Jagora: Ma’aikata Su Ne Jari Mafi Girma Domin Cimma Manufar Bunkasa Tattalin Arziki
Published: 10th, May 2025 GMT
Jagoran juyin musulunci na Iran Ayatullah Sayyid Ali Khamnei ya fada a yau Asabar cewa: Ma’aikata ne jari mafi muhimmanci na samun zaman lafiya a cikin al’umma da kuma cimma manufar sunan da aka bai wa wannan shekarar na : “Zuba Hannun Jari Domin Yin Kere-Kere.”
Ayatullah Sayyid Ali Khamnei wanda ya gana da ma’aikata da su ka fito daga sassan Iran, ya yi ishara da sake bude kamfanoni da dama a zamanin shugabancin Shahid Ra’isi, alhali gabaninsa an rufe su,tare da bayyana hakan da cewa daya ne daga cikin ayyukan da Shahidin ya aiwatar.
Jagoran juyin musuluncin na Iran ya kuma bayyana ma’aikatar da cewa, su nekashin bayan kowace al’umma, yana kuma mai yin addu’ar Allah ya ba su dacewa a cikin ayyukan da su ka Sanya a gaba.
Ayatullah Sayyid Ali Khamnei ya kuma ishara da cewa bude kasa domin shigo da haja abu ne mai sauki, amma a lokaci daya yana karya kasa, don haka abinda ya zama wajibi shi ne a kare yin kere-kere daga cikin gida.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun kashe kansila yayin Zaɓen Gwamnan Anambra
Wasu ‘yan bindiga sun kashe wani kansila mai suna Nze Ala Kuru Orji yayin da ya fita jefa ƙuri’arsa a rumfar zaɓe da ke ƙauyen Orumba, a yankin ƙaramar hukumar Orumba ta Kudu, lokacin zaɓen gwamnan Jihar Anambra da aka gudanar ranar Asabar da ta gabata.
Rahotanni sun nuna cewa, lamarin ya faru ne da ranar Asabar, a akwatin zaɓe na mazabar Ezukaka 1, da misalin ƙarfe ɗaya na rana.
Ban taɓa zargin Shettima da ƙirƙiro Boko Haram ba — Sheriff Yaran Bello Turji sun kashe mutum 5, sun sace 9 a SakkwatoWani ganau ya shaida wa wakilinmu cewa: “Ana tsaka da jefa ƙuri’a sai wasu matasa da ke sanye da abun rufe fuska suka bayyana, suka harbe mutumin nan kafin kowa ya ankara. Daga nan suka tsere da motarsu ba tare da sun cutar da wani ba.”
Wannan lamari ya jefa masu jefa ƙuri’a cikin firgici da tsoro, inda wasu suka bayyana damuwa kan abin da ka iya biyo baya kafin a kammala zaɓen.
Wani mazaunin yankin da ke wurin a lokacin faruwar lamarin ya ce: “Abin ya firgita mu. Ana zaune lafiya kawai sai a ji an kashe mutum haka. Wannan abu ya girgiza mu sosai domin ba a taɓa samun matsala irin wannan a mazabar nan ba.”
Shi ma wani mai suna Odemenna, wanda ya kasance a wurin, ya tabbatar da cewa jami’an tsaro sun isa yankin domin gudanar da bincike da kuma neman waɗanda suka aikata wannan aika-aika.
A cewar wani mazaunin yankin, Chukwudi Chinanso: “Maharan sun kai harin ne kan kansilan, kuma sun yi sa’ar tarar da shi ne lokacin da ya zo jefa ƙuri’a. Da nan suka harbe shi suka gudu.”
Haka zalika, wata mata mai suna Joyce Okoro ta shaida cewa: “Wasu matasa ɗauke da muggan makamai sun zo mazabar mu suka harbe kansilan sannan suka tsere.”
Rahotanni sun nuna cewa ana zargin rikicin siyasa ne ya haddasa kisan, kasancewar Nze Ala Kuru Orji ɗaya ne daga cikin shugabannin jam’iyyar APGA a mazabar.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Anambra, SP Tochukwu Ikenga, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce jami’ansu sun shiga bincike domin cafke masu hannu a cikin wannan ɗanyen aiki.