Aminiya:
2025-11-08@17:19:55 GMT

NAJERIYA A YAU: Abin ya sa aka kasa kawo ƙarshen Tamowa a Arewa Maso Gabas

Published: 9th, May 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Hukumomi a jihar Yobe sun ɗora alhakin ƙazancewar matsalar tamowa a kan rikicin Boko Haram da rashin shayar da jarirai nonon uwa yadda ya kamata da kuma gurɓacewar harkar kiwon lafiya, da sauran su.

Bayanin hakan na zuwa ne bayan Babban Jami’i mai Kula da Ayyukan Jinƙai na Majalisar Dinkin Duniya a Najeriya, Mista Mohamed Malick Fall, ya sanar cewa yara miliyan daya a jihohin Borno da Adamawa da Yobe suna fuskantar barazanar rasa rayukansu sakamakon cutar tamowa a bana.

An kuma ruwaito shi yana cewa wannan adadi ya ruɓanya na yaran da suka fuskanci barzanar a bara.

NAJERIYA A YAU: Ƙalubalen Da Iyaye Ke Fuskanta Wajen Tarbiyyar ’Ya’yansu DAGA LARABA: Ɓoyayyun Dalilan Da ke Sa Faɗuwa Jarabawa A Najeriya

Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari ne kan hanyoyin da za a bi don magance Tamowa a wasu jihohin Arewa maso Gabas.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Arewa maso Gabas tamowa yara

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya ta yi watsi da sanya sunanta cikin jerin kasashen da ake tauye ’yancin addini

Gwamnatin Tarayya ta yi watsi da matakin da Gwamnatin Amurka ta dauka na sanya sunan Najeriya cikin jerin “Kasashen Da Ake Tauye ’Yancin Addini” , wato jerin kasashen da ake zargi da take hakkin addini.

Ministan Yada Labarai da Al’adu, Mohammed Idris Malagi ne, ya bayyana hakan a ranar Laraba a Abuja, inda ya ce matsalar tsaro da ake fuskanta a Najeriya ba ta shafi wani rukuni na addini ko kabila kai-tsaye ba.

Gwamnatin Tarayya ta fara shirin sayar da matatun manta ga ’yan kasuwa Hafsan sojin sama ya umarci a yawaita yi wa ’yan ta’adda ruwan bama-bamai

Ya ce masu yada bayanan karya ne suka sa ake ganin kamar Najeriya tana nuna bambanci ta fuskar addini.

Malagi, ya ce gwamnati tana ci gaba da kokari wajen inganta harkar tsaro, sai dai ya bayyana cewa jami’an tsaro na wahala wajen isa wasu yankuna masu nisa a kan lokaci, don kai dauki.

Ya kara da cewa gwamnati na shirin dawo da tsarin tsaron al’umma domin tallafa wa rundunar tsaro ta kasa.

Da aka tambaye shi ko rashin nada jakadu ne ya haddasa wannan ce-ce-ku-ce da Amurka, Malagi ya ce dangantakar Najeriya da Amurka da sauran kasashe na tafiya daidai, kuma Shugaba Bola Tinubu na kokarin warware batun nada jakadu.

’Yan siyasar da suka fadi zabe ne ke yada labaran karya — Alake

A nasa bangaren, Ministan Harkokin Ma’adanai, Dele Alake, ya ce wasu ’yan siyasa da suka fadi a zabe ne ke yada labaran karya a Amurka cewa ana kashe Kiristoci a Najeriya.

Ya gargade su da cewa irin wadannan maganganu na iya haddasa karin tashin hankali wanda zai iya shafar kowa, ba tare da la’akari da addini ba.

Keyamo ya karyata zargin

Shi ma Ministan Harkokin Sufurin Jiragen Sama, Festus Keyamo, ya ce ikirarin Amurka karya ne, domin gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ba ta nuna wariyar addini.

Ya bayyana cewa yawancin manyan hafsoshin tsaro a Najeriya Kiristoci ne, sannan kuma Tinubu Musulmi ne matarsa Kirista, wacce malamar coci ce.

Keyamo, ya kara da cewa matsalolin tsaro a Najeriya suna shafar Musulmi da Kiristoci baki daya, don haka ya roki gwamnatin Amurka ta taimaka wajen yaki da ta’addanci maimakon dogaro da rahotannin karya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Barau ya nemi Trump ya janye kalamansa, ya nemi afuwar Najeriya
  • Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma
  • Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
  • Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump
  • Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 
  • Shugaban Najeriya Bola Tinubu Ya yi Alwashin Kawo Karshen Ta’addanci A Kasar
  • Sojin Amurka sun gabatar da shirin ƙaddamar da hari a Najeriya
  • Najeriya ta yi watsi da sanya sunanta cikin jerin kasashen da ake tauye ’yancin addini
  • Najeriya: Ta Sake Jaddada Yin Watsi Da Zargin Take Hakkin Kiristoci A Kasar
  • NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Cutar Basir