Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Published: 14th, May 2025 GMT
Ma’aikatar cinikayya ta kasar Sin ta bayyana cewa, kasar za ta kara inganta kula da duk wani abu mai nasaba da sarrafawa ko samarwa a bangaren ma’adanan kasa masu matukar muhimmanci, don hana fitarwa ba bisa ka’ida ba, da kuma kiyaye tsaron kasa.
Mai magana da yawun ma’aikatar wanda ya bayyana haka a yau Laraba, ya ce, karfafa yadda ake kula da fitar da albarkatun ma’adanai masu muhimmanci zuwa ketare yana da muhimmanci ga tsaron kasa da muradun ci gaba.
A ranar Litinin da ta gabata ne, wani taron kasa da aka kira a Changsha, babban birnin lardin Hunan, ya jaddada bukatar karfafa “kula da cikakken tsarin fitar da manyan ma’adanai masu muhimmanci zuwa kasashen waje.” Taron ya samu halartar jami’ai daga hukumomin gwamnatin tsakiya 10 da yankuna bakwai masu arzikin muhimman ma’adanai, ciki har da jihar Mongoliya ta gida da lardin Jiangxi.
Mai magana da yawun ma’aikatar ya kara da cewa, “Domin hana fitar da ma’adanai masu muhimmanci ba bisa ka’ida ba, dole ne a fara kula da lamarin daga tushe kuma a karfafa shi a dukkan sassan harkar ma’adanai, da suka hada da hakawa, narkawa, sarrafawa, sufuri, masana’antu, sayarwa, da kuma fitarwa zuwa kasashen waje.” (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
NDLEA ta kafa cibiyar kula da masu shaye-shaye a Yobe
Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA) ta kafa karamar cibiyar kula da muggan kwayoyi a Damaturu babban birnin jihar Yobe.
Kwamandan hukumar a Jihar, Abdulazeez Ogunboye ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Damaturu a wani bangare na bikin ranar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta duniya ta shekarar 2025.
Tinubu ya rattaba hannu kan sababbin dokokin haraji Sheikh Dahiru Bauchi ya cika shekara 101 a duniyaOgungboye ya kara da cewa cibiyar wacce tun daga lokacin da ta fara aiki na daya daga cikin nasarorin da hukumar ta samu a jihar.
“An shigar da mutane tara da suke ta’ammali da muggan kwayoyi a cibiyar, daga cikin su an samu nasarar gyara halayyar mutum takwas halayyar su, an sallame su tare da sake haduwa da iyalansu, yayin da daya ke ci gaba da karbar hoton gyaran hali.
“Daya daga cikinsu yanzu haka ya samu tallafin fara gudanar da harkokin kasuwanci don dogaro da kai tare da watsar da waccar mummunar dabi’a ta ta’ammali da muggan kwayoyi,” in ji Ogunboye.
Kwamandan ya ce bisa la’akari da tsadar ayyuka a cibiyar, hukumar ta hada kai da masu hannu da shuni a jihar domin taimaka wa a wannan kokarin gyaran halim masu ta’ammali da kwayoyin.
Kwamandan ya kuma shawarci masu shaye-shaye a kananan hukumomi 17 na jihar da su tuntubi kwamandojin shiyya na hukumar da ke kusa da su kan yadda za su shiga wurin, wanda ya ce shi ne irinsa na farko a tarihin jihar.