Aminiya:
2025-08-11@21:03:56 GMT

Matashi ya kashe saurayin ƙanwarsa a Kano

Published: 13th, May 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan Kano ta sanar da kama wani matashi bisa zargin kashe saurayin ƙanwarsa da ya wanke ƙafa ya tafi zance gidansu.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ’yan sandan Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Mahaifin tsohon Gwamnan Kaduna ya rasu Kwalara ta yi ajalin mutum 4 a Filato

Kiyawa ya bayyana cewa matashin ya fito da gora kuma ya buga wa saurayin da ya je zance gidansu a ƙauyen Kunya da ke Ƙaramar Hukumar Minjibir a Kano.

Sanarwar ’yan sandan ta ce matashin wanda ɗan asalin ƙauyen Goda, ya je Kunya ne wajen budurwarsa domin zance.

Sai dai jim kaɗan bayan zuwan nasa sai aka yi zargin cewa yayan budurwar mai suna Mansur Umar mai shekara 25 ya doke shi da sanda a ka, lamarin da ya haddasa masa munanan raunuka.

“An garzaya da shi asibitin Kunya daga baya kuma aka mayar da shi Asibitin Murtala domin ba shi kulawar gaggawa, amma daga baya aka tabbatar da mutuwarsa,” a cewar Kiyawa.

’Yan sanda sun ce tuni suka kama Mansur, domin gudanar da bincike a sashen binciken manyan laifuka na rundunar ’yan sandan jihar.

Rundunar ’yan sandan ta yi kira ga jama’a su riƙa sanya haƙuri a cikin al’amuransu, tare da kai rahoton duk wata jayayya da aka samu tsakanin wasu mutane zuwa ofishin ’yan sanda mafi kusa.

Cikin wani sautin murya da Kiyawan ya sake wallafawa, matashin ya bayyana nadamarsa tare da neman afuwar duk makusantan mamacin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Jihar Kano Ƙanwa Saurayi

এছাড়াও পড়ুন:

U Reporters Sun Gudanar Da Taron Wayar Da Kan Jama’a Game Da Shayarwa A Kano

A ci gaba da gudanar da bukukuwan makon shayarwa da nonon uwa na duniya, asusun kula da kananan yara na majalisar dinkin duniya UNICEF ya shirya tarurruka a Kano tare da hadin gwiwar U-Reporters da sauran kungiyoyin matasa domin wayar da kan al’umma kan amfanin shayarwa.

 

An gudanar da gangamin a lokaci guda a wurare daban-daban a fadin jihar, wadanda suka hada da Dangi Roundabout, KSIP Roundabout dake kan titin Ahmadu Bello, Central Road, Triumph Roundabout, Legas Street, Hotoro Roundabout dake Gabashin Bypass, Gidan Gwamnati dake kan titin Jiha, da Kasuwar Abubakar Rimi.

 

Sauran wuraren sun hada da Kofar Gadon Kaya, Kofar Nasarawa, Gadar Lado dake kan titin Zaria, da Unguwar Kasuwar Yankaba dake kan titin Hadejia.

 

Da yake jawabi a wajen gangamin zagayen, shugaban kungiyar Malik Muhammad Abdullahi ya bayyana cewa shirin na da nufin inganta muhimmancin shayar da jarirai nonon uwa.

 

Ya yi nuni da cewa, shayar da jarirai nonon uwa zalla na watanni shida na farkon rayuwar yaro na iya hana cututtuka masu kashe yara da sauran matsalolin lafiya.

 

Wata wakilin U-Report, Yahanasu Adam, ta yi kira da a kara tallafawa mata masu shayarwa, inda ta jaddada bukatar samar da daidaiton abinci da tsafta don kiyaye lafiya da walwalar iyaye mata da ’ya’yansu.

 

A yayin da take zantawa da manema labarai na U a yayin gangamin, wata uwa mai ‘ya’ya uku, Maryam Shehu, ta bayyana yadda ta samu, inda ta ce shayar da ‘ya’yanta ba wai nonon uwa ba ya sa ‘ya’yanta su fara rayuwa cikin koshin lafiya.

 

Ta tuna yadda aka ba ta kwarin gwiwar gudanar da shayar da jarirai nonon uwa zalla yayin kula da mata masu juna biyu a cibiyar kula da lafiya a matakin farko na Sheka.

 

Hakazalika, wata uwa mai suna Yahanasu Danladi, ta ce shayar da ’yar tata ya taimaka wajen shawo kan cutar gudawa da sauran matsalolin lafiya da ke da nasaba da rashin tsaftataccen ruwa.

 

Cov/Khadija Aliyu

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za a gyara tarbiyar tubabbun ’yan daban Kano
  • UNICEF Da Gavi Sun Bada Na’urorin Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Ga Jihar Kano
  • Majalisar Dokokin Kano Ta Karɓi Ƙarin Kasafin Kuɗi Na 2025
  • U Reporters Sun Gudanar Da Taron Wayar Da Kan Jama’a Game Da Shayarwa A Kano
  • ‘Yan Sandan Nasarawa Sun Kama Mutum Shida Da Laifin Fashi Da Makami Da Garkuwa Da Mutane
  • Runduunar ‘Yan Sandan Jihar kwara Ta Karfafa Tsaro A Banbila
  • Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK
  • Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam
  • Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi
  • An Rantsar Da Sabbin Mataimaka Na Musamman A Karamar Hukumar Auyo