Aminiya:
2025-10-13@20:19:09 GMT

Matashi ya kashe saurayin ƙanwarsa a Kano

Published: 13th, May 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan Kano ta sanar da kama wani matashi bisa zargin kashe saurayin ƙanwarsa da ya wanke ƙafa ya tafi zance gidansu.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ’yan sandan Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Mahaifin tsohon Gwamnan Kaduna ya rasu Kwalara ta yi ajalin mutum 4 a Filato

Kiyawa ya bayyana cewa matashin ya fito da gora kuma ya buga wa saurayin da ya je zance gidansu a ƙauyen Kunya da ke Ƙaramar Hukumar Minjibir a Kano.

Sanarwar ’yan sandan ta ce matashin wanda ɗan asalin ƙauyen Goda, ya je Kunya ne wajen budurwarsa domin zance.

Sai dai jim kaɗan bayan zuwan nasa sai aka yi zargin cewa yayan budurwar mai suna Mansur Umar mai shekara 25 ya doke shi da sanda a ka, lamarin da ya haddasa masa munanan raunuka.

“An garzaya da shi asibitin Kunya daga baya kuma aka mayar da shi Asibitin Murtala domin ba shi kulawar gaggawa, amma daga baya aka tabbatar da mutuwarsa,” a cewar Kiyawa.

’Yan sanda sun ce tuni suka kama Mansur, domin gudanar da bincike a sashen binciken manyan laifuka na rundunar ’yan sandan jihar.

Rundunar ’yan sandan ta yi kira ga jama’a su riƙa sanya haƙuri a cikin al’amuransu, tare da kai rahoton duk wata jayayya da aka samu tsakanin wasu mutane zuwa ofishin ’yan sanda mafi kusa.

Cikin wani sautin murya da Kiyawan ya sake wallafawa, matashin ya bayyana nadamarsa tare da neman afuwar duk makusantan mamacin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Jihar Kano Ƙanwa Saurayi

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 

Gwamna Uba Sani ya jaddada cewa wannan titin ba na yankin Arewa kadai ba ne, ya bayyana shi a matsayin jijiyar ƙasa da ƙasa ne wadda ke haɗa yankuna daban-daban tare da ƙarfafa haɗin kai da bunƙasar tattalin arziki.

 

Ya kara da cewa titin Abuja- Kaduna da Kano na ɗaya daga cikin manyan ayyukan gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu a ƙarƙashin Manufar Sabon Fata na (Renewed Hope Agenda), wadda ke nufin sabunta manyan gine-ginen ƙasa da inganta tattalin arziki.

 

Yace “Wannan titi ba hanya ce kawai ba inda yace wata hanya ce ta tattalin arziki wadda ke haɗa mutane, kasuwanni, da dama a fadin Arewacin Nijeriya da ma bayan haka,”

 

A nasa jawabin, Sanata Umahi ya yaba wa Gwamna Uba Sani bisa yadda yake kaiwa da komowa domin kare muradun al’ummar Kaduna, tare da tabbatar da cewa gwamnatin tarayya ta kuduri aniyar kammala aikin cikin lokaci. Ya bayyana cewa an umarci kamfanonin da ke aikin da su rika aiki sau biyu a rana domin hanzarta cigaba ba tare da rage inganci ba.

 

Ministan ya kara da cewa amfani da fasahar siminti mai ɗorewa wanda zai tabbatar da cewa titin zai dawwama tare da rage kudin gyara nan gaba.

 

Kamfanonin da ke aikin sun yi alkawarin ƙara gaggautawa musamman a yankin Jere dake jihar Kaduna, inda ake sa ido sosai kan ci gaban aiki. Gwamnatin Jihar Kaduna ta kuma tabbatar da ci gaba da haɗin kai da Ma’aikatar Ayyuka ta Tarayya domin magance ƙalubalen da ke iya janyo tsaiko.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari October 11, 2025 Manyan Labarai Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP October 11, 2025 Manyan Labarai Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano October 10, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Kungiyar ‘Yan Dako Ta Kasa Ta Nada Sabon Sakatare A Jigawa
  • Soja ya kashe matarsa, ya hallaka kansa a Jihar Neja
  • Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22
  • Egbetokun ya sauke kwamishinan ’yan sandan Abuja
  • Gwamna Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Cuba Ta Bayyana Bada Kyautar Noble Ga Dan Kasar Veunzuelas machado A Matsayin Abin Kunya.
  • Gwamna Uba Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba
  • Mutane 2 sun rasu a rikicin manoma da makiyaya a Kebbi