Shugaban kasar Iran ya jaddada cewa: Iran ba zata taba yin watsi da haƙƙinta na makamashin nukuliya na zaman lafiya ba a kowane yanayi

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya bayyana cewa: Iran da gaske take yi wajen gudanar da tattaunawa domin neman cimma matsaya da zata gamsar da kowane bangare, amma neman yin watsi da cibiyoyin nukiliyarta ba abu ne da za a amince da shi ba.

A yammacin jiya Lahadi ne jami’an gwamnatin kasar Iran suka gudanar da wani taro karkashin jagorancin shugaban kasar Masoud Pezeshkian, inda ya jaddada aniyar gwamnatin kasar na kare nasarorin da Iran ta a fagen ayyukanta na zaman lafiya, yana mai jaddada cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba ta taba neman mallakar makamin nukiliya ba, kuma ba ta nemansa a yanzu, kuma ba za ta nemi mallakar makamin nukiliya a nan gaba ba.

Shugaban na Iran ya kara da jaddada matsayar Iran kan wannan lamari: Suna da matsaya na akida, kuma a cewar fatawar Jagoran juyin juya halin Musulunci, neman makamin nukiliya haramun ne a addinance, to sai dai abin da ake gabatar da shi dangane da yin watsi da dukkanin cibiyoyin nukiliyar Iran abu ne da ba za a taba amince da shi ba, ire-iren gagarumar nasara da Iran ta samu a fagage ilimummuka masu yawa misalin, samar da magunguna, harkar noma, kyautata muhalli, da bunkasa masana’antu, kuma zata ci gaba da ayyukanta na nukiliya na zaman lafiya da cikakken karfi.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Shugaban kasar

এছাড়াও পড়ুন:

Putin  Na Rasha Ya Gana Da Shugabannin Afirka Akan Batun Tsaro

Shugaban kasar Rasha Vladmir Putin ya karbi bakuncin shugabannin kasashen Afirka da su ka hada na Zimbabwe da na Burkina Fasa, inda su ka tattaunawa hanyoyin karfafa alaka a tsakanin kasashen nasu.

Shugaban kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa da na Burkina Faso Ibrahim Taraore sun isa birnin Moscow domin halartar bikin cika shekaru 80 da samun nasara akan ‘yan Nazi na Jamus a lokacin yakin duniya na 2.

Bugu da kari shugaban kasar ta Rasha ya kuma gana da shugaban gwamnatin kwarya-karyar Falasdinawa Mahmmud Abbas Abu Mazin,inda su ka yi musayar ra’ayi akan yadda za a kawo karshen kisan kiyashin da HKI take yi wa al’ummar Falasdinu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Kaduna Za Ta Sanya Mutane 700 Cikin Tsarin Kiwon Lafiya Na Jiha
  • Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Matsayin Kasarsa Na Tattaunawa Da Amurka
  • Kashi 42 Na Ma’aikatan Jinya Na Niyyar Barin Afirka Saboda Rashin Albashi – WHO
  • Putin  Na Rasha Ya Gana Da Shugabannin Afirka Akan Batun Tsaro
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Gana Da Tokwaransa Na Kasar Saudiya A Jiya Asabar
  • Shugaban Putin Ya Gana Da Sisi Don Karfafa Harkokin Kasuwanci Tsakanin Kasashen Biyu
  • Jagora Ya Jaddada Wajabci Daukan Matakan Kalubalantar Zaluncin ‘Yan Sahayoniyya
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Yi Allah Wadai Da Kai Hari Kan Ofishin Jakadancin Kasarsa A Kasar Sweden
  • Majalisar Da Take Kula Da Nukiliyar Pakistan Za Su Yi Taron Gaggawa