Gwamnatin kasar Pakisatan ta basa sanarwan kai hare-haren maida martani kan kasar Indiya, inda tayi amfani da makamai masu linzami wadanda suka fada kan rumbun ajiyar makaman kasar ta Indiya da wani filin tashin jiragen.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto majiyar sojojin kasar Nacewa daga wadannan wurare biyu ne makaman kasar Indiya suka tashi suka kuma yi sanadiyyar kashe mutane fararen hula a cikin kasar Pakisatan a makon da ya gabata.

Labarin ya kara da cewa sojojin Pakisatan sun bawa wannan farmakin maida martani suna [Bunyanun Marsus) inda suka dauki aron Kalmar daga wata ayar al-kur’ani mai girma.

Hare-haren maida martanin sun auku ne a safiyar yau Asabar, don haka har yanzun bamu ta bakin kasar Indiya ba.

Yaki a tsakanin kasashen biyu ya soma ne daga ranar 22 ga watan Afrilun da ya gabata, inda kasar Indiya ta zargi Pakistan da hannu a cikin hare-haren da wasu yan ta’adda suka kai a yankin Pahalgam na yankin Kashmir da ke karkashin ikon kasar Indiya inda mutane 26 masu yawan shakatawa ko bude ido suka rasa rayukansu.

Ba tare da bata lokaci ba sojojin kasar Indiya suka fara cilla makamai kan kasar Pakistan, daga ciki har da farmakin da ta kira “sindoor”.

Da farko kasar Pakisatan ta musanta zargin ta kuma yi allawadai da hare-haren na ta’addanci a cikin kasar Indiya. Sai dai tunda kasar Indiya bata saurareta ba, bata da zabi in banda maida martani a safiyar yau Asabar.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Indiya

এছাড়াও পড়ুন:

An kashe manomi da dabbobi 39 a Bauchi

Wani rikici da ya ɓarke ya yi sanadin mutuwar wani manomi mai suna Irmiya Yohanna, mai shekara 40, tare da hallaka shanu da tumaki 39, a ƙauyen Kaduna da ke Ƙaramar Hukumar Bogoro, a Jihar Bauchi.

Haka kuma  ’yan sanda sun ceto shanu 249 da aka yi ƙoƙarin kashewa.

Obi ya ziyarci Bauchi, ya ba da tallafin N15m don inganta ilimi PDP ta gargaɗi ’ya’yanta kan goyon bayan Tinubu a zaɓen 2027

Kakakin ’yan sandan jihar, CSP Ahmed Mohammed Wakil, ya bayyana cewa, a ranar 7 ga watan Agusta 2025, Irmiya ya tafi gonarsa amma bai dawo gida ba.

Bayan yin bincike, aka gano gawarsa a kwance a gonarsa.

Bayan samun rahoto daga Sarkin ƙauyen, Emmanuel Bulus, ’yan sanda ƙarƙashin jagorancin DPO SP Fitoka Golda sun wajen domin yin bincike.

Sun ɗauki gawar zuwa Babban Asibitin Bogoro, inda likita ya tabbatar da mutuwarsa.

Bincike, ya nuna cewa wasu da ba a san ko su wane ne ba suka kashe shi.

Daga baya, wasu fusatattu a yankin suka kai wa dabbobin Fulani hari a kusa da ƙauyen, inda suka kashe shanu 20 da tumaki 19, sannan suka jikkata wasu.

Sai dai rundunar ta kama wani mutum mai suna Ahmadu Mairiga da ake zargi da hannu a kisan.

Rahoton ’yan sanda ya ce rikicin ya fara ne lokacin da Irmiya ya tarar da shanu suna cin amfanin gonarsa.

Ya nemi makiyayan su fitar da su, sai faɗa ta kaure a tsakaninsu wanda hakan ya kai ga mutuwarsa.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Sani-Omolori Aliyu, ya kai ziyara yankin, inda ya gana da shugabannin Fulani, sarakuna da shugabannin al’umma.

Ya gargaɗi mazauna yankin da su guji tashin hankali tare da tabbatar da cewa za su ɗauki matakan tsaro don kawo zaman lafiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya
  • An kashe manomi da dabbobi 39 a Bauchi
  • Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta, Sun Kashe Ƴan Ta’adda A Borno
  • Zamfarawa sun yi zanga-zanga kan hare-haren ’yan bindiga
  • Manjo Janar Mousawi: Martanin Iran Nan Gaba Zai Kasance Mafi Muni Kan Makiya  
  • Hare-Haren Sojojin Mamayar Isra’ila Kan Gaza Sun Janyo Shahadan Falasdinawa Masu Yawa
  • Nijeriya Da Indiya Za Su Haɗa Kai Wajen Yaƙi Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi
  • Ana zargin ‘yan sanda da karya hannun Sowore
  • Jamus: Shahararrun mutane fiye da 160 da ‘yan jarida sun bukaci a daina baiwa Israila makamai
  • Gaza: Fararen hula 22 sun yi shahada a hare-haren Isra’ila a daren jiya