Aminiya:
2025-06-27@05:53:36 GMT

’Yan bindiga sun yi awon gaba da mutum 5 a Filato

Published: 12th, May 2025 GMT

Wasu ’yan bindiga sun yi awon gaba da mutane biyar yayin da suka kai hari ana tsaka da cin kasuwa a ƙauyen Dogon Ruwa da ke Ƙaramar Hukumar Wase ta Jihar Filato.

A cewar mazauna, maharan sun wawushe kayayyaki a shaguna inda suka yi awon gaba da kayan abinci da magunguna masu tarin yawa.

Jami’ar Maryam Abacha ta rufe ɗakunan kwanan ɗalibai a Kano Awakin da ke rayuwa sama da shekaru 200 a inda babu ruwa

Aminiya ta ruwaito cewa ’yan bindigar sun kai hari kan kasuwar ce mai tara ɗaruruwan mutane da ke zuwa daga gari-gari makwabtaka domin baza hajoji iri-iri musamman kayan abinci da suka haɗa da shinkafa, fulawa, wake, lemuka da sauransu.

Shafi’i Sambo, wani shugaban matasa a yankin, ya shaida wa Aminiya cewa ’yan bindigar sun kai farmakin da misalin ƙarfe 11 na safe haye a kan babura — inda suka fara harbe-harbe kan mai uwa wabi.

Sai dai ya ce daga bisani jami’an tsaro da suka da sojoji da ’yan sa-kai sun kawo ɗauki tare da bin sawun ɓata-garin da suka kawo farmakin.

Aminiya ta yi ƙoƙarin jin ta bakin kakakin rundunar Operation Safe Haven, Manjo Samson Zhakom, amma lamarin ya ci tura har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Jihar Filato kasuwa

এছাড়াও পড়ুন:

Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja

Majiyoyi sun kuma ce “an kashe adadi mai yawa na ‘yan bindigar”.

 

Shugaban karamar hukumar, Abbas Adamu Kasuwan-Garba, ya ce harin ya kara firgitar da manoman yankin.

 

Ya ce taimakon gaggawa daga barikin soji na Kontagora ya tilastawa ‘yan bindigar tserewa zuwa dazuka.

 

Ya kuma ce ‘yan bindigar sun yi awon gaba da shanu, sun farfasa shaguna tare da kwashe kayan abinci da kayayyaki masu daraja a shagunan mutanen yankin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ronaldo ya tsawaita kwantaraginsa a Al Nassr
  • Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya
  • Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina
  • Yadda na kuɓuta daga harin Filato — Wani mutum
  • Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja
  • ’Yan bindiga sun kashe ɗan sanda, sun jikkata wasu 3 a Zariya
  • Isra’ila da Iran sun ci gaba da musayar wuta duk da sanarwar tsagaita wuta
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara
  • Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato
  • An Cafke Mutum 22 Kan Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato – Uba Sani