Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa
Published: 11th, May 2025 GMT
Ya ce: “A yau ni ne Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Jama’a na Nijeriya. Ba kawai ɗan watsa shirye-shirye ba ne ni, ni ne babban mai magana da yawun gwamnatin Nijeriya.
“Don haka za ka ga yadda burin da ake ganin kamar an kashe shi shekaru da dama da suka wuce, ya dawo ya amfanar.”
Ya ce kafin ya zama minista, ya mallaki tashar rediyo da talbijin har ma da gidan jarida.
Ministan ya buƙaci matasa da kada su yi watsi da burin su ko da ba sa ganin damar cimma buƙatar su. Ya ce shauƙin sa ne yake motsa shi wajen yaƙi da yaɗuwar labaran ƙarya ta hanyar ƙarfafa fahimtar kafofin sadarwa.
Idris ya kuma bayyana cewa daga watan Nuwamba mai zuwa, Nijeriya za ta fara gudanar da Cibiyar Ilimin Kafofin Sadarwa ta UNESCO mai Mataki na 2.
Ya ce: “Ni ne na jagoranci Nijeriya wajen kafa Cibiyar Ilimin Kafofin Sadarwa ta UNESCO Category 2 – wadda ita ce irin ta ta farko a duniya – kuma za a kafa ta a Abuja. Zuwa watan Nuwamba idan hukumar UNESCO ta bayar da amincewar ƙarshe, duk duniya za ta dinga kallon Nijeriya.”
Ya ƙara da cewa, “Don haka ba wai kawai ku matasa maza da mata ku ɗauki makirfo, kwamfuta ko wayoyin ku na zamani ku fara faɗin duk abin da kuka ga dama ba ne. Kuna iya samun ilimi, amma kuma kuna buƙatar fahimtar yadda kafofin sadarwa suke.”
An tsara cibiyar ne don koyar da matasa daga Nijeriya da ƙasashen waje dabarun amfani da kafofin sadarwa cikin basira tare da yin kaffa-kaffa da kuma kare kan su daga labaran ƙarya da yaɗuwar bayanan da ba su da tushe.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Andrea Thompson ta zama mace mafi ƙarfi a duniya
An naɗa Andrea Thompson, ’yar ƙasar Birtaniya, a matsayin mace mafi ƙarfi a duniya.
Wannan na zuwa ne bayan tabbatar da cewa wanda aka bayyana a matsayin zakara — Jammy Booker — tun da farko namiji ne da aka sauya masa halitta zuwa mace, lamarin da ya sa aka soke nasararsa bisa saɓawa dokokin gasar.
Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro Real Madrid za ta yi karon-batta da Olympiacos a Gasar Zakarun TuraiThompson mai shekaru 43, ta karɓi lambar yabon ne daga masu shirya gasar nunin ƙarfi ta duniya, kwanaki biyu bayan kammala bikin a Arlington da ke birnin Texas na Amurka, wanda aka gudanar a daga 20 zuwa 23 ga watan Nuwamba.
Gasar nuna ƙarfin ta duniya tana da tsauraran ƙa’idoji, inda ake bai wa ’yan takara damar fafatawa ne kawai bisa jinsinsu na asali domin tabbatar da adalci.
A gasar bana, Thompson ta ƙare a matsayi na biyu bayan kammala fannonin wasanni guda shida da suka haɗa da ɗaga nauyi da sauran gwaje-gwaje a rukunin mata.