Da muna kan mulki ni da Lamido da mun ƙalubalanci Tinubu — Amaechi
Published: 14th, May 2025 GMT
Tsohon Gwamnan Jihar Ribas, Rotimi Amaechi, ya bayyana cewa da shi da Sule Lamido har yanzu suna kan kujerar mulki, da sun fito ƙarara sun ƙalubalanci Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Amaechi ya bayyana haka ne a wajen ƙaddamar da littafin tarihin rayuwar Sule Lamido mai suna ‘Being True to Myself’ da aka gudanar a Abuja.
“Da mun fito da ƙarfinmu, mun ƙalubalanci gwamnati, mun kalubalanci shugaban ƙasa,” in ji Amaechi.
“Haka muka saba a lokacin muna Gwamnoni. Muna da kishin ƙasa da ƙwarin gwiwar sauya al’amura.”
Ya bayyana yadda dangantakar siyasar da ke tsakaninsa da Lamido, inda ya ce duk da kasancewar suna da alaƙa a wancan lokaci, sun raba gari ne lokacin da Lamido ya ƙi komawa jam’iyyar APC domin su haɗa ƙarfi wajen kayar da tsohon Shugaban Ƙasa Goodluck Jonathan.
“A lokacin, Lamido ya zaɓi kafa sabuwar jam’iyya – SDP, amma mu mun yarda cewa za mu fi samun nasara a jam’iyyar APC,” in ji Amaechi.
“Wannan ne ya sa hanyoyinmu suka rabu.”
Shugaba Tinubu, wanda Ministan Yaɗa Labarai, Mohammed Idris, ya wakilta a taron, ya ce shugaban ƙasa ya amince da mahawara mai ma’ana, amma hakan ba zai hana shi yi wa ƙasar nan abin da ya dace ba.
Tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo ma ya yi jawabi a wajen taron, inda ya bayyana Lamido a matsayin jagoran da ke da gaskiya da tsayawa kan aƙidarsa, inda ya ce lokacin da Lamido ke Ministan Harkokin Waje, ya taimaka wajen dawo da mutuncin Najeriya a idon duniya.
Obasanjo ya ce, “Sule ya taɓa faɗa, ‘Idan ka ga ban cancanta ba, ka ba ni minti biyar kawai na yi murabus. Amma ka da ka tambaye ni takardar murabus da ba ta da kwanan wata.’ Na girmama wannan matsayi nasa.”
Tsohon Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa, Farfesa Attahiru Jega, wanda ya wakilci Janar Abdulsalami Abubakar, ya jinjina wa littafin Lamido da cewa ya bayyana tarihin siyasar Najeriya da darusan da matasa za su amfana da su.
Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Dokta Iyorchia Ayu, wanda ya yi nazari a kan littafin, ya soki gwamnatin APC da cewa ta zama annoba ga Najeriya.
Ya buƙaci Lamido da ya ci gaba da rubuta littattafai domin su zama jagora ga ’yan Najeriya.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025
Ya ci gaba da cewa, Hukumar ta NPA, ta yi kasafin da dara haka, na wannan adadin, musaman ganin cewa, ta na burin, kara inganta ayyukanta, yadda za su yi dai-dai, da yadda ake gudanar da ayyukan, a sauran Tashoshin Jiragen Ruwa na duniya.
Shugaban Hukumar ya kuma sanar da cewa, a shekarar 2024, Hukumar ta NPA, kudin shigar da ta yi hasashen Tarawa daga na Naira biliyan 865.39, sun karu zuwa Naira biliyan 894.86.
“ Wannan ya nuna yadda Hukumar ta NPA, ta mayar da hankali da kuma kara zage Damtse wajen ganin ta Tarawa Gwamnatin Tarayya kudaden shiga, masu yawa,” A cewar Dantsoho.
Shugaban ya kuma bayyana cewa, kudaden shigar da Hukumar ke hasashen Tarawa a shekarar ta 2025, za ta samar da su ne, daga harajin da take karba daga gun Jiregen Ruwan da aka yo jigar kaya wanda ya kai Naira biliyan 544.06 da Naira biliyan 413.06 na Jiragen Ruwa da kuma wasu sauran kudade na Naira biliyan 249.69 sai kuma kudaden shiga, na sasehn gudnar da mulki, da suka kai Naira biliyan 73.07.
Shi kuwa a na sa jawabin, a zaman na Kwamitin, Shugaban Kwamitin Nnolim Nnaji, ya yi kira ga Hukumar ta NPA, da ta kara kaimi kan nasarorin da ta samar, tare da kuma kara inganta kayan da take gudanar da ayyukanta, musaman ta kuma bayar da gagarumar gudunmawa, wajen kara samar da hanyoyin ayyukan yi, ga ‘yan kasar nan.
Nnaji ya sanar da cewa, Hukumar ta NPA, ta kasance wata ginshike ce, wajen bayar da gagarumar gudunmawa na kara bunkasa tattalin arzikin kasar nan.
Shugaban ya kuma bukaci Hukumar da kara mayar da hankali, kan burukan da take son cimma duka manyan kalubalen da take fuskanta.
“Babu kata kasa a fadin duniya da za ta iya samar da wani ci gaba mai dorewa, ba tare da yin aiki, da sanarorin da Hukumar Jiragen Ruwa, ke samarwa ba,” Inji Shugaban.
Ya ci gaba da
“Hukumomin Jiragen Ruwa na kowacce kasa a fadin duniya, sune kashin bayan ci gaban tattalin arzikin kasa, musamman kan yadda ake gudanar da hada-hadar fitar da kaya da kuma shigar da su,” A cewar Nnaji.
Kazalika, Shugaban Kwamitin ya sanar da cewa, namijin kokarin da Hukumar ta NPA take kan yi, abin yabawa ne, kuma hakan, zai kara taimaka wa, wajen kara samar da ayyukan yi, a kasar nan.
“Hukumar ta NPA, ba wai kawai tana aikin tara kudaden shiga ba ne, ta kasance wata babbar kadara ce, wajen samar da ayyukan yi ga ‘yan Nijeriya da kuma kara habaka, tattalin arzikin kasar,” Inji Shugaban.
Nnaji ya bayyana cewa, wannan Kwamtin na jiran ya ga dabarun da Hukumar za ta yi amfani da su, musamman domin kara bunkasa kudaden shigar da kuma kara samar da damar ayyukan yi, ga ‘yan kasar nan, ta hanyar kasafin kudinta, na shekarar 2025.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp