Majalisar dokokin jihar Nasarawa ta amince da dokar kafa doka da za ta samar da tsari da kula da bada izinin filaye da yarjejeniyoyin al’umma ga masu hakar ma’adanai da sauran batutuwan da suka shafi hakan.

 

Shugaban Majalisar Dokta Danladi Jatau, ya sanar da amincewa da kudirin a zaman majalisar a Lafiya.

 

Shugaban majalisar ya ce kudirin dokar idan Gwamna Abdullahi Sule ya amince da shi zai magance kalubalen hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba a jihar.

 

Shugaban majalisar ya ce sashe na uku na kudirin ya ba da umarnin kafa Asusun Raya Al’umma na CDF don inganta walwalar al’ummomin da ke hakar ma’adanai ta hanyar samar da ayyukan more rayuwa da ayyukan jin kai.

 

“Kamfanonin hakar ma’adinai za su ba da gudummawar kashi 5% na kudaden shigarsu na shekara ga CDF. 50% na kudaden da ke cikin asusun CDF za a yi amfani da su ne don biyan kuɗi ga al’umma masu amfana, yayin da 50% za a ba da gudummawa ga samar da kuɗaɗen ayyukan,” in ji shi.

 

“Sashe na hudu na kudirin ya bukaci a kafa kungiyar sa ido kan ci gaban al’umma (CDMU)

 

“Sashi na biyar na kudirin ya ce, Kamfanonin hakar ma’adanai za su gabatar da cikakken rahoton shekara-shekara kan kudaden ci gaban al’umma da aiwatar da ayyukan ga (CDMU) da kuma karamar hukumar.

 

Dokta Jatau ya ce, shawarwarin kudurin sun kuma kunshi hukuncin daurin rai da rai kan rashin bin ka’idojin doka, musamman wajen soke yarjejeniyar ci gaban al’umma ta CDA.

 

“Hukunce-hukuncen karya ko rashin bin duk wani tanadi na wannan Doka zai kasance kamar haka;

 

(a) Ga Ƙungiyoyin Ma’adinai/Kamfanoni za su biya tarar jimillar Miliyan Goma (¥ 10,000.000.00) Naira ko aƙalla shekaru biyu (2) zuwa shekaru biyar (5) a gidan yari.

 

(b) Duk wani mutum zai biya tarar Naira Miliyan Biyar (N5,000.000.00) ko mafi karancin shekaru biyu (2) da kuma mafi girman zaman gidan yari na shekaru biyar (5).

 

Shugaban masu rinjaye na majalisar Mista Suleiman Yakubu Azara ya gabatar da kudirin amincewa da kudirin wanda ya samu goyon baya

Mr. Luka Iliya Zhekaba, shugaban marasa rinjaye na majalisar.

 

Majalisar dai ta amince da kudurin dokar ta zama doka baki daya kuma shugaban majalisar ya umurci magatakardar da ya ba shi kwafin domin tantancewa kafin mikawa Gwamna.

 

Za a ba da rahoton cewa mamba mai wakiltar mazabar Kokona ta Gabas, Mista Daniel Oga Ogazi ne ya dauki nauyin kudirin.

 

COV/Aliyu Muraki/lafia

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Lafiya nasarawa Shugaban Majalisar Shugaban majalisar hakar ma adanai

এছাড়াও পড়ুন:

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

A wata hira tare da gidan talabijin na Arise, Obi ya ce duk da cewa cire tallafin mai yana da muhimmanci, amma ya kamata a aiwatar da wannan tsari cikin tsari.

Ya ce ya amince cewa tallafin mai yana cike da ta’asa da cin hanci wanda akwai bukatar a kawo karshensa, amma ya yi suka ga hanyoyin da gwamnatin Tinubu take bi, yana bayyana su a matsayin wadanda aka yi ba bisa kwarewa ba.

Obi ya tambayi jagororin kula da kudin da aka ajiye daga cire tallafin, yana cewa, “Tun da aka ce manatallafin man fetur, ana cewa an cire ne saboda ba a so mu dunga ciyo bashi kuma kudaden za su ba da dama wajen zuba jari a muhimman ababen more rayuwa.

‘’Ina biliyoyin kudaden da aka tara? Ina aka zuba su a muhimman yankunan ci gaba? Kowa na sane da muhimman yankunan ci gaba da suka hada da ilimi, lafiya, da fitar da mutane daga talauci. Shin ko daya daga cikin wadannan abubuwan gda uku ya inganta? A’a.’’

Obi ya ce ya kamata a yi musayar farashi mai da masu ruwa da tsaki da kyau ta yadda zai rage tasirin ga matsalolin da ‘yan kasa ke ciki.

Da yake mayar da martini ga Obi, mai taimaka wa shugaban kasa kan batutuwan tsare-tsare, Daniel Bwala, ya bayyana dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP a matsayin mutum mai son kansa wanda ba ya da ilimin warware al’amuran da suka shafi tattalin arziki da shugabanci.

Bwala, a cikin wata sanarwa da ya wallafa ta shafinsa na sada zumunta na Tuwita, ya bayyana cewa ya yi mamakin yadda Obi ya yarda da manufofin tattalin arzikin Shugaba Tinubu, musamman kan cire tallafin mai da hada-hadar kudaden waje, amma ya jaddada cewa Obi sauran manyan ‘yan adawa suna neman samun iko ne kawai ko ta wani hali a wannan lokaci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
  • Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun
  • Masana Ilimin Nukiliyar Iran Sun Yi Shahada
  • Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki
  • Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje
  • Cikakken Jerin Sunaye: Tinubu Ya Karrama ‘Yan Nijeriya 102 Don Bukin Ranar Dimokuradiyya Ta 2025
  • An Gudanar Da Taron Ministoci Masu Daidaita Ayyukan Da Aka Amince Yayin Taron FOCAC
  • Ana shirin mayar da rantsar da Shugaban Nijeriya zauren majalisa
  • Jagora Ya Bambance Tsakanin Majalisun Dokokin Kasashe A Fagen Gudanar Da Ayyukan Kasa
  • Mokwa: Zulum ya kai ziyarar jaje Neja, ya bayar da tallafin N300m