Leadership News Hausa:
2025-05-12@19:28:10 GMT

NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

Published: 12th, May 2025 GMT

NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

Ɗan majalisar jihar Kano mai wakiltar mazabar Sumaila, Hon. Zubairu Hamza Masu, ya bar jam’iyyar NNPP ya koma APC.

A cikin wasiƙar murabus da ya aika wa shugaban majalisar, Hon. Ismail Falgore, Masu ya bayyana cewa rikice-rikice da shari’o’in cikin NNPP a matsayin dalilin ficewarsa.

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar 2027: PDP Ta Mutu, APC Na Shirin Sake Yin Nasara – Martanin Ganduje Ga Lamido 

Shugaban majalisar ya karanta wasiƙar a zaman majalisa na ranar Litinin, inda ya bayyana cewa Masu ya fice daga NNPP tun daga ranar 12 ga Mayu, 2025, kuma ya samu amincewa ga shugabannin APC a dukkan matakan da suka dace su karɓe shi.

Ɗan majalisar ya kuma bayyana cewa wasu mutane daban-daban a matakin jiha da na ƙasa suna da’awar shugabancin NNPP, ciki har da Dr. Suleiman Hashim Dungurawa da Sanata Mas’ud El-Jibrin Doguwa a matakin jiha, yayin da Dr. Ahmed Ajuji da Dr. Agbo Major ke da’awar shugabancinta na ƙasa, tare da shari’o’in kotu da ke dagula jam’iyyar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar Kurdawan Turkiya Za Ta Ajiye Makamanta Na Yaki

 Kungiyar Kurdawan Turkiya PKK ta sanar da cewa za ta ajiye makamanta ta kuma rusa kanta.

Kamfanin dillancin labarum “Furat” mai kusanci da kungiyar ta PKK, ya nakalto cewa; Kungiyar ta yanke zartar da wannan matakin ne a yayin taron da ta yi kaso na 12 da ta yi kwanaki kadan da su ka gabata.

Sanarwar ta PKK ta kuma kunshi cewa;Jam’iyyun siyasa na kurdawa za su yi aiki da nauyin da ya rataya a wuyansa domin bunkasa tsarin demokradiyya da sake gina al’ummar Kurdawa.”

Haka nan kuma PKK ta ce, da akwai alakar a sake Shata salon alakar Kurdawa da Turkiya.

A martanin da jam’iyyar dake Mulki a Turkiya ta fitar, ta bayyana cewa;  Zartar da  matakin da kungiyar ta Kurdawa ta dauka na ajiye makamanta da kuma rusa kanta, da dukkanin rassanta, zai zama bude wani sabon shafi.

Kakakin jam’iyyar, Umar Jalik ya ce; Matakanin yana da matukar muhimmanci ga Turkiya, domin hakan yana nufin kawo karshen ta’addanci,kuma gwamnati za ta sa ido ta ga aiwatar da wannan matakin, kuma za a rika sanar da shugaba Rajab Tayyib Urdugan akan zartar da matakan.

Kungiyar dai ta PKK ta yi taronta ne a arewacin Iraki a ranakun 5 da 7 ga watan Mayu, bisa gayyatar jagoranta Abdullahi Ojlan da yake tsare tsawon shekaru 26 da su ka gabata.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kungiyar Kurdawan Turkiya Za Ta Ajiye Makamanta Na Yaki
  • An kama ɗan daba mai yin fashi a cikin shigar mata a Kano
  • ’Yan ta’adda sun ƙwace makaman sojoji na tiriliyoyin naira —Majalisa
  • 2027: PDP Ta Mutu, APC Na Shirin Sake Yin Nasara – Martanin Ganduje Ga Lamido 
  • Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar
  • Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow
  • Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP
  • Majalisar Da Take Kula Da Nukiliyar Pakistan Za Su Yi Taron Gaggawa
  • Rikicin Filato Ya Sa Makiyaya Yin Asarar Naira Miliyan 300 Cikin Wata 2