An ƙaddamar da tashin sahun farko na maniyyatan Nijeriya zuwa ƙasar Saudiyya domin gudanar da Aikin Hajjin 2025.

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima ne ya ƙaddamar da tashin maniyattan a filin jirgin Sam Mbakwe da ke birnin Owerri na Jihar Imo.

’Yan kungiyar asiri sun kashe masu shirin tafiya NYSC a Bayelsa JAMB ta saki sakamakon jarrabawar 2025

Sahun farko na maniyyata 315 waɗanda suka kama hanyar ƙasa mai tsarki sun fito ne daga jihohin Imo da Abia da Bayelsa inda jirgin Air Peace ne ya kwashe su.

Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma da Shugaban Hukumar Alhazan Nijeriya, Farfesa Abdullahi Usman da Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammadu Sa’adu Abubakar III da sauran manyan jami’an gwamnatin Nijeriya ne suka tarbi Kashim Shettima domin ƙaddamar da tashin maniyyatan.

Aƙalla mutum 43,000 ne waɗanda suka yi rajistar gudanar da aikin hajji daga jihohi 36 da birnin tarayyar ƙasar za su tafi ƙasa mai tsarki domin sauke farali.

Hukumar alhazan ta ce jirgin Air Peace zai kwashi maniyyata 5,128 daga Jihohin Abia da Akwa Ibom da Anambra da Bayelsa da Benue da Cross River da Delta da Ebonyi da Edo da Ondo da Ribas da Taraba.

Sai kuma jirgin FlyNas zai ɗauki maniyyata 12,506 daga Abuja babban birnin Nijeriya da Kebbi da Legas da Ogun da Osun da Sokoto da Zamfara.

Sannan kuma jirgin Max Air zai ɗauki fasinjoji 15,2043 daga Jihohin Gombe da Jigawa da Kano da Katsina da Kwara da Oyo da Filato.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Imo maniyyata Sarkin Musulmi ƙaddamar da tashin

এছাড়াও পড়ুন:

Za a gudanar da wasannin ƙwallon yashi a Abuja

Hukumar shirya gasar ƙwallon yashi ta ƙasa ta tabbatar da cewa za a gudanar da wasannin ƙarshe na bana a filin wasa na Jabi Lake Park, da ke babban birnin tarayya Abuja.

Kodinetan hukumar a Najeriya, kuma shugaban hukumar a nahiyar Afirka, Mahmud Hadejia, ne ya tabbatar da hakan a lokacin da yake zantawa da Trust Radio a cikin shirin “Bakin Raga” da safiyar yau Laraba.

An amince da hukuncin yi wa malamai ɗaurin shekara 14 kan lalata da ɗalibai Yara biyu sun mutu bayan faɗawa rijiya a Kano

Shugaban ya bayyana cewa wannan ce gasa ta biyar da za a buga, kuma ta farko da za a fafata a Abuja.

A cewarsa, za a fara buga wasannin ƙarshe daga gobe Alhamis, 6 ga watan Nuwamba, sannan a kammala a ranar Lahadi, 9 ga watan Nuwamba, 2025.

Wannan dai gasa ce da kungiyoyin da suka fi fice a zagayen farko za su fafata a cikinta, wanda ya haɗa da jihoyin Akwa Ibom, Jigawa, Kebbi, Kaduna da wasu sauran jihohi.

Haka kuma, manyan baki da ake sa ran halartar bikin buɗe gasar a ranar Laraba, 5 ga watan Nuwamba, sun haɗa da Ahmed Musa, Ibrahim Musa Gusau, Seyi Tinubu, da sauran fitattun ‘yan wasa da jami’ai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Jirgin Kasan Dakon Kaya Na Farko Daga Rasha Ya Iso Kasar Iran A Yau Asabar
  • An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa
  • Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma
  • Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya
  • Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta
  • Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya
  • Sojin Amurka sun gabatar da shirin ƙaddamar da hari a Najeriya
  • Gharibabadi: Kyakkyawar Alaka Tsakanin Iran Da Saudiyya Na Da Babban Tasiri Ga Yankin Da Ma Duniya
  • Za a gudanar da wasannin ƙwallon yashi a Abuja
  • Jirgin ƙasa ya murƙushe babur mai ƙafa uku a Jos