Aminiya:
2025-11-27@23:00:46 GMT

’Yan bindiga sun yi awon gaba da mutum 5 a Filato

Published: 12th, May 2025 GMT

Wasu ’yan bindiga sun yi awon gaba da mutane biyar yayin da suka kai hari ana tsaka da cin kasuwa a ƙauyen Dogon Ruwa da ke Ƙaramar Hukumar Wase ta Jihar Filato.

A cewar mazauna, maharan sun wawushe kayayyaki a shaguna inda suka yi awon gaba da kayan abinci da magunguna masu tarin yawa.

Jami’ar Maryam Abacha ta rufe ɗakunan kwanan ɗalibai a Kano Awakin da ke rayuwa sama da shekaru 200 a inda babu ruwa

Aminiya ta ruwaito cewa ’yan bindigar sun kai hari kan kasuwar ce mai tara ɗaruruwan mutane da ke zuwa daga gari-gari makwabtaka domin baza hajoji iri-iri musamman kayan abinci da suka haɗa da shinkafa, fulawa, wake, lemuka da sauransu.

Shafi’i Sambo, wani shugaban matasa a yankin, ya shaida wa Aminiya cewa ’yan bindigar sun kai farmakin da misalin ƙarfe 11 na safe haye a kan babura — inda suka fara harbe-harbe kan mai uwa wabi.

Sai dai ya ce daga bisani jami’an tsaro da suka da sojoji da ’yan sa-kai sun kawo ɗauki tare da bin sawun ɓata-garin da suka kawo farmakin.

Aminiya ta yi ƙoƙarin jin ta bakin kakakin rundunar Operation Safe Haven, Manjo Samson Zhakom, amma lamarin ya ci tura har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Jihar Filato kasuwa

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun yi yi garkuwa da mutane 11 a Kwara

’Yan bindiga sun yi garkuwa da mutane 11, ciki har da wat mai juna biyu da ƙananan yara Jihar Kwara.

Maharan sun kai farmaki tare da sace mutanen ne a yankin Eruku da ke Ƙaramar Hukumar Ekiti da ke jihar.

Ƙarin bayani na tafe…

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban Amurka
  • Ko sisi ba a biya ’yan bindiga ba kafin su saki ɗaliban da suka sace – Gwamnan Kebbi
  • Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Oyo saboda aikata kisan kai
  • ’Yan bindiga sun sake kai hari a Kwara, sun sace mutum 11
  • Kano Pillars ta kawo ƙarshen wasanni 8 ba tare da nasara ba
  • An sako ɗalibai 25 da ’yan bindiga suka sace a Kebbi
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 8 a Kano
  • ’Yan bindiga sun yi yi garkuwa da mutane 11 a Kwara
  • Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina
  • Gobarar tankar mai ta ƙone gidaje a Jihar Neja