra’ila yaƙinta da Iran — Houthi
  • CMG Ya Ja Hankulan Baki A Dandalin Tattaunawar Tattalin Arziki Na Kasa Da Kasa Na St. Petersburg Karo Na 28 
  • Wakilin Sin Ya Yi Kira A Yayyafa Ruwa Ga Rikicin Isra’ila Da Iran