Hamas ta yi tir da Isra’ila kan rufe makarantun MDD
Published: 9th, May 2025 GMT
Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa, Hamas, ta yi kakkausar suka kan rufe makarantu guda 6 na MDD da Isra’ila ta yi a yammacin gabar kogin Jordan, tare da bayyana hakan a matsayin keta dokokin kasa da kasa
ranar Alhamis 8 ga watan Mayu, Hamas ta bayyana cewa harin da aka kai kan makarantun hukumar agaji ta MDD UNRWA da ke birnin Quds da aka mamaye, da kuma rufe su da aka yi bayan korar dalibai da malamai da aka yi, ya zama harin kai tsaye ga daukacin tsarin MDD da cibiyoyinta.
Sanarwar da kungiyar Hamas ta fitar ta ce, irin wadannan matakai na aikata laifuka wani bangare ne na yakin da gwamnatin Isra’ila ke yi da wanzuwar Falasdinu da kuma asalinsu.
Don haka kungiyar ta yi kira ga Majalisar Dinkin Duniya da dukkanin hukumomin kasa da kasa da abin ya shafa da su dauki matakai na gaggawa don kawo karshen cin zarafi da gwamnatin Isra’ila ke yi tare da tabbatar da mayar da yara Falasdinawa sama da 800 zuwa ajujuwa.
Tuni dai kwamishinan hukumar ta UNRWA Philippe Lazzarini ya yi Allah wadai da hare-haren da Isra’ila ke kai wa makarantun hukumar, yana mai tunatar da cewa wadannan cibiyoyi na da kariya ce ta Majalisar Dinkin Duniya, kuma rufe su cin zarafin yara ne da kuma ‘yancin samun ilimi.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Hizbullah: Amurka na hakoron taimaka wa ajandar Isra’ila ne a kan Lebanon
Kungiyar Hizbullah ta yi gargadin cewa Lebanon da yankin gabas ta tsakiya na fuskantar daya daga cikin yanayi mafi hadari a tarihin baya-bayan nan, inda al’ummar yankin ke fuskantar barazanar wanzuwa da kuma ‘yancinsu.
A cikin wata sanarwa da ta fitar bayan taronta na yau da kullun, kungiyar ta yi Allah wadai da yadda Isra’ila ke ci gaba da ruruta wutar rikici a yankin gabas ta tsakiya tare da goyon bayan Amurka da wasu kasashen yammacin duniya da na larabawa, a wani bangare na yunkurin sake fasalin yankin da kasar Lebanon.
Babban abin da kungiyar tafi nuna takaicinta akansa shi ne amincewar da gwamnatin Lebanon ta yi a baya-bayan nan da shawarar da manzon Amurka Tom Barrack ya gabatar.
Kungiyar ta bayyana matakin a matsayin wani sabon salo na saba alkawuran ministocin gwamnati da kuma karya rantsuwar da shugaban kasa ya yi. Ta nanata cewa takardar ta sabawa ka’idojin yarjejeniyar Taif, wadda ta tabbatar da ‘yancin kare kai da kuma kiyaye ‘yancin kasar Lebanon.
Kungiyar ta bayyana amincewar da gwamnatin kasar ta yi wa takardar Amurka a matsayin rashin gaskiya,” tana mai gargadin cewa irin wannan matsayi a file yake kan cewa ya keta yarjejeniyar kasa” tare da yin barazanar kwace wa kasar Lebanon daya daga cikin manyan hanyoyin karfinta, wato gwagwarmayar sa kai domin kare kasa.
Kungiyar ta kuma tabbatar da cewa, karfinta na soji wani babban jigo ne kuma ginshiki a fagen tsaron kasar Lbanon, musamman ma ganin yadda ake samun karuwar barazana da kuma rashin wani tabbataccen lamuni na kasa da kasa.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ramaphosa da Putin sun tattauna rikicin Ukraine da batutuwan da suka shafi kasashensu August 8, 2025 Australia ta gargadi Isra’ila game da yunkurin mamaye Gaza August 8, 2025 Axios: Majalisar ministocin Isra’ila ta amince da sabon shiri na mamaye birnin Gaza August 8, 2025 Iran Ta Kira taron Gaggawa Na Kungiyar Kasashen Musulmi August 8, 2025 Iraniyawa Miliyon 1.2 Ne Suka Shiga Iraki Ta Kofar Shiga Na Mehran August 8, 2025 Ansarullah Ta Yi Gargadi Ga Amurka Da HKI Kan Kara Tada Hankali A Yakin August 8, 2025 Hizbullah Da Amal Sun Yi Tir da Shirin Kwance Damarar Hizbullah August 8, 2025 Jirgin Daukar Marasa Lafiya Ya fadi A kasar kenya Ya Kuma Kashe Akalla mutane 6 August 8, 2025 Araqchi: Hari Kan Cibiyoyin Nukiliyar Iran Ba Zai Taba Canza Matsayinta Ba August 7, 2025 Manjo Janar Mousawi: Martanin Iran Nan Gaba Zai Kasance Mafi Muni Kan Makiya August 7, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci