’Yan ta’adda sun ƙwace makaman sojoji na tiriliyoyin naira —Majalisa
Published: 12th, May 2025 GMT
Ɗan Majalisar Wakilai, Honorabul Yusuf Gadgi, ya yi iƙirarin cewa mayaƙan Boko Haram sun ƙwace makaman sojoji da kuɗaɗensu ya kai tiriliyoyin naira a hare-haren da kungiyar ta kai kan sansanonin soji a yankin Arewa maso Gabas.
Gadgi ya bayyana haka ne a yayin da yake tsokaci kan ƙudirin da Honorabul Ahmed Satomi daga Jihar Borno ya gabatar a zauren Majalisar, kan gobarar da ta tashi a ma’ajiyar makamai ta rundunar soji da ke Barikin Sojoji na Giwa da ke Maiduguri da kuma ƙaruwar hare-haren Boko Haram a jihohin Borno da Yobe a baya-bayan nan.
Ɗan malisar ya ce yawan yadda ’yan ta’adda ke lalata kayan yaƙin sojoji a yanzu, ba a taɓa ganin irinsa ba a baya. Ya ƙara da cewa rashin ɗaukar mataki cikin gaggawa zai haifar da mummunan sakamako musamman ga zaɓaɓɓun shugabanni.
Ya ce, “Na firgita da abin da Boko Haram ta yi a Barikin Giwa da sauran cibiyoyin sojoji. Akwai abin damuwa game da tsaro da amincin ’yan Najeriya da ma ita kanta ƙasar.”
Yusuf Gadgi ya ce Majalisa ta ware wa sojoji kuɗaɗe a cikin kasafi domin sayen motocin yaƙi sama da 40 da sauran kayan yaƙi, da kuɗinsu ya kai tiriliyoyin naira, domin tsaron ’yan Najeriya.
Ya ce. “To yaya za mu samu tabbacin tsaron al’umma a irin wannan yanayi, idan ’yan ta’dda sun kwace waɗannan kayan yaƙi?”
Ya ci gaba da cewa “Majalisa tana yin iya bakin ƙoƙarinta wajen yin magana da kan sha’anin tsaro, amma wajibi ne hukumomin gwamnati su ɗauki mataka. Ya zama tilas shugaban ƙasa ya binciki shuagabannin sojoji da sauran hukumomin tsaro game da wannan sakacin, sannan ya ɗauki mataki a kansu.
“Sannan ya zama dole mu gayyaci hukumomin gwamnati domin su rika bayani a game da gazawarsu wajen gudanar da ayyukansu,” in Honorabul Yusuf Gadgi.
Ya bayyana cewa yawan halin ko-in-kula daga gwamnati da hukumomin tsaro zai haifar da rashin yardar al’umma da su, wanda hakan babbar barazana ce ga shugabannin siyasa.
Ya ce ya zama wajibi a ɗauki mataki, idan ba haka ba, “’yan Najeriya za su ɗauki matakan kare kansu da kansu, kuma za su yake mu kamar yadda za su yakar Boko Haram.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan ta adda Boko Haram kayan yaƙi Tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
Za A Yi Wa Masu Lalurar Ido Aiki Kyauta A Jihar Jigawa
Wata kungiya mai zaman kanta ta tantance mutane 60 wadanda za’a yiwa aikin ido kyauta a wasu kananan hukumomi 2 dake jihar Jigawa.
Shugaban kungiyar mai zaman kanta, Alhaji Umar Saidu Yelleman Jambola ya bayyana cewar za’a gudanar da aikin ne kyauta ga mutane 60 a kananan hukumomin Malam madori da kaugama.
A cewar sa wadanda za su ci moriyar aikin an zabi su ne daga dukkanin mazabu da ke kananan hukumomin.
Sa’idu Yalleman ya kara da cewa yara da manya ne za su amfana da aikin idon kyauta wanda kungiyar ta dau nauyi.
Da yake jawabi ga manema labarai, Dr Abubakar Adamu yace wadanda aka tantance kuma suke da yanar ido za’a kai su asibitin koyarwa na Malam Aminu Kano dake birnin Kano don yi masu aikin.
Wakilan shirin na kananan hukumomin Malam Madori and Kaugama, Malam Bashari Suleiman da Dan-Alhaji sun ce a mako mai zuwa ne za’a gudanar da aikin ga wadanda aka tantance.
Da yake jawabi a madadin wadanda zasu ci moriyar aikin, wakilan mazabun Garun-Gabas da Mairakumi, Mustapha Bala da Suraja Garba sun yabawa kokarin Alhaji Umar Jambola.
A nasu jawaban, Shugabannin kananan hukumomin Kaugama da Malam madori, Alhaji Salisu Sani Garun-Gabas da Alhaji Masaki Usman Dansule sun yaba da hobbasan Umar Jambola na taimakawa masu karamin karfi a kananan hukumominsu.
Usman Mohammed Zaria