Pakisatan Ta Maida Martanin Farmakin Sindoor Na Indiya Kan Rumbun Makamai Masu Linzami Na Indiya
Published: 10th, May 2025 GMT
Gwamnatin kasar Pakisatan ta basa sanarwan kai hare-haren maida martani kan kasar Indiya, inda tayi amfani da makamai masu linzami wadanda suka fada kan rumbun ajiyar makaman kasar ta Indiya da wani filin tashin jiragen.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto majiyar sojojin kasar Nacewa daga wadannan wurare biyu ne makaman kasar Indiya suka tashi suka kuma yi sanadiyyar kashe mutane fararen hula a cikin kasar Pakisatan a makon da ya gabata.
Labarin ya kara da cewa sojojin Pakisatan sun bawa wannan farmakin maida martani suna [Bunyanun Marsus) inda suka dauki aron Kalmar daga wata ayar al-kur’ani mai girma.
Hare-haren maida martanin sun auku ne a safiyar yau Asabar, don haka har yanzun bamu ta bakin kasar Indiya ba.
Yaki a tsakanin kasashen biyu ya soma ne daga ranar 22 ga watan Afrilun da ya gabata, inda kasar Indiya ta zargi Pakistan da hannu a cikin hare-haren da wasu yan ta’adda suka kai a yankin Pahalgam na yankin Kashmir da ke karkashin ikon kasar Indiya inda mutane 26 masu yawan shakatawa ko bude ido suka rasa rayukansu.
Ba tare da bata lokaci ba sojojin kasar Indiya suka fara cilla makamai kan kasar Pakistan, daga ciki har da farmakin da ta kira “sindoor”.
Da farko kasar Pakisatan ta musanta zargin ta kuma yi allawadai da hare-haren na ta’addanci a cikin kasar Indiya. Sai dai tunda kasar Indiya bata saurareta ba, bata da zabi in banda maida martani a safiyar yau Asabar.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Indiya
এছাড়াও পড়ুন:
Sabuwar Shugabar Kwamitin Wasannin Olympics Na Duniya Na Fatan Sake Ziyartar Kasar Sin
A ranar 23 ga wata, Kirsty Coventry, wacce ta karbi ragamar shugabancin kwamitin wasannin Olympics ta kasa da kasa kwanan nan, ta yi hira ta musamman da wani shirin gidan talabijin na CCTV mai lakabin “High-End Interview” a birnin Lausanne na kasar Switzerland. Wannan ita ce hira ta farko da ta yi da kafar yada labarai tun bayan da ta karbi ragamar shugabancin kwamitin wasannin Olympics na duniya.
Coventry ta ce ya zama wajibi a kiyaye kima da kuzarin wasannin motsa jiki na Olympics, tare da kara kiyaye su da kuma karfafa su. Ta ce, tana fatan yin mu’amala mai zurfi da dukkan masu ruwa da tsaki a watanni masu zuwa, tare da haduwa tare wajen tsara fasalin aiki na nan gaba da kuma yin aiki tare don tabbatar da yiwuwarsa a zahiri.
A halin da ake ciki kuma, ta ce, tana matukar fatan sake ziyartar kasar Sin nan da wasu watanni masu zuwa. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp