Aminiya:
2025-06-26@22:45:49 GMT

Matakan da gwamnonin Arewa suke so a ɗauka kan matsalar tsaron yankin

Published: 11th, May 2025 GMT

Gwamnoni da kuma Sarakunan gargajiya na Arewacin Nijeriya sun gudanar da taro a Kaduna, domin tattaunawa kan matsalolin rashin tsaro da suka addabi yankin.

Taron wanda ya gudana ne a gidan gwamnatin jihar ta Kaduna, inda suka tattauna kan matsalar talauci da yaran da ba su zuwa makaranta da kuma sauran al’amura da suke damun yankin.

An kama matashi da kawunan mutanen a Legas Indiya da Pakistan sun cimma yarjejeniyar tsagaita wuta

Gwamnonin jihohin Katsina da Zamfara da Kebbi da Gombe da Neja da Filato da Yobe da Jigawa da Kogi da Adamawa da kuma Zamfara na cikin waɗanda suka halarci taron.

A ɓangaren sarakunan gargajiya kuma akwai mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III da Sarkin Zazzau, Ahmed Bamalli da Etsu na Nupe da Sarkin Zamfara da Sarkin Bauchi da Sarkin Ilorin da Sarkin Keffi da sauransu.

Sarakunan gargajiya da gwamnonin Arewa da suka halarci taron

Gwamnonin sun yaba wa ƙoƙarin Shugaban Najeriya Bola Tinubu na magance matsalar tsaro a faɗin ƙasar, sai dai sun buƙaci tana a ƙara ƙaimi domin a cewarsu an fara mayar da hannun agogo baya.

Gwamnonin sun ce yadda Boko Haram ke ƙoƙarin dawo da ayyukanta a wasu sassan Arewa maso Gabas, da kashe-kashe a Arewa ta Tsakiya ne ya sa suke kira da a yi garambawul a ɓangaren tsaro.

Da wannan ne Ƙungiyar Gwamnonin Arewa ta yi kira da a ƙara samun haɗin kai tsakanin jami’an tsaron gwamnatin tarayya da na jihohi da ƴan sa-kai.

Shugaban ƙungiyar, Gwamnan Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya ne ya bayyana hakan a sanarwar bayan taron da aka yi ranar Asabar a Kaduna.

“Ƙungiyar za ta haɗa ƙarfi da ƙarfe da Ƙungiyar Gwamnonin Nijeriya domin samar da hanyoyin taimakon jami’an tsaron gwamnatin tarayya wajen magance matsalar da ƙasar ke fuskanta,” in ji shi.

Sannan ya ce ƙungiyar za ta kafa kwamitin haɗin gwiwa domin samar da tsarin bai-ɗaya na tsaro domin sa ido kan tsaron iyakokin jihohi.

Haka kuma ƙungiyar ta sake nanata goyon bayan da kafa ’yan sandan jiha, inda gwamnonin suka yi kira ga majalisar ƙasar da ta gaggauta ɗaukar matakin yin doka domin tabbatar da ƙirƙirar ƴansandan na jiha.

Ga wasu abubuwa 5 da Gwamnonin Arewa suka tattauna a taron:

1. Kungiyar ta yaba wa shugaba Bola Tinubu kan kokarin da yake a fannin samar da tsaro a Arewa.

2. ⁠Kungiyar za ta haɗa kai da kungiyar Gwamnonin Nijeriya domin karfafa fannin tsaro a yankin.

3. ⁠Kungiyar za ta ɓullo da tsarin inganta tsaro a yankin tun daga tushe.

4. ⁠Kungiyar ta buƙaci a yi gaggawar ɗaukar matakan samar da tsaro a iyakokin jihohin yankin.

5. ⁠Kungiyar ta jaddada goyon bayanta kan samar da ‘yan sandan jihohi, inda ta buƙaci Majalisar Tarayya ta tabbatar da hakan.

Ƙungiyar ta ce za su sake zama a ranar 30 ga watan Agustan 2025.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Arewa Gwamnonin Arewa Jihar Kaduna matsalar tsaro Muhammad Inuwa Yahaya Gwamnonin Arewa da Gwamnonin

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun kashe ɗan sanda, sun jikkata wasu 3 a Zariya

Wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun kai wa motar ’yan sanda hari a Zariya, inda suka harbe ɗaya daga cikinsu har lahira, tare da raunata wasu uku.

Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 10:30 na daren ranar Talata, a unguwar Dalan Waje da ke kan hanyar Galadimawa, a Ƙaramar Hukumar Zariya da ke Jihar Kaduna.

An ɗaure mutum 6 shekaru 120 kan satar yara a Kano Isra’ila da Iran sun ci gaba da musayar wuta duk da sanarwar tsagaita wuta

A cewar wani mazaunin yankin da ya shaida faruwar lamarin, motar ‘yan sandan na bin wata mota ƙirar Golf kafin a ji ƙarar harbe-harbe.

Nan take mutane suka fara kwanciya a ƙasa domin tsira da rayukansu.

Wannan hari ya girgiza mazauna yankin, inda suka ce ko da yake yankin ya daɗe yana fama da hare-haren ’yan bindiga, amma an daɗe ba samu hari ba.

A harin, an kashe wani ɗan sanda mai suna Nasiru Musa.

Ɗan sandan mazaunin ƙofar Kibo ne a cikin birnin Zariya.

Sauran da suka jikkata sun haɗa da direban motar ’yan sandan, Auwalu Hassan Ɗan Jos, wani ɗan-sa-kai mai suna Awwal Hassan, Iliyasu Ya’u da Salisu Mohammed.

An garzaya da su zuwa Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ahmadu Bello da ke Shika, Zariya, domin samun kulawar likitoci.

Da Aminiya ta tuntuɓi kakakin ’yan sandan Jihar Kaduna, DSP Mansur Hassan, ya ce yana wajen wani taron sanin makamar aiki, don haka bai da cikakken bayani.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Katsina ta amince da ƙidayar almajirai, makarantun Islamiyya
  • Gwamnatin Katsina ta amince da ƙidayar almajirai da makarantun Islamiyya
  • Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga
  • Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr
  • DHQ Za Ta Tura Dakaru Na Musamman 800 Yankunan Da Ke Fama Da Rashin Tsaro – CDS
  • Nazarin CGTN: Neman Kashe Kaso 5 Na GDP Kan Tsaro Ya Nuna Rashin Dabara Na NATO
  • ’Yan bindiga sun kashe ɗan sanda, sun jikkata wasu 3 a Zariya
  • Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida
  • Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?
  • Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Muharram