HOTUNA: An ƙaddamar da tashin sahun farko na maniyyatan Nijeriya zuwa Saudiyya
Published: 9th, May 2025 GMT
An ƙaddamar da tashin sahun farko na maniyyatan Nijeriya zuwa ƙasar Saudiyya domin gudanar da Aikin Hajjin 2025.
Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima ne ya ƙaddamar da tashin maniyattan a filin jirgin Sam Mbakwe da ke birnin Owerri na Jihar Imo.
’Yan kungiyar asiri sun kashe masu shirin tafiya NYSC a Bayelsa JAMB ta saki sakamakon jarrabawar 2025Sahun farko na maniyyata 315 waɗanda suka kama hanyar ƙasa mai tsarki sun fito ne daga jihohin Imo da Abia da Bayelsa inda jirgin Air Peace ne ya kwashe su.
Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma da Shugaban Hukumar Alhazan Nijeriya, Farfesa Abdullahi Usman da Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammadu Sa’adu Abubakar III da sauran manyan jami’an gwamnatin Nijeriya ne suka tarbi Kashim Shettima domin ƙaddamar da tashin maniyyatan.
Aƙalla mutum 43,000 ne waɗanda suka yi rajistar gudanar da aikin hajji daga jihohi 36 da birnin tarayyar ƙasar za su tafi ƙasa mai tsarki domin sauke farali.
Hukumar alhazan ta ce jirgin Air Peace zai kwashi maniyyata 5,128 daga Jihohin Abia da Akwa Ibom da Anambra da Bayelsa da Benue da Cross River da Delta da Ebonyi da Edo da Ondo da Ribas da Taraba.
Sai kuma jirgin FlyNas zai ɗauki maniyyata 12,506 daga Abuja babban birnin Nijeriya da Kebbi da Legas da Ogun da Osun da Sokoto da Zamfara.
Sannan kuma jirgin Max Air zai ɗauki fasinjoji 15,2043 daga Jihohin Gombe da Jigawa da Kano da Katsina da Kwara da Oyo da Filato.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Imo maniyyata Sarkin Musulmi ƙaddamar da tashin
এছাড়াও পড়ুন:
Za mu ci gaba da yi wa Isra’ila luguden wuta — Shugaban Iran
Shugaban Ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya bayyana cewa ƙasarsa za ta ci gaba da mayar da martani kan hare-haren da Isra’ila ke kai mata.
Ya bayyana haka ne a lokacin da yake magana da shugaban Faransa, Emmanuel Macron, ta wayar tarho.
Uba Sani ya yi jajen ’yan ɗaurin aure 12 da aka kashe a Filato Ɗan ƙunar baƙin wake ya kashe mutum 10 da bam a BornoShugaba Pezeshkian ya ce Iran tana da niyyar yin haɗin gwiwa da sauran ƙasashe don amfani da makamashin nukiliya ta hanyar da ba ta da alaƙa da yaƙi, amma hakan ba yana nufin za su dakatar da inganta shirye-shiryensu na nukiliya gaba ɗaya ba.
Ya ƙara da cewa hare-haren da Isra’ila ke kai wa ƙasarsa ba za su wuce haka nan ba, domin kuwa Iran za ta riƙa mayar da martani mai zafi.
A ranar Asabar, rundunar sojin Iran ta yi gargaɗi cewa za ta kai wa Isra’ila ta hark ta jiragen ruwa.
A cewar wani kakakin rundunar sojin Iran da ya bayyana a wani bidiyo, duk ƙasar da ta tura makamai zuwa Isra’ila, kamar ta shiga yaƙi da Iran ce kai-tsaye, kuma Iran ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen kare kanta ba.
A ranar Juma’ar da ta gabata, Iran ta harba makamai masu linzami da jiragen yaƙi marasa matuƙa zuwa Isra’ila, lamarin da ya jikkata mutane aƙalla 19 a birnin Haifa da ke Arewacin Isra’ila, kamar yadda wani asibiti a yankin ya tabbatar.