Da muna kan mulki ni da Lamido da mun ƙalubalanci Tinubu — Amaechi
Published: 14th, May 2025 GMT
Tsohon Gwamnan Jihar Ribas, Rotimi Amaechi, ya bayyana cewa da shi da Sule Lamido har yanzu suna kan kujerar mulki, da sun fito ƙarara sun ƙalubalanci Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Amaechi ya bayyana haka ne a wajen ƙaddamar da littafin tarihin rayuwar Sule Lamido mai suna ‘Being True to Myself’ da aka gudanar a Abuja.
“Da mun fito da ƙarfinmu, mun ƙalubalanci gwamnati, mun kalubalanci shugaban ƙasa,” in ji Amaechi.
“Haka muka saba a lokacin muna Gwamnoni. Muna da kishin ƙasa da ƙwarin gwiwar sauya al’amura.”
Ya bayyana yadda dangantakar siyasar da ke tsakaninsa da Lamido, inda ya ce duk da kasancewar suna da alaƙa a wancan lokaci, sun raba gari ne lokacin da Lamido ya ƙi komawa jam’iyyar APC domin su haɗa ƙarfi wajen kayar da tsohon Shugaban Ƙasa Goodluck Jonathan.
“A lokacin, Lamido ya zaɓi kafa sabuwar jam’iyya – SDP, amma mu mun yarda cewa za mu fi samun nasara a jam’iyyar APC,” in ji Amaechi.
“Wannan ne ya sa hanyoyinmu suka rabu.”
Shugaba Tinubu, wanda Ministan Yaɗa Labarai, Mohammed Idris, ya wakilta a taron, ya ce shugaban ƙasa ya amince da mahawara mai ma’ana, amma hakan ba zai hana shi yi wa ƙasar nan abin da ya dace ba.
Tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo ma ya yi jawabi a wajen taron, inda ya bayyana Lamido a matsayin jagoran da ke da gaskiya da tsayawa kan aƙidarsa, inda ya ce lokacin da Lamido ke Ministan Harkokin Waje, ya taimaka wajen dawo da mutuncin Najeriya a idon duniya.
Obasanjo ya ce, “Sule ya taɓa faɗa, ‘Idan ka ga ban cancanta ba, ka ba ni minti biyar kawai na yi murabus. Amma ka da ka tambaye ni takardar murabus da ba ta da kwanan wata.’ Na girmama wannan matsayi nasa.”
Tsohon Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa, Farfesa Attahiru Jega, wanda ya wakilci Janar Abdulsalami Abubakar, ya jinjina wa littafin Lamido da cewa ya bayyana tarihin siyasar Najeriya da darusan da matasa za su amfana da su.
Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Dokta Iyorchia Ayu, wanda ya yi nazari a kan littafin, ya soki gwamnatin APC da cewa ta zama annoba ga Najeriya.
Ya buƙaci Lamido da ya ci gaba da rubuta littattafai domin su zama jagora ga ’yan Najeriya.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?
Haka zalika, sun ki bayyana takamaiman wajen da za a daura auren, har sai bayan an kammala, inda suka bayyana yin hakan a matsayin wata hanya ta kawar da cece-kuce daga al’umma.
Kazalika a ‘yan watannin da suka gabata kuma, an sake daura auren jaruma a masana’antar Kannywood, Rahama Sadau tare da angonta Ibrahim Garba, a wani biki wanda za a iya kira da na sirri da aka gudanar a birnin Kaduna, daura auren shahararriyar jarumar Kannywood din, Rahma Sadau da mijinta Ibrahim Garba, wanda aka gudanar a ranar Asabar, ya yi matukar bai wa mutane mamaki, duba da cewa; kafin daurin auren babu wata alama ko sanarwa da aka fitar daga makusantan mijin ko matar.
An yi bikin da safe, a Masallacin Atiku Auwal da ke Unguwar Rimi, inda ‘yan’uwa da abokan arziki suka halarta, Rahma yayin da take magana da manema labarai ta bayyana cewa; ta zabi yin bikin cikin natsuwa ne, domin kauce wa hayaniya, bayan labarin ya bayyana a kafafen sada zumunta, ta tabbatar da daura auren nata.
Rahma ta shahara a fina-finan Kannywood da kuma wasu daga cikin fina-finan Nollywood, bayan da aka daura auren, masoyanta da abokan aikinta, suka tura mata sakwannin taya murna daga sassa daban-daban na Nijeriya, wannan aure ya zo ne watanni kadan bayan rasuwar mahaifinta, wanda ya rasu bayan gajeriyar rashin lafiya.
Haka yasa ake saka alamar tambaya a kan jaruman masana’antar ta Kannywood, a kan cewa; me ya sa suke daura aurensu a sirrance? Yayin da wasu ke ganin yin hakan a matsayin wata hanya ce da jaruman ke bi wajen kauce wa bakin mutane, wasu kuma na ganin wannan a matsayin wata hanya ta nuna girman kai ko isa da jaruman ke bi, domin nuna wa duniya cewa; su ba kamar sauran al’umma ba ne.
Koma dai mene ne, akwai bukatar jaruman su tuna cewa; suna da dimbin mutane da ke kiran kansu a matsayin masoyan jaruman, wanda ko babu komai dai, bai dace a ce masoyinka ba shi da labarin wani abin alherin da ya same ka ba, musamman harka ta aure, wadda ka iya zama silar daina fitowa a fina-finai ga jarumai mata da mazajensu, ba su amince su ci gaba da harkar fim ba.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA