’Yan ta’adda sun ƙwace makaman sojoji na tiriliyoyin naira —Majalisa
Published: 12th, May 2025 GMT
Ɗan Majalisar Wakilai, Honorabul Yusuf Gadgi, ya yi iƙirarin cewa mayaƙan Boko Haram sun ƙwace makaman sojoji da kuɗaɗensu ya kai tiriliyoyin naira a hare-haren da kungiyar ta kai kan sansanonin soji a yankin Arewa maso Gabas.
Gadgi ya bayyana haka ne a yayin da yake tsokaci kan ƙudirin da Honorabul Ahmed Satomi daga Jihar Borno ya gabatar a zauren Majalisar, kan gobarar da ta tashi a ma’ajiyar makamai ta rundunar soji da ke Barikin Sojoji na Giwa da ke Maiduguri da kuma ƙaruwar hare-haren Boko Haram a jihohin Borno da Yobe a baya-bayan nan.
Ɗan malisar ya ce yawan yadda ’yan ta’adda ke lalata kayan yaƙin sojoji a yanzu, ba a taɓa ganin irinsa ba a baya. Ya ƙara da cewa rashin ɗaukar mataki cikin gaggawa zai haifar da mummunan sakamako musamman ga zaɓaɓɓun shugabanni.
Ya ce, “Na firgita da abin da Boko Haram ta yi a Barikin Giwa da sauran cibiyoyin sojoji. Akwai abin damuwa game da tsaro da amincin ’yan Najeriya da ma ita kanta ƙasar.”
Yusuf Gadgi ya ce Majalisa ta ware wa sojoji kuɗaɗe a cikin kasafi domin sayen motocin yaƙi sama da 40 da sauran kayan yaƙi, da kuɗinsu ya kai tiriliyoyin naira, domin tsaron ’yan Najeriya.
Ya ce. “To yaya za mu samu tabbacin tsaron al’umma a irin wannan yanayi, idan ’yan ta’dda sun kwace waɗannan kayan yaƙi?”
Ya ci gaba da cewa “Majalisa tana yin iya bakin ƙoƙarinta wajen yin magana da kan sha’anin tsaro, amma wajibi ne hukumomin gwamnati su ɗauki mataka. Ya zama tilas shugaban ƙasa ya binciki shuagabannin sojoji da sauran hukumomin tsaro game da wannan sakacin, sannan ya ɗauki mataki a kansu.
“Sannan ya zama dole mu gayyaci hukumomin gwamnati domin su rika bayani a game da gazawarsu wajen gudanar da ayyukansu,” in Honorabul Yusuf Gadgi.
Ya bayyana cewa yawan halin ko-in-kula daga gwamnati da hukumomin tsaro zai haifar da rashin yardar al’umma da su, wanda hakan babbar barazana ce ga shugabannin siyasa.
Ya ce ya zama wajibi a ɗauki mataki, idan ba haka ba, “’yan Najeriya za su ɗauki matakan kare kansu da kansu, kuma za su yake mu kamar yadda za su yakar Boko Haram.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan ta adda Boko Haram kayan yaƙi Tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
Juyin mulki ya rutsa da Jonathan a Guinea-Bissau
Tsohon Shugaban Ƙasa, Goodluck Jonathan, ya maƙale a Guinea-Bissau bayan da sojoji suka yi juyin mulki tare da karɓe ragamar mulkin ƙasar.
Jonathan da sauran baƙi baƙi masu sanya ido kan zaɓen da aka gudanar, ba za su iya barin ƙasar ba domin sojoji sun rufe iyakokin ƙasar baki ɗaya, tare da dakatar da zaɓen gaba ɗaya.
Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban Amurka Andrea Thompson ta zama mace mafi ƙarfi a duniyaLamarin ya samo asali ne bayan manyan ’yan takara biyu sun yi iƙirarin samun nasara a zaɓen shugaban ƙasa da ya gudana.
Ba jimawa wasu dakarun sojin ƙasar suka hamɓarar da gwamnatin farar hula ta ƙasar.
Sun kuma sanar da dokar hana fita da kuma kama manyan jami’an da ke da alaƙa da zaɓen.
“An hamɓarar da gwamnatina,” in ji Shugaba Umaro Sissoco Embalo cikin wata tattaunawa ta waya da gidan talabijin na ƙasashen waje.
Jonathan ya je Guinea-Bissau ne a matsayin shugaban tawagar West African Elders Forum (WAEF) domin sanya ido kan zaɓen.
Ya ziyarci wasu rumfunan zaɓe a ƙasar kuma ya wallafa bayanai a kafafen sada zumunta kafin juyin mulkin.
Mutanen da ke tare da shi sun ce yana cikin ƙoshin lafiya, amma ba shi da damar barin ƙasar.
Sojojin suna kuma ƙoƙarin katse Intanet, lamarin da ya sa ake samun tangarɗa wajen sadarwa a ƙasar.
Hakan ya sa ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa suka fara nuna damuwa kan tsaron manyan ’yan siyasa da jami’an zaɓe.
A cikin wata sanarwa, Jonathan da wasu shugabannin Afirka sun yi Allah-wadai da juyin mulkin.
“Mun yi Allah-wadai da wannan yunƙuri na daƙile tsarin dimokuraɗiyya, kuma muna kira ga Tarayyar Afirka da ECOWAS su ɗauki matakin dawo da tsarin mulki,” in ji su.
Sun buƙaci mutanen Guinea-Bissau su kwantar da hankalinsu, tare da kira ga sojoji su saki dukkanin jami’an da suka kama domin a ci gaba da gudanar da zaɓe cikin lumana.