Oloyede, wanda ya bayyana tangardar a matsayin “zagon kasa” ga shirin jarabawar UTME ta 2025, ya ce, wadanda abin ya shafa za su fara samun sako a wayar salularsu daga Hukumar daga ranar Alhamis, 15 ga Mayu, 2025.

 

Daga cikin dalibai miliyan 1.9 da suka zana jarabawar UTME ta shekarar 2025, sama da miliyan 1.

5 aka bayar da rahoton, sun samu maki kasa da 200 daga cikin mafi girman maki 400, lamarin da ya haifar da damuwa a bangaren ilimi na kasar.

 

UTME ta wannan shekara, ta gamu da koma baya sosai, wanda ya haifar da damuwa tsakanin ɗalibai, iyaye, da malamai.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

Taron dandalin tattaunawa kan tattalin arzikin duniya na lokacin zafi na Davos, wanda aka gudana a tsakanin ranar 24 zuwa ranar 26 ga watan nan da muka ciki, a birnin Tianjin na kasar Sin, ya samu halartar wakilai kimanin 1800 daga kasashe da yankuna sama da 90, adadin da ya kai koli cikin tarihi. Kamar yadda babban daraktan dandalin Davos Borge Brende ya bayyana, “in muka duba yanayin kasashen duniya, za a gane cewa, wakilai a fannonin masana’antu da kasuwanci na kasashe da dama, suna fatan zuba jari a kasar Sin, tare da zurfafa hadin gwiwar cinikayya dake tsakaninsu da kasar Sin.”

A halin yanzu, kasuwannnin kasar Sin suna ci gaba da samun kyautatuwa da karuwa, lamarin da ya samar da damammaki ga bunkasar hadin gwiwar cinikayya a tsakanin kasa da kasa. Ci gaba da yin kirkire-kirkire a kasar Sin, ya samar da sabon karfi na neman samun bunkasa. A ciki kuma, bunkasar fasahar kwaikwayon tunanin dan Adam ta AI ta janyo hankulan jama’a cikin taron Davos. Masana na ganin cewa, idan muka yi amfani da fasahohin da abin ya shafa kan aikin nazarin sabbin kayayyaki, zai ninka saurin gudana da ayyukanmu sau 100 har ma zuwa sau 1000. Kuma kasar Sin za ta taka muhimmiyar rawa cikin wannan babban sauyi.

Haka kuma, cikin farkon watanni 5 na bana, an kafa sabbin kamfanoni masu jarin waje guda 24,018 a cikin kasar Sin, adadin da ya karu da kaso 10.4 bisa dari idan aka kwatanta da na makamancin lokacin bara. Kamfanonin kasashen duniya sun nuna fatansu na hada kai da kasar Sin. Kamar yadda tsohon firaministan kasar Burtaniya Tony Blair ya bayyana a yayin taron Davos cewa, “ya kamata a ci gaba da tuntubar kasar Sin a kai a kai.” (Mai Fassara: Maryam Yang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 
  • Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
  • An Fara Gudanar Da Jana’izar Shahidan Yakin Kwanaki 12 A nan Tehran
  • Iran Ta Shigar Da Korafi A Hukumar Kare Hakkin Bil’adama Ta MDD
  • Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
  • JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa
  • Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai
  • Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC
  • Ganduje ya yi murabus daga shugabancin jam’iyyar APC
  • Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS