HausaTv:
2025-06-26@21:01:03 GMT

Pakisatan Ta Kore Cewa Ta Keta Yarjejeniyar Tsagaita Wutar Yaki

Published: 11th, May 2025 GMT

 Ma’aikatar harkokin wajen kasar Pakistan ta jadada cewa ko kadan sojojin kasar ba su keta tsagaita wutar yaki da Indiya ba.

 A cikin wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen ta Pakistan ta fitar ta ce; kasar tana ci gaba da aiki da tsagaita wutar yaki wacce aka sanar da ita, kuma sojojin kasar sun kai zuciya nesa, duk da cewa Indiya ce ta keta wutar yakin.

Saanrwar da Pakistan ta biyo bayan zargin da Indiya ta yi wa kasar ne cewa tana keta yarjejeniyar wutar yaki bayan an cimma yarjejeniya a kan hakan.

Jami’i a ma’aikatar harkokin wajen Indiya Bigram Maisari ne ya bayyana hakan a wani taron manema labaru da ya gabatar a yau, sannan ya kara da cea; Muna yin kira ga kasar Pakistan da ta dauki matakan da su ka dace domin kawo karshen keta wutar yakin da take yi.

Shi kuwa Fira ministan yankin Jammo da Kashmir Umar Abdullah cewa ya yi an ji kararrakin fashewar abubuwa masu karfi a garin Sirinigar, da shi ne babbar birnin Kashmir dake karkashin Indiya.

Wasu shaidun ganin ido sun kuma bayyana cewa, an ga jirage marasa matuki suna zarya a sararin samaniyar yankin.

Tun da fari, Fira ministan Pakistan Shahbaz Sharif ya bayyana cewa; Kasarsa ta yi nasara akan makiya, yana mai jinjinawa sojojin kasar da su ka mayar da martani akan wuce gona da irin Indiya da karfi, kuma cikin kwarewa”

Shahbaz ya kuma ce; Indiya ta shelanta yaki akanmu ba tare da wani dalili ba, yana siffata abinda Indiya din ta yi da cewa; Abin kunya ne.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An Cafke Mutum 22 Kan Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato – Uba Sani

Wasu kuma sun jikkata a harin.

Gwamna Sani ya ce kisan rashin imani ne, kuma ya bayyana cewa ya tattauna da Gwamnan Filato, Caleb Mutfwang, da Shugaban Ƙasa Bola Tinubu don tabbatar da cewa an hukunta waɗanda suka aikata wannan aika-aika.

Ya kai ziyara ga waɗanda suka tsira daga harin a Asibitin Rundunar Sojin Naieriya na 44 da ke Kaduna, sannan ya yaba wa jama’ar Kaduna kan zaman lafiya da kaucewa fitina.

Ya kuma roƙi shugabannin Filato da su hana faruwar irin wannan mummunan lamari.

Gwamnan ya buƙaci hukumomin tsaro da su hanzarta kama masu laifin tare da gurfanar da su a gaban kotu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ba zan yi Tinubu ba a 2027 matukar ya canza Kashim Shettima – Sheik Jingir
  • Za mu ci gaba da tattaunawa da Iran kan yarjejeniyar nukiliya — Trump
  • Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba
  • Trump ya soki Iran da Isra’ila kan saɓa wa yarjejeniyar tsagaita wuta
  • Trump ya zargi Isra’ila da Iran da saɓa yarjejeniyar tsagaita wuta
  • Iran ta kama ’yan leƙen asirin Isra’ila 6
  • Iyalan Kanawa da aka kashe a Uromi sun zargin gwamnati da yin watsi da su
  • An Cafke Mutum 22 Kan Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato – Uba Sani
  • Iran da Isra’ila sun amince da tsagaita wuta —Trump
  • Trump ta ce Iran da Isra’ila sun amince da tsagaita wuta bayan harin Iran kan sansanonin Amurka