Yadda ISWAP ta kashe sojoji ta kwashe makamai a sansanin soji a Borno
Published: 13th, May 2025 GMT
Mayaƙan Boko Haram sun kashe sojoji da ba a san adadinsu ba tare da yin awon gaba da wasu da dama bayan wani ƙazamin hari da suka kai a sansanin soji da ke yankin Marte a Jihar Borno.
Majiyoyin soji sun ce mayaƙan ƙungiyar sun fi karfin sojojin, inda suka kwashi makamai masu tarin yawa sa’annan suka cinna wa ma’ajiyar makamai da ke sansanin sojin wuta.
Mazauna yankin sun bayyana cewa da misalin ƙarfe 3 na asuba, kafin wayewar garin ranar Asabar ne Boko Haram ta ƙaddamar da harin.
Wani soja da ya nemi a ɓoye sunansa ya ce, “ISWAP ta ƙwace Marte, an kashe sojoji da dama, an kama wasu, amma wasu sun samu sun tsere zuwa Dikwa, inda runduna ta 24 take.
Ya kashe abokinsa saboda hula a Kano NAJERIYA A YAU: Matsalar lantarki: ’Yan Najeriya sun yi tir da biyan diyya ga ’yan Band A“’Yan ta’addan sun ƙona tankokin yaƙi kuma sun kwashi makamai daga sansanin sojin,” in ji shi.
Wani mazaunin Marte, gari mai nisan kilomita 38 daga Dikwa, hedikwatar Ƙaramar Hukumar Dikwa, ya ce sun ji karar harbe-harben kuma daga bisani suka ga jirgin soji yana shawagi.
Ya ce, “mun samu labarin cewa an tura ƙarin jami’an tsaro kuma an ƙwato sansanin sojin, amma ’yan ta’addan sun sun sace makamai kuma sun koma motoci da rumbun makaman sojin da ke wurin.”
Ya ci gaba da cewa, “abin takaici mayaƙan sun tsare mata da ƙananan yara da dama a Sabon Marte, amma wasu da dama sun samu tserewa zuwa Dikwa domin tseratar da rayuwarsu.
“Ba a daɗe ba da ’yan ƙungiyar suka kai hari a Malam Fatori, inda suka kashe sojoji 21 da wani daga cikin kwamdojinmu.”
Daga watan Janairu zuwa yanzu an kai wa sansanonin soji da dama hare-hare a yankin Tafkin Chadi da kuma Dutsen Mandara da ke Dajin Sambisa a jihohin Borno da Yobe.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram ISWAP Marte tankokin yaƙi
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yan Nijeriya Miliyan 14 Sun Yi Bikin Murnar Karɓar Kyautar N23m Daga Bankin STANBIC IBTC
Hakan ya gudana a ƙarƙashin jagorancin hukumomin da ke lura da yadda ake tafiyar da gasar da kuma kare haƙƙin masu amfani da kaya (FCCPC), hukumar kula da tallace-tallace ta Nijeriya (ARCON), da hukumar kula da harkokin caca da wasanni ta Jihar Legas (LSLGA).
Zaɓen ya kasance cikin gaskiya da adalci, inda waɗanda yi nasara suka bar Naira 10,000 a cikin asusun ajiyarsu na Stanbic IBTC ko @ease Wallet har tsawon kwanaki 30.
Daga mata ‘yan kasuwa, zuwa ɗalibai, har zuwa ma’aikatan da suka yi ritaya, waɗanda suka yi nasara yanzu suna iya biyan kuɗin makaranta, fara ƙananan sana’o’i, ko kuma tafiyar da buƙatun gidajensu cikin sauƙi.
An ƙara sanya wasu mutane takwas cikin farin ciki a zaɓen babbar garaɓasar wata huɗu ta farkon shekara wanda aka yi a ranar 7 ga wata.
Mutane bakwai daga kowace shiyya sun samu Naira miliyan ɗaya kowannensu, yayin da babbar kyauta ta wata huɗu ta kai Naira miliyan biyu aka bai wa mutum ɗaya.
Jimillar kyautar ta kai Naira miliyan tara. Hanyoyin da aka bi wajen zaɓar waɗanda suka yi nasara sun nuna irin yadda Bankin Stanbic IBTC ke bai wa kowane mai ajiya muhimmanci.
Zaɓen waɗanda suka yi nasara saboda ajiyar kuɗi a watan Mayun 2025, bankin ya raba Naira miliyan 30 ga mutane 218 a karo na huɗu, yayin da aka raba wa mutane sama da 2,000 Naira miliyan 300 masu asusun ajiya tun fara shirin a shekarar 2021.
Bankin Stanbic IBTC ya kasance ginshiƙi wajen tallafanwa rayuwar ‘yan Nijeriya.
Emmanuel Aihevba, Shugaban Bankin Stanbic IBTC a Nijeriya, ya ce: “Bikin zaɓar waɗanda suka cancanta, ba su kyauta, da yadda aka gudanar da shi a cikin wata biyu, har ma na farkon wata huɗu na bana, ya nuna yadda muke farin ciki da abokan hulɗarmu da suka mayar da hankali kan ajiya. Mun saka wa masu hulɗa da mu 148 zunzurutun kuɗi har Naira miliyan 23 saboda amincewarsu da tafiya tare da mu. Muna son su yi amfani da wannan kuɗi don bunƙasa harkar ilimi ko sana’a.
“A Bankin Stanbic IBTC, muna nuna cewa ya dace mu samar wa abokan hulɗarmu damar bunƙasa rayuwarsu da kuma koya musu yadda za su saba da al’adar ajiyar kuɗi a faɗin Nijeriya.”
Kesena Igben, wani mutum da ya yi ritaya kuma ɗaya daga cikin waɗanda suka yi nasara a gasar, ya bayyana farin cikinsa.
“Na zo tare da ‘yata domin karɓar kyauta. A hanya ta ce, ‘Baba, na ga kana farin ciki.’ Sai na ce mata, ‘Kin san wannan kuɗi zai taimaka min wajen sayen man fetur na mako biyu?’ A gare ni, wannan kyauta ta Bankin Stanbic IBTC babbar alfarma ce, saboda ta rage min damuwar neman kuɗin fetur na mako biyu.”
Yadda Stanbic IBTC ke nuna damuwarsa kan farin cikin abokan hulɗarsa ya nuna yadda suka saka gaskiya da adalci a harkokinsu.
Hukumar Kare Haƙƙin Masu Amfani da Kaya ta bai wa bankin kyautar ARCON a shekarun 2023 da 2024.
Don haka kai ma shiga cikin jerin waɗanda za su kasance cikin farin ciki!
Ajiye Naira 10,000 kacal ko sama da haka har tsawon kwanaki 30 ko a asusun ajiyarka na Stanbic IBTC ko @ease Wallet domin samun damar shiga sahun waɗanda za su lashe kyautar.
Latsa wannan domin samun damar shiga https://smebanking.stanbicibtc.com/AccountOpening/tier-one ko ka ziyarci kowanne reshen bankin, ka fara daga yau!
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp