HausaTv:
2025-05-14@15:46:04 GMT

Sojojin HKI  Sun Sake Yin Kisan Kiyashi Mai Firgitarwa A Cikin Asibitin Gaza

Published: 14th, May 2025 GMT

A jiya Talata sojojin HKI su ka kai wani mummunan hari akan asibitin Gaza na “Turai” da kuma zagayensa da hakan ya yi sanadiyyar samun shahidai da kuma jikkata wasu da dama.

Sojojin mamayar sun yi amfani da jiragen sama wajen kai wadannan munanan hare-haren akan Asibitin da ake kir ana turai, da kuma gefensa a kudu maso gabashin birnin  Khan-Yunus.

Tashar talabijin din ‘almayadin’ ta bayar da labarin cewa; jiragen saman na HKI sun kai hare-haren ne ta hanyar harba makamai masu linzami akan bangare da kuma kula da matsalolin gaggawa na asibitin da kuma bangaren dake kula da asibitin da gyara abubuwan da su ka baci.

Haka nan kuma jiragen yakin na HKI sun kai wasu hare-haren a cikin sansanoni dake cike da Falasdinawan da aka raba su da gidajensu saboda yaki da suke daura da asibitin.

Gwamman Falasdinawa ne dai su ka yi shahada,kuma wasu gwamman majiyyatan suna a karkashin baraguzan gininin asibitin da ya fada a kansu.

Masu ayyukan ceto sun sanar da tsamo shahidai 28 da kuma wadanda su ka jikkata su 70,kamar yadda mai Magana da yawun kungiyar Muhammad Basal ya ambata.

Jiragen yakin HKI sun harba makamai masu linzami guda 6, da hakan ya haddasa rusau mai yawa akan ginin asibitin.

Tuni dai masu tafiyar da asibitin su ka sanar da cewa, ba za su iya karbar wadanda su ka jikkata ba.

An dauki marasa lafiya da kuma wadanda su ka jikkata zuwa asibitin “Nasir” wanda shi ma bangarensa mafi girma ya rushe.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran: Babban Kwamandan Sojojin Ruwa Na JMI Yace Sojojinsa A Shirye Suke Su Shiga Yaki Da Makiya

Babban hafsan hafsoshin sojojin JMI ya bayyana cewa sojojin kasar musamman sojojin ruwa a shirye suke su shigaba yaki dank are kasar a ko yauce, ya kuma kara da cewa idan makiya sun yi wani kuskure zasu yi nadamar hakan.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ya nakalto Manjo Janar Mohammad Hussain Bakiri yana fadar haka a jiya litinin a lokacinda shi da wasu manya manayan jami’an sojojin kasar suka kai ziyarar ganewa kansu irin shirin da sojojin kasar suke ciki a tashoshin jiragen ruwa da suke gabar tekun Farisa da kuma arewacin mashigar ruwa ta Hurmus

Tare da manjo janar Bakiri dai akwai kwamandan sojojin ruwa na dakarun IRGC  Manjo Janar Abdolrahim Mousavi, sai kuma Manjo Janar Hossein Salami shugaban Lundunonin IRGC da kuma wasu manya-manyan jami’an sojojin kasar.

A wani labarin kuma Janar Salami babban kwamandan sojojin IRGC gaba daya ya bayyana cewa Iran zata kai hari a kan duk wani wurin da makami ya rashi zuwa kasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Falasdinawa Sun Harba Wa HKI Makamai Masu Linzami
  • Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe
  •  Falasdinawa Da Dama Sun Yi Shahada A Yau Talata
  • Iran: Babban Kwamandan Sojojin Ruwa Na JMI Yace Sojojinsa A Shirye Suke Su Shiga Yaki Da Makiya
  • Iran Ta Yi Allawadai Da Hare-Haren HKI Kan Wani Sansanin Yan Gudun Hijira A Gaza
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Gudanar Da Kisan Kiyashi Kan Falasdinawa A Jabaliya Da Khan Yunus
  • Falasdinawa 1500 Ne Su Ka Zama Makafi Sanadiyyar Yaki
  • HKI Ta Kai Hare Hare Kan Wani  Sansanin Yan Gudun Hijira A Yamma Da Kogin Jordan
  • Kungiyar Hamas Ta Amince Ta Saki Fursinan Yaki Wanda Yake Da Jinsiyar Amurka Da HKI