Miliyoyin mutane, mafi yawansu mabiya mazhabar iyalan gidan manzon All..(s) sun taru a hubbaren limami na 8 daga limamai masu tsarki wasiyan manzon All..(s)..12.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa, miliyoyin mutanen kasar Iran da kuma wasu bakin da suka zo daga kasashen waje sun yi cincirindo a hubbaren Imam Aliyu dan Musa Al-rida(a) limamai na 8 daga cikin limamai masu tsarki daga iyalan gidan manzon Alll.

.(s) da ke birnin Mashad na arewa maso gabacin kasar Iran don tunawa da ranar haihuwarsa.

An kawata hubbaren na sa da fulawowi wasu na lantarki sannan malamai suna bayyana matsayinsa a wajen raya addinin kakakinsa manzon All..(s), musamman a lokacinda sarki Mamun daga cikin sarakunan Abbasiyawa ya tilasta masa kaura daga madina zuwa Maru cibiyar mulkinsa. Da kuma yadda ya bayyana dimbin ilmin da All..ya basu sannan ya bayyana addinin musulunci na gaskiya wanda manzon All..(s) ya zo da shi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Talauci da tsangwama na hana yara mata karatu a Gombe — Kwamishina

Kwamishiniyar Ilimi ta Jihar Gombe, Dokta Aishatu Umar Maigari, ta ce talauci da nuna bambanci na daga cikin manyan dalilan da ke hana yara mata damar samun ilimi a jihar.

Ta bayyana hakan ne a wajen bikin Ranar Yara Mata ’Yan Makaranta ta Duniya ta shekarar 2025, wanda Shirin AGILE tare da Access Initiative Africa da Nudge Initiative suka shirya a Gombe.

Gwamnan Kebbi ya bai wa sojoji kyautar motoci 6 da babura 30 don inganta tsaro ’Yan ta’adda sun kashe sojoji 4 a wani sabon hari a Borno

A wajen bikin, Uwargidan Gwamnan Jihar Gombe, Asma’u Inuwa Yahaya, ta yaba da yadda gwamnatin jihar ke ƙoƙarin tabbatar da cewa ba a bar wata yarinya a baya wajen samun ilimi.

Ta ce Gwamnan jihar, ya bai wa ilimin yara mata muhimmanci, wanda hakan ya sa ake samu ƙaruwa yara mata da ke zuwa makaranta.

Kwamishiniyar, ta ƙara da cewa ma’aikatar ilimi tana aiki wajen samar da sabbin manufofi da tsare-tsare da za su taimaka wajen rage waɗannan matsaloli da tabbatar da damar ilimi ga kowa cikin adalci.

A nata jawabin, Kodinetan Shirin AGILE, Dokta Amina Haruna Abdul, ta ce bikin na bana an shirya shi ne don ƙarfafa gwiwar yara mata wajen ci gaba da neman ilimi duk da ƙalubalen da suke fuskanta.

Ta gode wa Uwargidan Gwamnan da ma’aikatar ilimi bisa goyon bayansu.

Haka kuma, Akawun Majalisar Dokokin Jihar Gombe, Barista Rukayyatu Jalo, ta shawarci yara mata da su dage wajen yin karatu, inda ta bayyana cewa ilimi ne hanyar da za ta gina rayuwarsa.

Wasu daga cikin ɗaliban da suka halarci bikin, sun bayyana farin ciki da godiya kan shirya taron saboda yadda ya ƙara musu ƙwarin gwiwa.

Ɗalibai da dama sun gudanar da muhawara da wasan kwaikwayo a wajen taron.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kungiyar Hamas Ta Mika Yahudawa 7 Daga Cikin 20 Da ke Hannunta  Ga Kungiyar Red Cross
  • Tsokaci A Kan Mata Masu Tsananin Kishi
  • Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa
  • ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna
  • Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?
  • Tarihin Hassan Usman Katsina (1)
  • Talauci da tsangwama na hana yara mata karatu a Gombe — Kwamishina
  • Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
  • Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa
  • Li Qiang Ya Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Koriya Ta Arewa