Majalisar dokokin jihar Nasarawa ta amince da dokar kafa doka da za ta samar da tsari da kula da bada izinin filaye da yarjejeniyoyin al’umma ga masu hakar ma’adanai da sauran batutuwan da suka shafi hakan.

 

Shugaban Majalisar Dokta Danladi Jatau, ya sanar da amincewa da kudirin a zaman majalisar a Lafiya.

 

Shugaban majalisar ya ce kudirin dokar idan Gwamna Abdullahi Sule ya amince da shi zai magance kalubalen hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba a jihar.

 

Shugaban majalisar ya ce sashe na uku na kudirin ya ba da umarnin kafa Asusun Raya Al’umma na CDF don inganta walwalar al’ummomin da ke hakar ma’adanai ta hanyar samar da ayyukan more rayuwa da ayyukan jin kai.

 

“Kamfanonin hakar ma’adinai za su ba da gudummawar kashi 5% na kudaden shigarsu na shekara ga CDF. 50% na kudaden da ke cikin asusun CDF za a yi amfani da su ne don biyan kuɗi ga al’umma masu amfana, yayin da 50% za a ba da gudummawa ga samar da kuɗaɗen ayyukan,” in ji shi.

 

“Sashe na hudu na kudirin ya bukaci a kafa kungiyar sa ido kan ci gaban al’umma (CDMU)

 

“Sashi na biyar na kudirin ya ce, Kamfanonin hakar ma’adanai za su gabatar da cikakken rahoton shekara-shekara kan kudaden ci gaban al’umma da aiwatar da ayyukan ga (CDMU) da kuma karamar hukumar.

 

Dokta Jatau ya ce, shawarwarin kudurin sun kuma kunshi hukuncin daurin rai da rai kan rashin bin ka’idojin doka, musamman wajen soke yarjejeniyar ci gaban al’umma ta CDA.

 

“Hukunce-hukuncen karya ko rashin bin duk wani tanadi na wannan Doka zai kasance kamar haka;

 

(a) Ga Ƙungiyoyin Ma’adinai/Kamfanoni za su biya tarar jimillar Miliyan Goma (¥ 10,000.000.00) Naira ko aƙalla shekaru biyu (2) zuwa shekaru biyar (5) a gidan yari.

 

(b) Duk wani mutum zai biya tarar Naira Miliyan Biyar (N5,000.000.00) ko mafi karancin shekaru biyu (2) da kuma mafi girman zaman gidan yari na shekaru biyar (5).

 

Shugaban masu rinjaye na majalisar Mista Suleiman Yakubu Azara ya gabatar da kudirin amincewa da kudirin wanda ya samu goyon baya

Mr. Luka Iliya Zhekaba, shugaban marasa rinjaye na majalisar.

 

Majalisar dai ta amince da kudurin dokar ta zama doka baki daya kuma shugaban majalisar ya umurci magatakardar da ya ba shi kwafin domin tantancewa kafin mikawa Gwamna.

 

Za a ba da rahoton cewa mamba mai wakiltar mazabar Kokona ta Gabas, Mista Daniel Oga Ogazi ne ya dauki nauyin kudirin.

 

COV/Aliyu Muraki/lafia

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Lafiya nasarawa Shugaban Majalisar Shugaban majalisar hakar ma adanai

এছাড়াও পড়ুন:

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

Wannan lamari ya haifar da tambaya kan yiwuwar dorewar shirin sauye-sauye da na zamani da ake gudanarwa a karkashin jagorancin Babban Kwanturola Janar, Adewale Adeniyi.

 

Adewale Adeniyi, wanda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya kara wa wa’adin mulki na shekara guda, shima zai yi ritaya daga hukumar a watan Agusta, 2026.

 

A halin yanzu, za a dauki babban mataki kafin a cike gibin ma’aikata da ake bukata a hukumar kwastam, musamman idan aka yi la’akari da cewa jami’ai 825 za su bar aiki ba tare da sabon daukar ma’aikata ba.

 

Binciken da leadership Hausa ta gudanar ya gano cewa ritayar ta shafi kowane mataki a hukumar daga manyan shugabanni, zuwa matsakaita, har da kananan jami’ai.

 

Daga cikin jami’ai 825 da za su yi ritaya saboda shekaru 60 da suka kai ko kuma shekaru 35 na aiki:

 

5 suna da mukamin mataimakan kwanturola na kasa wato (DCG) sai wasu kananan mataimaka Kwanturola na kasa (ACG) su 13 sai kuma Kwanturololi ( CAC) guda 53 da mataimakanau (DC) guda 51 kananan mataimaka Kwanturola ( AC) guda 46.

 

Sauran sune ; masu mukaman (CSC) guda 61 sai ( SC) Guda 226 da ( DSC) su 285 sai (ASC I) 64 da (ASC II) su 10 (IC), su 8 (CA I) guda 1 sai (CA II) su 2 Jami’an mataimaka Kwanturola Janar ( DCG) guda biyar da ritayar ta shafa su ne: Mista C.K. Niagwan da K.I. Adeola da kuma Mista S. Chiroma; Mr. G.M. Omale; da Mista A. Nnadi.

 

Kananan Jami’an mataimaka Kwanturola Janar (ACG) guda goma sha uku (13) da abin ya shafa su ne: K.C. Egwuh, M.S. Yusuf, da Z.M. Gaji da N.P. Umoh da O.A. Adebakin da kuma T. Bomodi da B.O. Olomu, O.P. Olaniyan, I.K. Oladeji, K. Mohammed, O.A. Adebakin, da B. Mohammed, da C.C. Dim.

 

Daga cikin Kwanturololi da za su yi ritaya a 2026, akwai: D. Abubakar, da O.Y. Shuaibu, F.A. Bodunde da P.C. Chibuoke, da kuma O.O. Akingbade, da A. Salihu, da wasu da dama.

 

A matsayin shiri kafin ranar ritayar 2026, Hedikwatar Hukumar Kwastam da ke Abuja ta bayar da umarni ga dukkan jami’an da abin ya shafa su fara shirye-shiryen barin aiki kamin ranar ta isko su.

 

Hakazalika, An umurce su da su mika sanarwar izinin hutu na watanni uku kafin ritaya ga Babban Kwanturola Janar na Kwastam (CGC).

 

A cikin takardar da wakilinmu ya gani mai taken “Jerin karshe Na Jami’ai da Ma’aikata Don Ritaya A Shekarar 2026”, wacce aka fitar ranar 19 ga Satumba, 2025, kuma Kwanturola A.A. Bazuaye ya sanya hannu a madadin DCG na Sashen Albarkatun Dan Adam (HR), an bukaci jami’an da abin ya shafa da su bi doka da tsari.

 

Kamar yadda takardar ta ce: “A bisa Dokar Aikin Gwamnati (PSR No. 100238) da kuma Sanarwar Gwamnati mai lamba 36216/S.1/D/T: CR1/2001/5 na 20/3/2001, dukkan jami’an da suka cika shekarun ritaya a 2026 za su bar aiki kuma su tafi hutu na watanni uku kafin ranar da ritayar za ta fara aiki.”

 

Haka kuma, an umurci dukkan jami’an da abin ya shafa su tabbatar da bin umarnin, tare da tura takardar sanarwar hutun ritayarsu ga Babban Kwanturola Janar yadda ya dace.

 

Takardar ta kuma bukaci Koordinetocin Yankuna da Kwamandojin Yankuna su sanar da duk jami’an da abin ya shafa a yankunansu.

 

Da wannan yawan ma’aikata da za su bar aiki a 2026, har yanzu ana cikin tunanin irin dabarar da shugabancin kwastam zai yi amfani da ita don cike gibin da zai biyo baya, tare da tabbatar da ci gaba da sabbin domin gudanar da ayyukan hukumar.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara October 10, 2025 Manyan Labarai Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano October 10, 2025 Labarai Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN October 10, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Shura ta fara ganawar sirri da Malam Triumph
  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista
  • Ƴan Bindiga Sun Amince Da Dakatar Da Hare-Hare A Ƙananan Hukumomi 5 A Katsina
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Yi  Afuwa Ga Wasu Mutanen Da Kotuna Su Ka Hukunta
  • Ayyukan Da Suka Sauya Fuskar Zamfara A Ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal
  • Wani Dan Majalisar Dokokin Kasar Iran Ya Ja Kunnen Amurka Kan Taba Jiragen Dakon Man Kasa
  • Majalisar Turai Ta Bukaci Kasashen Nahiyar Su Kakkabo Jiragen Yakin Rasha
  • Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya
  • Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya