Shugaban kasar Amurka Donal Trump ya bukaci shugaban kasar Ukraine ya amince da tayin shugaban Putin na Rasah na sun hadu a birnin Istambul na kasar Turkiya don tattauna yiyuwar  tsagaita budewa juna wuta.

Kamfanin dillancin labaran Sputnik na kasar Rasha ya nakalto shugaban Trump yana fadar haka a jiya Asabar ya kuma bayyana cewa wannan wata dama ce kawo karshen zubar da jinni tsakanin kasashen biyu na fiye da shekaru uku da suka gabata.

Trump ya bayyana haka ne a shafinsa na yanar gizo, ya kuma kara da cewa, haduwar shuwagabannin biyu zai fayyace matsayin yakin, da kuma yiyuwar dakatar da shi nan kusa. Banda haka haduwarsu zai bawa kasar Amurka damar gane matakin da zata dauka nan gaba, haka ma tarayyar turai.

Kafin haka dai a ranar Asabar da ta gabata ce, shugaba Vladimir Putin na kasar Rasha ya bayyana cewwa, Rasha a shirye take ta bude tattaunawa gaba da gaba da kasar Ukraune a birnin Istambul na kasar Turkiyya a ranar 15 ga watan mayun da muke ciki wato ranar Alhamis mai zuwa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Musanta Zargin Kamfanin Dillancin Labaran Reuters Dangane Da Aikawa Rasha Makamai

Jakadan JMI a MDD ya musanta zargin kamfanin dillancin labaran reuters dangane da rotohonsa na cewa JMI tana aika makamai masu linzami zuwa kasar Rasah don taimakawa kasar Rasha yakin da take fafatwa da kasar Ukraine fiye da shekaru 3 da suka gabata.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto

Ofishin jakadancin JMI dake birnin NewYork ya kara da cewa, abin mamaki da kamfanin dilancin laraban reuters, shi ne ba wannan ne karo na farko yake yada labaran karya a duniya wanda wai yake samu daga wasu wadanda basa son a bayyana sunansu.

Kafin haka dai JMI ta sha nanata cewa bata bayan wani bangare daga cikin bangarori biyu da suke fafatawa a kasar Ukraine.

Don haka bata taba taimakawa kasar Rasha da makamai don yakar kasar Ukraine ba, kuma bata taba taimaka kasar Ukraine.

Ofishin jakadancin ya bayyana cewa ra’ayinta da so samu ne ta zama mai shiga tsakani don warware rikicin kasar ta Ukraine.

Amma reuters ya ci gaba da bada labaran karya wadanda suke cewa tana shirin aikawa kasar Rasha damdamalin cilla makamai masulinzami wadanda Iran ta aikawa kasar Rasa a Bara, kamar yadda Amurka take zargin hakan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Zabi Birnin Esfahan Na Kasar Iran A Matrsayin Cibiyar Yawon Bude Ido A Asia Na Shekara Ta 2025
  • Kungiyar Hamas Ta Amince Ta Saki Fursinan Yaki Wanda Yake Da Jinsiyar Amurka Da HKI
  • Iran ta ce tattaunawa ta hudu da Amurka tana da wahala amma tana da amfani  
  • Putin ya ba da shawarar tattaunawa kai tsaye da Ukraine a Istanbul
  • Putin  Na Rasha Ya Gana Da Shugabannin Afirka Akan Batun Tsaro
  • Iran Ta Musanta Zargin Kamfanin Dillancin Labaran Reuters Dangane Da Aikawa Rasha Makamai
  • Shugaban Putin Ya Gana Da Sisi Don Karfafa Harkokin Kasuwanci Tsakanin Kasashen Biyu
  • Indiya da Pakistan sun cimma yarjejeniyar tsagaita wuta
  • Amurka da Iran zasuyi tattaunawa ta hudu a ranar Lahadi