Matakan da gwamnonin Arewa suke so a ɗauka kan matsalar tsaron yankin
Published: 11th, May 2025 GMT
Gwamnoni da kuma Sarakunan gargajiya na Arewacin Nijeriya sun gudanar da taro a Kaduna, domin tattaunawa kan matsalolin rashin tsaro da suka addabi yankin.
Taron wanda ya gudana ne a gidan gwamnatin jihar ta Kaduna, inda suka tattauna kan matsalar talauci da yaran da ba su zuwa makaranta da kuma sauran al’amura da suke damun yankin.
Gwamnonin jihohin Katsina da Zamfara da Kebbi da Gombe da Neja da Filato da Yobe da Jigawa da Kogi da Adamawa da kuma Zamfara na cikin waɗanda suka halarci taron.
A ɓangaren sarakunan gargajiya kuma akwai mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III da Sarkin Zazzau, Ahmed Bamalli da Etsu na Nupe da Sarkin Zamfara da Sarkin Bauchi da Sarkin Ilorin da Sarkin Keffi da sauransu.
Gwamnonin sun yaba wa ƙoƙarin Shugaban Najeriya Bola Tinubu na magance matsalar tsaro a faɗin ƙasar, sai dai sun buƙaci tana a ƙara ƙaimi domin a cewarsu an fara mayar da hannun agogo baya.
Gwamnonin sun ce yadda Boko Haram ke ƙoƙarin dawo da ayyukanta a wasu sassan Arewa maso Gabas, da kashe-kashe a Arewa ta Tsakiya ne ya sa suke kira da a yi garambawul a ɓangaren tsaro.
Da wannan ne Ƙungiyar Gwamnonin Arewa ta yi kira da a ƙara samun haɗin kai tsakanin jami’an tsaron gwamnatin tarayya da na jihohi da ƴan sa-kai.
Shugaban ƙungiyar, Gwamnan Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya ne ya bayyana hakan a sanarwar bayan taron da aka yi ranar Asabar a Kaduna.
“Ƙungiyar za ta haɗa ƙarfi da ƙarfe da Ƙungiyar Gwamnonin Nijeriya domin samar da hanyoyin taimakon jami’an tsaron gwamnatin tarayya wajen magance matsalar da ƙasar ke fuskanta,” in ji shi.
Sannan ya ce ƙungiyar za ta kafa kwamitin haɗin gwiwa domin samar da tsarin bai-ɗaya na tsaro domin sa ido kan tsaron iyakokin jihohi.
Haka kuma ƙungiyar ta sake nanata goyon bayan da kafa ’yan sandan jiha, inda gwamnonin suka yi kira ga majalisar ƙasar da ta gaggauta ɗaukar matakin yin doka domin tabbatar da ƙirƙirar ƴansandan na jiha.
Ga wasu abubuwa 5 da Gwamnonin Arewa suka tattauna a taron:
1. Kungiyar ta yaba wa shugaba Bola Tinubu kan kokarin da yake a fannin samar da tsaro a Arewa.
2. Kungiyar za ta haɗa kai da kungiyar Gwamnonin Nijeriya domin karfafa fannin tsaro a yankin.
3. Kungiyar za ta ɓullo da tsarin inganta tsaro a yankin tun daga tushe.
4. Kungiyar ta buƙaci a yi gaggawar ɗaukar matakan samar da tsaro a iyakokin jihohin yankin.
5. Kungiyar ta jaddada goyon bayanta kan samar da ‘yan sandan jihohi, inda ta buƙaci Majalisar Tarayya ta tabbatar da hakan.
Ƙungiyar ta ce za su sake zama a ranar 30 ga watan Agustan 2025.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Arewa Gwamnonin Arewa Jihar Kaduna matsalar tsaro Muhammad Inuwa Yahaya Gwamnonin Arewa da Gwamnonin
এছাড়াও পড়ুন:
Tabarbarewar Tsaro na Barazana ga Siyasar Ƙasar Nan Gabanin Zaɓen 2027-Ado Doguwa
Daga Salihu Tsibiri
Tsohon shugaban masu rinjaye na Majalisar Wakilai, Alhassan Ado Doguwa, ya bayyana tabarbarewar tsaro da ake fuskanta, wato ta’addanci, garkuwa da mutane da kuma hare-haren ’yan bindiga, a matsayin barazana ga siyasar ƙasar nan gabanin zaɓen 2027.
Ya yi wannan tsokacin ne a jawabinsa yayin bude zaman taron musamman na yini biyu da Majalisar Wakilai ta shirya kan halin tsaro da ƙasar ke ciki.
Alhassan Ado Doguwa, wanda ya yaba da ayyukan da hukumomin tsaro ke ci gaba da gudanarwa, ya ce halin da Arewa ke ciki abin takaici ne ƙwarai, la’akari da yawan mutanen da ke hannun masu garkuwa da kuma waɗanda ke rayuwa cikin tsananin rashin tabbas.
Tsohon shugaban ya jaddada cewa duk da cewa su ma gwamnoni suna da alhakin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a tare da gwamnatin tarayya, lokaci ya yi da za a duba batun tsaro a matsayin barazana da ba ta da alaƙa da jam’iyya, addini ko ƙabila.
Ya kara da cewa idan matsalar tsaro ta ci gaba da ta’azzara, akwai bukatar a rufe majalisa gaba ɗaya tare da ayyana dokar ta-baci, har sai an ɗauki matakin gaggawa don kare ƙasar daga halin da take ciki.
A nasa bangaren, shugaban kwamitin majalisar kan harkokin ’yan sanda, Makki Abubakar Yalleman, ya bayyana tsaro a matsayin alhakin kowa, inda ya yaba wa umarnin shugaban ƙasa na janye ’yan sanda daga wasu manyan mutane domin ƙara ƙarfi a yaki da laifuka a fadin ƙasar.
Sai dai Makki Yalleman ya yi kira da a samar da isasshen kuɗi da na’urorin zamani domin inganta ƙwarin gwiwa da ƙwarewar rundunar ’yan sandan Najeriya a yakin da take yi da ta’addanci, garkuwa da mutane da kuma ’yan bindiga.
A nasa bangaren, shugaban marasa rinjaye na majalisar, Kingsley Chinda, ya danganta matsalolin tsaro da ake fuskanta ga gazawar bangarorin gwamnati uku wajen tabbatar da bin tanade-tanaden kundin tsarin mulki, musamman kan ta’addanci, garkuwa da mutane, ’yan bindiga da kuma masu yi wa gwamnati tawaye.