Majalisar dokokin jihar Nasarawa ta amince da dokar kafa doka da za ta samar da tsari da kula da bada izinin filaye da yarjejeniyoyin al’umma ga masu hakar ma’adanai da sauran batutuwan da suka shafi hakan.

 

Shugaban Majalisar Dokta Danladi Jatau, ya sanar da amincewa da kudirin a zaman majalisar a Lafiya.

 

Shugaban majalisar ya ce kudirin dokar idan Gwamna Abdullahi Sule ya amince da shi zai magance kalubalen hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba a jihar.

 

Shugaban majalisar ya ce sashe na uku na kudirin ya ba da umarnin kafa Asusun Raya Al’umma na CDF don inganta walwalar al’ummomin da ke hakar ma’adanai ta hanyar samar da ayyukan more rayuwa da ayyukan jin kai.

 

“Kamfanonin hakar ma’adinai za su ba da gudummawar kashi 5% na kudaden shigarsu na shekara ga CDF. 50% na kudaden da ke cikin asusun CDF za a yi amfani da su ne don biyan kuɗi ga al’umma masu amfana, yayin da 50% za a ba da gudummawa ga samar da kuɗaɗen ayyukan,” in ji shi.

 

“Sashe na hudu na kudirin ya bukaci a kafa kungiyar sa ido kan ci gaban al’umma (CDMU)

 

“Sashi na biyar na kudirin ya ce, Kamfanonin hakar ma’adanai za su gabatar da cikakken rahoton shekara-shekara kan kudaden ci gaban al’umma da aiwatar da ayyukan ga (CDMU) da kuma karamar hukumar.

 

Dokta Jatau ya ce, shawarwarin kudurin sun kuma kunshi hukuncin daurin rai da rai kan rashin bin ka’idojin doka, musamman wajen soke yarjejeniyar ci gaban al’umma ta CDA.

 

“Hukunce-hukuncen karya ko rashin bin duk wani tanadi na wannan Doka zai kasance kamar haka;

 

(a) Ga Ƙungiyoyin Ma’adinai/Kamfanoni za su biya tarar jimillar Miliyan Goma (¥ 10,000.000.00) Naira ko aƙalla shekaru biyu (2) zuwa shekaru biyar (5) a gidan yari.

 

(b) Duk wani mutum zai biya tarar Naira Miliyan Biyar (N5,000.000.00) ko mafi karancin shekaru biyu (2) da kuma mafi girman zaman gidan yari na shekaru biyar (5).

 

Shugaban masu rinjaye na majalisar Mista Suleiman Yakubu Azara ya gabatar da kudirin amincewa da kudirin wanda ya samu goyon baya

Mr. Luka Iliya Zhekaba, shugaban marasa rinjaye na majalisar.

 

Majalisar dai ta amince da kudurin dokar ta zama doka baki daya kuma shugaban majalisar ya umurci magatakardar da ya ba shi kwafin domin tantancewa kafin mikawa Gwamna.

 

Za a ba da rahoton cewa mamba mai wakiltar mazabar Kokona ta Gabas, Mista Daniel Oga Ogazi ne ya dauki nauyin kudirin.

 

COV/Aliyu Muraki/lafia

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Lafiya nasarawa Shugaban Majalisar Shugaban majalisar hakar ma adanai

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan Majalisar Kudu sun roƙi Tinubu ya yi wa Nnamdi Kanu Afuwa

’Yan Majalisar Wakilai daga yankin Kudu sun yi kira ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya yi wa jagoran ƙungiyar IPOB, Nnamdi Kanu, afuwa bayan da kotu ta yanke masa hukuncin ɗaurin rai da rai.

Kungiyar ’Yan Majalisar Wakilai daga yankin Kudu maso Gabas ta yi kira ga Shugaba Tinubu da ya yi amfani da ikon da kundin tsarin mulki ya ba shi, wajen yi wa Nnamdi Kanu afuwa wanda kotu ta same shi da laifin ta’addanci.

Alƙali James Omotosho na Babban Kotun Tarayya da ke Abuja ne ya yanke hukuncin, inda ya same shi da laifi a kan tuhumar da ake masa guda bakwai, sannan ya yanke masa hukuncin daurin rai da rai.

Tuni aka tura Nnamdi Kanu zuwa gidan yari a Jihar Sakkwato inda yake zaman waƙafi.

Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina NAJERIYA A YAU: Irin Radadin Da Masu Cutar Amosanin Jini Ke Fuskanta

A cikin sanarwa bayan taron gaggawa da suka gudanar a Abuja, ’yan majalisar sun ce duk da cewa suna girmama kotu da tsarin shari’a, lamarin ya rikiɗe zuwa matsalar ƙasa mai tasiri ga rayuwar jama’a, tattalin arziki da tsaro.

Da yake karanta sanarwar, Hon. Iduma Igariwey ya ce yin afuwa zai taimaka wajen rage tashin hankali da dawo da zaman lafiya a yankin.

Sun lissafa dalilai guda huɗu da suka sa suka yi wannan kira.

Dalilan da suke bayyana su ne ƙaruwa da rashin tsaro da tashin hankali da ke da alaƙa da tsare Kanu; Wahalar rayuwa da tattalin arziki da jama’a ke fuskanta da kuma buƙatar shugabanci mai tausayawa wajen shawo kan matsalolin ƙasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutuwar Sheikh Dahiru Bauchi Babban Rashi Ne Ga Kasa Baki Daya- Shugaba Tinubu
  • Mutuwar Sheikh Dahiru Bauchi Babban Rashi Ne Ga Kasa Baki Daya
  • Majalisar Wakilai ta nemi gwamnati ta gaggauta dauko Jonathan daga Guinea Bissau
  • An Zabi JMI A Cikin Majalisar Zartarwan Ta Hukumar Yaki Da Makaman Guba Ta Duniya CWC
  • Gwamna Radda Ya Sanya Hannu Kan Kasafin 2026 Ya Zama Doka
  • Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen jakadu
  • Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yabawa Pakistan Saboda Goyon Bayanta
  • Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yawaba Pakistan Saboda Goyon Bayanta
  • Yan Majalisar Kudu Sun Nemi Gafarar Tinubu Ga Nnamdi Kanu
  • ’Yan Majalisar Kudu sun roƙi Tinubu ya yi wa Nnamdi Kanu Afuwa