Aminiya:
2025-08-11@20:43:14 GMT

Kwalara ta yi ajalin mutum 4 a Filato

Published: 13th, May 2025 GMT

Ɓarkewar cutar kwalara ta yi ajalin mutum huɗu yayin da wasu gommai suka kwanta jinya a yankunan Ƙaramar Hukumar Bokkos ta Jihar Filato.

Aminiya ta ruwaito cewa yankunan da abin ya shafa sun haɗa da Hurti, Bokkos ta Yamma, Bokkos ta Tsakiya da kuma Mangol.

’Yan bindiga sun yi awon gaba da mutum 5 a Filato Jami’ar Maryam Abacha ta rufe ɗakunan kwanan ɗalibai a Kano

Galibin waɗanda ake zargi sun harbu da cutar an killace su a cibiyoyin lafiya a matakin farko daban-daban da kuma Asibitin Cottage inda suke samun kulawar gaggawa.

Shugaban Ƙaramar Hukumar Bokkos, Mista Amalau Samuel Amalau wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce suna aiki tare da mahukuntan asibitin domin daƙile ƙalubalen

A cewarsa, wasu daga cikin waɗanda ke fama da rashin lafiyar sun fara samun sauƙi yayin da tuni an sallami wasu daga asibiti.

Sai dai shugaban ƙaramar hukumar ya gargaɗi mazauna da su riƙa taka-tsan-tsan wajen kiyaye dokokin da mahukuntan lafiya suka shar’anta domin kaucewa kamuwa da cutar musamman tsaftace jiki, muhalli da kuma uwa-uba abinci.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Filato Kwalara

এছাড়াও পড়ুন:

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

Bayan da aka ɗaura auren, masoyanta da abokan aikinta suka tura mata saƙonni taya murna daga sassa daban-daban na Nijeriya.

Wannan aure ya zo watanni kaɗan bayan rasuwar mahaifinta, wanda ya rasu bayan gajeriyar rashin lafiya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za a gyara tarbiyar tubabbun ’yan daban Kano
  • Mahukuntan Iraki Sun Bayyana Cewa: Akwai Yiwuwar Masu Ziyarar Arba’een Na Imam Husaini {a.s} Zasu Zarce Miliyan 4
  • An kashe mutum 24 an sace 144 a mako guda a Zamfara — Rahoto
  • ‘Yan Sandan Nasarawa Sun Kama Mutum Shida Da Laifin Fashi Da Makami Da Garkuwa Da Mutane
  • Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam
  • Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara
  • Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas
  • EFCC ta kama ’yan damfara a ɗakin karatun Obasanjo 
  • An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna
  • ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya