Aminiya:
2025-08-08@02:35:21 GMT

NAJERIYA A YAU: Abin ya sa aka kasa kawo ƙarshen Tamowa a Arewa Maso Gabas

Published: 9th, May 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Hukumomi a jihar Yobe sun ɗora alhakin ƙazancewar matsalar tamowa a kan rikicin Boko Haram da rashin shayar da jarirai nonon uwa yadda ya kamata da kuma gurɓacewar harkar kiwon lafiya, da sauran su.

Bayanin hakan na zuwa ne bayan Babban Jami’i mai Kula da Ayyukan Jinƙai na Majalisar Dinkin Duniya a Najeriya, Mista Mohamed Malick Fall, ya sanar cewa yara miliyan daya a jihohin Borno da Adamawa da Yobe suna fuskantar barazanar rasa rayukansu sakamakon cutar tamowa a bana.

An kuma ruwaito shi yana cewa wannan adadi ya ruɓanya na yaran da suka fuskanci barzanar a bara.

NAJERIYA A YAU: Ƙalubalen Da Iyaye Ke Fuskanta Wajen Tarbiyyar ’Ya’yansu DAGA LARABA: Ɓoyayyun Dalilan Da ke Sa Faɗuwa Jarabawa A Najeriya

Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari ne kan hanyoyin da za a bi don magance Tamowa a wasu jihohin Arewa maso Gabas.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Arewa maso Gabas tamowa yara

এছাড়াও পড়ুন:

Ɗaliba ’yar shekara 15 daga Yobe ta lashe Gasar Muhawara ta Duniya

Wata ɗaliba ’yar shekara 15 daga Jihar Yobe, Rukayya Muhammad Fema, ta zama Gwarzuwar Shekarar 2025 a Gasar Muhawara ta Duniya ta Teen Eagle.

Rukayya ta yi zarra ne a wannan babbar gasa da ta gudana a birnin Landan na ƙasar Birtaniya, inda zaƙaƙuran ɗalibai daga ƙasashe 69 a faɗin duniya suka fafata a tsakaninsu.

Jami’in Sadarwar Zamani na Gwamnatin Jihar Yobe, Yusuf Ali, ya bayyana cewa Rukayya ta samu kafa wannan tarihi ne a dalilin zurfin tunani da kuma kaifin basirarta da kuma fahimtar al’amuran duniya, duk kuwa da ƙarancin shekarunta.

Ɗalibar daga Kwalejin Nigerian Tulip International (NTIC), Rukayya, ta ɗauki hankalin alƙalan gasar da sauran jama’a saboda ƙarfin hujjojinta da ta gabatar da kuma iya bayani mai ganawarsa cikin natsuwa, lamarin da ya ba ta damar doke duk abokan karawarta.

Nafisa ta cancaci kyautar Dala 100,000 da gida da OON —Pantami NAJERIYA A YAU: Yadda Ayyuka Suka Ragu A Jihohi Bayan Kudin Shiga Ya Karu

Ita ce mutum ya biyu daga Jihar Yobe kuma daga makaranta tare da Nafisa Abdullah Aminu wadda ta zama gwarzuwa a ɓangaren Harshen Turanci a yayin gasar, inda suka wakilci Najeriya, ƙasa mai yawan al’umma sama da miliyan 200.

Nasararta nuna irin basirar da Allah Ya yi wa matasan Najeriya inda suke yin zarra a sassan duniya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ummar Zamfara: ’Yan bindiga sun karɓi N56m domin izinin yin noma
  • NAJERIYA A YAU: Mummunan Tasirin Rashin Bambance Zazzabin Lassa Kan Lafiyar Al’umma
  • Tinubu ya taya ’yan matan Yobe da suka lashe gasa a Ingila murna
  • ‘Za a yi ambaliyar kwana 5 a jihohi 19 na Najeriya’
  • Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu
  • Sashen Lafiya Zai Fara Amfani Da Sabuwar Fasahar AI Don Inganta Lafiya
  • FG Za Ta Raba Naira miliyan 3.4m Ga Wadanda Suke Amfana Da Shirin ACReSAL
  • Gwamnatin Tarayya Ta Karrama ‘Yan Wasan Kwallon Kwando Na Mata
  • Ɗaliba ’yar shekara 15 daga Yobe ta lashe Gasar Muhawara ta Duniya
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Ayyuka Suka Ragu A Jihohi Bayan Kudin Shiga Ya Karu