Jagoran juyin musulunci na Iran Ayatullah Sayyid Ali Khamnei  ya fada a yau Asabar cewa: Ma’aikata ne jari mafi muhimmanci na samun zaman lafiya a cikin al’umma da kuma cimma manufar sunan da aka bai wa wannan shekarar na : “Zuba Hannun Jari Domin Yin Kere-Kere.”

Ayatullah Sayyid Ali Khamnei wanda ya gana da ma’aikata da su ka fito daga sassan Iran, ya yi ishara da sake bude kamfanoni da dama a zamanin shugabancin Shahid Ra’isi, alhali gabaninsa an rufe su,tare da bayyana hakan da cewa daya ne daga cikin ayyukan da Shahidin ya aiwatar.

Jagoran juyin musuluncin na Iran ya kuma bayyana ma’aikatar da cewa, su nekashin bayan kowace al’umma, yana kuma mai yin addu’ar Allah ya ba su dacewa a cikin ayyukan da su ka Sanya a gaba.

Ayatullah Sayyid Ali Khamnei ya kuma ishara da cewa bude kasa domin shigo da haja abu ne mai sauki, amma a lokaci daya yana karya kasa, don haka abinda ya zama wajibi shi ne a kare yin kere-kere daga cikin gida.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Xi Jinping Zai Halarci Bikin Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan Da Yakin Kin Tafarkin Murdiya

Ofishin yada labarai na majalisar gudanarwar kasar Sin, ya bayyana cewa, shugaban kasar Xi Jinping, zai halarci bikin tunawa da cika shekaru 80 da cimma nasarar yakin kin jinin harin sojojin Japan, da yakin kin tafarkin murdiya, da safiyar ranar 3 ga watan Satumban bana, tare da gabatar da jawabi. Kazalika a ranar, kasar Sin za ta gudanar da gagarumin bikin faretin soja a filin Tian’anmen dake nan Beijing, inda shugaba Xi zai duba faretin. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Xi Jinping Zai Halarci Bikin Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan Da Yakin Kin Tafarkin Murdiya
  • Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Mako 3
  • Amurka ta roƙi China ta sa baki kada Iran ta rufe mashigar tekun Hormuz
  • Yakin Iran Da Isra’ila Ya Haifar Da Tashin Farashin Litar Man Fetur A Nijeriya
  • Mutum 2 sun mutu a ƙoƙarin ciro waya daga masai a Kano
  • Mutum 2 sun mutum a ƙoƙarin ciro wata daga masai a Kano
  • 2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega
  • Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u
  • Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?
  • Matsalolin Rayuwa: Matasan Suleja Na Buƙatar Ƙarfafa Gwuiwa