Jiragen yaki marasa matuka ciki sun kai hare-hare kan sansanin sojin ruwa mafi girma a Port Sudan

Sojojin tsaron saman Sudan sun dakile wani harin da jirgin sama maras matuki ciki ya yi niyyar kai wa kan mafi girman sansanin sojin ruwan kasar da sanyin safiyar Laraba, in ji wata majiyar soji. Wannan dai shi ne rana ta hudu a jere da ake kai hare-hare kan birnin Port Sudan da ke karkashin ikon gwamnati.

Majiyar wadda ta bukaci a sakaye sunanta ta ce, jiragen saman yakin marasa matuka ciki sun kai hari kan sansanin sojin ruwa na Flamingo, kuma na’urorin kakkabo makamai masu linzami suna kakkabo makaman da aka harba. Tsawon rabin sa’a ana jin karar makaman roka masu linzami da aka yi amfani da su a kasa da kuma wasu bama-bamai da suka samo asali daga arewacin Port Sudan, inda sansanin sojin ruwa yake.

Port Sudan dai ita ce wurin zama na wucin gadi na gwamnatin kasar, lamarin da ya sanya ta zama hedkwatar rikon kwarya bayan barkewar yaki tsakanin sojojin Sudan da dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces.

Tun a watan Afrilun shekara ta 2023 ne Sudan ta fada cikin kazamin rikici tsakanin kwamandan sojojin kasar Janar Abdel Fattah al-Burhan, wanda shi ne shugaban Majalisar Gudanar da Mulkin kasar tun bayan juyin mulkin shekarar 2021, da kuma tsohon mataimakinsa, Janar Mohamed Hamdan Dagalo, kwamandan dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda ISWAP ta kashe sojoji ta kwashe makamai a sansanin soji a Borno

Mayaƙan Boko Haram sun kashe sojoji da ba a san adadinsu ba tare da yin awon gaba da wasu da dama bayan wani ƙazamin hari da suka kai a sansanin soji da ke yankin Marte a Jihar Borno.

Majiyoyin soji sun ce mayaƙan ƙungiyar sun fi karfin sojojin, inda suka kwashi makamai masu tarin yawa sa’annan suka cinna wa ma’ajiyar makamai da ke sansanin sojin wuta.

Mazauna yankin sun bayyana cewa da misalin ƙarfe 3 na asuba, kafin wayewar garin ranar Asabar ne Boko Haram ta ƙaddamar da harin.

Wani soja da ya nemi a ɓoye sunansa ya ce, “ISWAP ta ƙwace Marte, an kashe sojoji da dama, an kama wasu, amma wasu sun samu sun tsere zuwa Dikwa, inda runduna ta 24 take.

Ya kashe abokinsa saboda hula a Kano NAJERIYA A YAU: Matsalar lantarki: ’Yan Najeriya sun yi tir da biyan diyya ga ’yan Band A

“’Yan ta’addan sun ƙona tankokin yaƙi kuma sun kwashi makamai daga sansanin sojin,” in ji shi.

Wani mazaunin Marte, gari mai nisan kilomita 38 daga Dikwa, hedikwatar Ƙaramar Hukumar Dikwa, ya ce sun ji karar harbe-harben kuma daga bisani suka ga jirgin soji yana shawagi.

Ya ce, “mun samu labarin cewa an tura ƙarin jami’an tsaro kuma an ƙwato sansanin sojin, amma ’yan ta’addan sun sun sace makamai kuma sun koma motoci da rumbun makaman sojin da ke wurin.”

Ya ci gaba da cewa, “abin takaici mayaƙan sun tsare mata da ƙananan yara da dama a Sabon Marte, amma wasu da dama sun samu tserewa zuwa Dikwa domin tseratar da rayuwarsu.

“Ba a daɗe ba da ’yan ƙungiyar suka kai hari a Malam Fatori, inda suka kashe sojoji 21 da wani daga cikin kwamdojinmu.”

Daga watan Janairu zuwa yanzu an kai wa sansanonin soji da dama hare-hare a yankin Tafkin Chadi da kuma Dutsen Mandara da ke Dajin Sambisa a jihohin Borno da Yobe.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Aiwatar Da Kisan Kiyashi Kan Falasdinawa A Gaza
  • Sojojin HKI  Sun Sake Yin Kisan Kiyashi Mai Firgitarwa A Cikin Asibitin Gaza
  •  Falasdinawa Da Dama Sun Yi Shahada A Yau Talata
  • Yadda ISWAP ta kashe sojoji ta kwashe makamai a sansanin soji a Borno
  • Iran Ta Yi Allawadai Da Hare-Haren HKI Kan Wani Sansanin Yan Gudun Hijira A Gaza
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Gudanar Da Kisan Kiyashi Kan Falasdinawa A Jabaliya Da Khan Yunus
  • ‘Yan Tawayen Sudan Sun Kai Hari Kan Gidan Yarin Al-Obeid Tare Da Kashe Fararen Hula Masu Yawa
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Boko Haram 5, Sun Kwato Makamai A Borno
  • HKI Ta Kai Hare Hare Kan Wani  Sansanin Yan Gudun Hijira A Yamma Da Kogin Jordan