HausaTv:
2025-05-12@04:15:29 GMT

Pakisatan Ta Kore Cewa Ta Keta Yarjejeniyar Tsagaita Wutar Yaki

Published: 11th, May 2025 GMT

 Ma’aikatar harkokin wajen kasar Pakistan ta jadada cewa ko kadan sojojin kasar ba su keta tsagaita wutar yaki da Indiya ba.

 A cikin wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen ta Pakistan ta fitar ta ce; kasar tana ci gaba da aiki da tsagaita wutar yaki wacce aka sanar da ita, kuma sojojin kasar sun kai zuciya nesa, duk da cewa Indiya ce ta keta wutar yakin.

Saanrwar da Pakistan ta biyo bayan zargin da Indiya ta yi wa kasar ne cewa tana keta yarjejeniyar wutar yaki bayan an cimma yarjejeniya a kan hakan.

Jami’i a ma’aikatar harkokin wajen Indiya Bigram Maisari ne ya bayyana hakan a wani taron manema labaru da ya gabatar a yau, sannan ya kara da cea; Muna yin kira ga kasar Pakistan da ta dauki matakan da su ka dace domin kawo karshen keta wutar yakin da take yi.

Shi kuwa Fira ministan yankin Jammo da Kashmir Umar Abdullah cewa ya yi an ji kararrakin fashewar abubuwa masu karfi a garin Sirinigar, da shi ne babbar birnin Kashmir dake karkashin Indiya.

Wasu shaidun ganin ido sun kuma bayyana cewa, an ga jirage marasa matuki suna zarya a sararin samaniyar yankin.

Tun da fari, Fira ministan Pakistan Shahbaz Sharif ya bayyana cewa; Kasarsa ta yi nasara akan makiya, yana mai jinjinawa sojojin kasar da su ka mayar da martani akan wuce gona da irin Indiya da karfi, kuma cikin kwarewa”

Shahbaz ya kuma ce; Indiya ta shelanta yaki akanmu ba tare da wani dalili ba, yana siffata abinda Indiya din ta yi da cewa; Abin kunya ne.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Da Take Kula Da Nukiliyar Pakistan Za Su Yi Taron Gaggawa

Fira ministan kasar Pakistan Shahbaz Sharif ya kira yi Majalisar kasa wacce take kula da makaman Nukiliyar kasar  da su yi taro.

Wannan matakin da ake yi wa Kallon mai hatsari yana faruwa ne a daidai lokacin da kasar ta Pakistan take yaki da Indiya.

Ita  dai Majalisar  kasar Pakistan dake kula da makaman Nukiliya da kuma manufofin kasa na koli, ta kunshi manyan kwamandojin soja, da fararen hula, aikinta kuma  shi ne kula da manyan batutuwa da su ka shafi kasa daga ciki har da siyasar makaman Nukiliya da kuma makamai masu linzami.An kafa wannan majalisar ne dai a 2000.

Tashar talabijin din “Sama News” ta bayar da labarin dake cewa; Mahalarta taron za su yi bitar halin da ake ciki ne na yaki, da kuma tattaunawa matakan da za a dauka a fagen diplomasiyya da kuma hanyoyin tsaro da kare kai.

Ita dai kasar Indiya tana cewa ba za ta taba zama wacce za ta fara amfani da makamin Nukiliya ba, don haka ba za ta zama ta farko da za ta kai wa Pakistan hari ba. Ita kuwa Pakistan ta gina akidarta ta tsaro ne akan cewa za ta iya fara amfani da makamin Nukiliya da Zarar ta faminci cewa wanzuwar kasar tana fuskantar rushewa.

Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana aiki tukuru domin ganin ta shiga Tsakani da kawo karshen rikicin dake tsakanin kasashen biyu da suke makwabtanta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Na Fatan India Da Pakistan Za Su Kaucewa Kara Rura Wutar Tashin Hankali
  •   Iran Ta Yi Maraba Da Tsayar Da Wutar Yaki A Tsakanin Indiya Da Pakistan
  • Indiya da Pakistan sun cimma yarjejeniyar tsagaita wuta
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Ce Kafa Hujja Da ‘Yan Tawaye Kan Iran Yankewar Kauna ce Ga Makiyanta
  • Shugaban Amurka Ya Ce An Cimma Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Indiya
  • Majalisar Da Take Kula Da Nukiliyar Pakistan Za Su Yi Taron Gaggawa
  • Pakisatan Ta Maida Martanin Farmakin Sindoor Na Indiya Kan Rumbun Makamai Masu Linzami Na Indiya
  • IRGC Ya Kaddamar Da Sabon Sansanin Jiragen Yaki Na Karkashiun Kasa
  • Janar Salami: Muna  Cikin Shirin fuskantar Yaki A Duk Yadda Ya Zo