HausaTv:
2025-06-29@06:41:34 GMT

Sojojin HKI  Sun Sake Yin Kisan Kiyashi Mai Firgitarwa A Cikin Asibitin Gaza

Published: 14th, May 2025 GMT

A jiya Talata sojojin HKI su ka kai wani mummunan hari akan asibitin Gaza na “Turai” da kuma zagayensa da hakan ya yi sanadiyyar samun shahidai da kuma jikkata wasu da dama.

Sojojin mamayar sun yi amfani da jiragen sama wajen kai wadannan munanan hare-haren akan Asibitin da ake kir ana turai, da kuma gefensa a kudu maso gabashin birnin  Khan-Yunus.

Tashar talabijin din ‘almayadin’ ta bayar da labarin cewa; jiragen saman na HKI sun kai hare-haren ne ta hanyar harba makamai masu linzami akan bangare da kuma kula da matsalolin gaggawa na asibitin da kuma bangaren dake kula da asibitin da gyara abubuwan da su ka baci.

Haka nan kuma jiragen yakin na HKI sun kai wasu hare-haren a cikin sansanoni dake cike da Falasdinawan da aka raba su da gidajensu saboda yaki da suke daura da asibitin.

Gwamman Falasdinawa ne dai su ka yi shahada,kuma wasu gwamman majiyyatan suna a karkashin baraguzan gininin asibitin da ya fada a kansu.

Masu ayyukan ceto sun sanar da tsamo shahidai 28 da kuma wadanda su ka jikkata su 70,kamar yadda mai Magana da yawun kungiyar Muhammad Basal ya ambata.

Jiragen yakin HKI sun harba makamai masu linzami guda 6, da hakan ya haddasa rusau mai yawa akan ginin asibitin.

Tuni dai masu tafiyar da asibitin su ka sanar da cewa, ba za su iya karbar wadanda su ka jikkata ba.

An dauki marasa lafiya da kuma wadanda su ka jikkata zuwa asibitin “Nasir” wanda shi ma bangarensa mafi girma ya rushe.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Falasdinu: Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kai Hare-hare A Yammacin Kogin Jordan
  • Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 
  • Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
  • Yunwa ta kashe ƙananan yara 66 a Gaza
  • Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato
  •  Kananan Yara 2 Falasdinawa  Masu Shan Nono Sun Yi Shahada Saboda Yunwa
  • Bom ya kashe mutum hudu da raunata 21 a Yobe
  • JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa
  • Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja
  • Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana