Aminiya:
2025-08-11@20:51:09 GMT

’Yan bindiga sun yi awon gaba da mutum 5 a Filato

Published: 12th, May 2025 GMT

Wasu ’yan bindiga sun yi awon gaba da mutane biyar yayin da suka kai hari ana tsaka da cin kasuwa a ƙauyen Dogon Ruwa da ke Ƙaramar Hukumar Wase ta Jihar Filato.

A cewar mazauna, maharan sun wawushe kayayyaki a shaguna inda suka yi awon gaba da kayan abinci da magunguna masu tarin yawa.

Jami’ar Maryam Abacha ta rufe ɗakunan kwanan ɗalibai a Kano Awakin da ke rayuwa sama da shekaru 200 a inda babu ruwa

Aminiya ta ruwaito cewa ’yan bindigar sun kai hari kan kasuwar ce mai tara ɗaruruwan mutane da ke zuwa daga gari-gari makwabtaka domin baza hajoji iri-iri musamman kayan abinci da suka haɗa da shinkafa, fulawa, wake, lemuka da sauransu.

Shafi’i Sambo, wani shugaban matasa a yankin, ya shaida wa Aminiya cewa ’yan bindigar sun kai farmakin da misalin ƙarfe 11 na safe haye a kan babura — inda suka fara harbe-harbe kan mai uwa wabi.

Sai dai ya ce daga bisani jami’an tsaro da suka da sojoji da ’yan sa-kai sun kawo ɗauki tare da bin sawun ɓata-garin da suka kawo farmakin.

Aminiya ta yi ƙoƙarin jin ta bakin kakakin rundunar Operation Safe Haven, Manjo Samson Zhakom, amma lamarin ya ci tura har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Jihar Filato kasuwa

এছাড়াও পড়ুন:

Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara

Kakakin NAF ya ce harin, an kai ne tare da hadin gwiwar runduna ta kasa, wanda ya yi sanadin mutuwar wasu fitattun ‘yan bindiga rundunarsu da dama.

 

Daraktan ya kuma jadadda cewa hadin kai tsakanin sassan sama da na kasa na Operation Fasan Yamma ya sa farmakin ya zama na musamman.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara
  • ‘Yan Ta’addar ISWAP Sun Kashe Shugaban Mafarauta A Borno
  • An kashe mutum 24 an sace 144 a mako guda a Zamfara — Rahoto
  • ‘Yan Sandan Nasarawa Sun Kama Mutum Shida Da Laifin Fashi Da Makami Da Garkuwa Da Mutane
  • Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara
  • Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas
  • ’Yan bindiga sun kashe gomman mutane a ƙauyukan Sakkwato
  • Ana Zanga-Zanga A Isra’ila Kan Shirin Netanyahu Na Mamaye Gaza
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi
  • Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza