An ƙaddamar da tashin sahun farko na maniyyatan Nijeriya zuwa ƙasar Saudiyya domin gudanar da Aikin Hajjin 2025.

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima ne ya ƙaddamar da tashin maniyattan a filin jirgin Sam Mbakwe da ke birnin Owerri na Jihar Imo.

’Yan kungiyar asiri sun kashe masu shirin tafiya NYSC a Bayelsa JAMB ta saki sakamakon jarrabawar 2025

Sahun farko na maniyyata 315 waɗanda suka kama hanyar ƙasa mai tsarki sun fito ne daga jihohin Imo da Abia da Bayelsa inda jirgin Air Peace ne ya kwashe su.

Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma da Shugaban Hukumar Alhazan Nijeriya, Farfesa Abdullahi Usman da Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammadu Sa’adu Abubakar III da sauran manyan jami’an gwamnatin Nijeriya ne suka tarbi Kashim Shettima domin ƙaddamar da tashin maniyyatan.

Aƙalla mutum 43,000 ne waɗanda suka yi rajistar gudanar da aikin hajji daga jihohi 36 da birnin tarayyar ƙasar za su tafi ƙasa mai tsarki domin sauke farali.

Hukumar alhazan ta ce jirgin Air Peace zai kwashi maniyyata 5,128 daga Jihohin Abia da Akwa Ibom da Anambra da Bayelsa da Benue da Cross River da Delta da Ebonyi da Edo da Ondo da Ribas da Taraba.

Sai kuma jirgin FlyNas zai ɗauki maniyyata 12,506 daga Abuja babban birnin Nijeriya da Kebbi da Legas da Ogun da Osun da Sokoto da Zamfara.

Sannan kuma jirgin Max Air zai ɗauki fasinjoji 15,2043 daga Jihohin Gombe da Jigawa da Kano da Katsina da Kwara da Oyo da Filato.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Imo maniyyata Sarkin Musulmi ƙaddamar da tashin

এছাড়াও পড়ুন:

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

Mazauna kauyuka akalla 30 daga Dan-Isa da Kagara dake karamar hukumar Kaura-Namoda a jihar Zamfara, sun mamaye gidan gwamnati dake Gusau babban birnin jihar domin nuna takaicinsu kan yadda rashin tsaro a yankin na su “yaki ci yaki cinyewa” a ranar Alhamis. Masu zanga-zangar da suka hada da mata da kananan yara suna dauke da alluna dauke da rubuce-rubuce kamar: “Muna bukatar zaman lafiya a kauyukan Kaura-Namoda,” “Gwamna Dauda Lawal da Matawalle ku kawo mana dauki”, “Ana kashe mu kowace rana,” da dai sauransu. Tsoffin Kansilolin APC Sun Yi Zanga-zangar Nesanta Kansu Da Maganganun Abdullahi Abbas  Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Jihohin Makwabta, Ya Kara Ta’azzarar Rashin Tsaro A Neja – Bago Da yake jawabi a gidan gwamnati, jagoran masu zanga-zangar, Lawal Kamilu daga Dan-Isa, ya ce sun gudanar da zanga-zangar ne don nuna takaicinsu kan yadda ’yan bindiga ke addabar kauyukansu tare da kashe mutanensu a koda yaushe. “Dukkanmu mun fito ne daga kauyuka kusan 30 don nuna rashin amincewa da rashin tsaro saboda yawancin mutanenmu ko dai an kashe su ko kuma ‘yan bindiga sun yi garkuwa da su. “Suna bukatar a biya su kudin fansa da ya kai miliyoyin Naira, alhalin ba mu da komai, babu abin da za mu bayar a matsayin kudin fansa, domin duk mun sayar da kadarorinmu da gonakanmu domin biyan kudin fansar ‘ya’yanmu da ‘yan uwanmu da aka yi garkuwa da su a baya,” in ji Kamilu. Masu zanga-zangar sun yi kira ga Ministan Tsaro, Bello Matawalle, da gwamnatin tarayya karkashin jagorancin shugaban kasa Bola Tinubu da su kawo musu dauki, suna masu cewa “Yanzu Zamfara na hannun Ubangiji mai rahama, Madaukakin Sarki”.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno
  • Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro 
  • Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara
  • Tsoffin Kansilolin APC Sun Yi Zanga-zangar Nesanta Kansu Da Maganganun Abdullahi Abbas 
  • Kasar Sin Ta Kammala Gwajin Farko Na Sauka Da Tashin Kumbon Binciken Duniyar Wata Mai Dauke Da Bil Adama
  • Nijeriya Da Indiya Za Su Haɗa Kai Wajen Yaƙi Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi
  • Yadda kwacen babur da waya ya maye gurbin garkuwa da mutane a Birnin Gwari
  • Manoma sun koka kan rabon takin gwamnati a Sakkwato
  • Jihar Zamfara: ‘Yan Sanda 390 Sun Sami Karin Girma
  • Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82