Aminiya:
2025-05-12@03:36:12 GMT

Matakan da gwamnonin Arewa suke so a ɗauka kan matsalar tsaron yankin

Published: 11th, May 2025 GMT

Gwamnoni da kuma Sarakunan gargajiya na Arewacin Nijeriya sun gudanar da taro a Kaduna, domin tattaunawa kan matsalolin rashin tsaro da suka addabi yankin.

Taron wanda ya gudana ne a gidan gwamnatin jihar ta Kaduna, inda suka tattauna kan matsalar talauci da yaran da ba su zuwa makaranta da kuma sauran al’amura da suke damun yankin.

An kama matashi da kawunan mutanen a Legas Indiya da Pakistan sun cimma yarjejeniyar tsagaita wuta

Gwamnonin jihohin Katsina da Zamfara da Kebbi da Gombe da Neja da Filato da Yobe da Jigawa da Kogi da Adamawa da kuma Zamfara na cikin waɗanda suka halarci taron.

A ɓangaren sarakunan gargajiya kuma akwai mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III da Sarkin Zazzau, Ahmed Bamalli da Etsu na Nupe da Sarkin Zamfara da Sarkin Bauchi da Sarkin Ilorin da Sarkin Keffi da sauransu.

Sarakunan gargajiya da gwamnonin Arewa da suka halarci taron

Gwamnonin sun yaba wa ƙoƙarin Shugaban Najeriya Bola Tinubu na magance matsalar tsaro a faɗin ƙasar, sai dai sun buƙaci tana a ƙara ƙaimi domin a cewarsu an fara mayar da hannun agogo baya.

Gwamnonin sun ce yadda Boko Haram ke ƙoƙarin dawo da ayyukanta a wasu sassan Arewa maso Gabas, da kashe-kashe a Arewa ta Tsakiya ne ya sa suke kira da a yi garambawul a ɓangaren tsaro.

Da wannan ne Ƙungiyar Gwamnonin Arewa ta yi kira da a ƙara samun haɗin kai tsakanin jami’an tsaron gwamnatin tarayya da na jihohi da ƴan sa-kai.

Shugaban ƙungiyar, Gwamnan Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya ne ya bayyana hakan a sanarwar bayan taron da aka yi ranar Asabar a Kaduna.

“Ƙungiyar za ta haɗa ƙarfi da ƙarfe da Ƙungiyar Gwamnonin Nijeriya domin samar da hanyoyin taimakon jami’an tsaron gwamnatin tarayya wajen magance matsalar da ƙasar ke fuskanta,” in ji shi.

Sannan ya ce ƙungiyar za ta kafa kwamitin haɗin gwiwa domin samar da tsarin bai-ɗaya na tsaro domin sa ido kan tsaron iyakokin jihohi.

Haka kuma ƙungiyar ta sake nanata goyon bayan da kafa ’yan sandan jiha, inda gwamnonin suka yi kira ga majalisar ƙasar da ta gaggauta ɗaukar matakin yin doka domin tabbatar da ƙirƙirar ƴansandan na jiha.

Ga wasu abubuwa 5 da Gwamnonin Arewa suka tattauna a taron:

1. Kungiyar ta yaba wa shugaba Bola Tinubu kan kokarin da yake a fannin samar da tsaro a Arewa.

2. ⁠Kungiyar za ta haɗa kai da kungiyar Gwamnonin Nijeriya domin karfafa fannin tsaro a yankin.

3. ⁠Kungiyar za ta ɓullo da tsarin inganta tsaro a yankin tun daga tushe.

4. ⁠Kungiyar ta buƙaci a yi gaggawar ɗaukar matakan samar da tsaro a iyakokin jihohin yankin.

5. ⁠Kungiyar ta jaddada goyon bayanta kan samar da ‘yan sandan jihohi, inda ta buƙaci Majalisar Tarayya ta tabbatar da hakan.

Ƙungiyar ta ce za su sake zama a ranar 30 ga watan Agustan 2025.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Arewa Gwamnonin Arewa Jihar Kaduna matsalar tsaro Muhammad Inuwa Yahaya Gwamnonin Arewa da Gwamnonin

এছাড়াও পড়ুন:

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

Ya kara da cewa bukatar kasa da kasa game da karfin ma’adinai na Kaduna yana karuwa, tare da masu saka hannun jari da yawa wadanda suke bincike kan yadda za su yi amfani da wadannan albarkatun da ba a taba amfani da su ba.

“Baya ga wannan, muna da ma’adanan karfe. Kamfanin ‘African Mines’ ya riga ya zo Kaduna don hakar wannan albarkatun, wanda ya nuna a fili cewa Kaduna tana da ma’adanan karfe da za a iya gudanar da kasuwancinsu,” in ji shi.

Bello ya jaddada cewa tsarin kamfanin yana nuna jajircewa don kokarin killace iyakokin ma’adinai da kuma habaka su.

Ya ce tun lokacin da aka kafa kamfanin, hukumar gudanarwaar kamfanin ta ba da fifiko ga ayyukan da ke sanya alhakin muhalli da zamantakewar al’umma a gaba a ayyukanta.

Haka kuma manajan daraktan ya kuma yaba wa Gwamna Uba Sani saboda goyon bayan da yake bayarwa ga bangaren hakar ma’adanai, yana mai cewa a karkashin jagorancin gwamnan, kamfanin ba wai kawai a shirye yake ba har ma yana da cikakkiyar kayan aiki don samar da sakamako mai kyau.

“Ana sa ran wannan kokari zai samar da ci gaba a hakar ma’adanai tare da bude hanyoyin arziki a bangaren ma’adanai, samar da dubban ayyuka, da kuma habaka ci gaban tattalin arziki ba kawai a Kaduna ba har ma a duk fadin Nijeriya,” in ji shi.

Ya kuma tabbatar wa masu saka hannun jari na cikin gida da na waje samar da yanayi mai aminci wanda ke karfafa kirkire-kirkire da ci gaba na dogon lokaci.

Bello ya kuma sanar da cewa kamfanin bunkasa ma’adanai na Kaduna a shirye yake ya yi maraba da masu saka hannun jari da ke da sha’awar yin amfani da albarkatun kasa na jihar.

Ya bayyana tashar sarrafa lithium ta Kangimi, wacce ke aiki a karfin tan 5,000 a kowace rana, a matsayin babban ci gaba a tafiyar hakar ma’adinai ta jihar.

“Bisa jajircewar kamfanin wajen samar da aminci da ci gaba mai dorewa, Kaduna za ta kasance a matsayin babban wurin saka hannun jari,” in ji shi.

Ya nuna godiya ga Gwamna Uba Sani, yana mai cewa, “Godiya ga kokarin da Gwamna Uba Sani ya yi, muna shaida canji mai ban mamaki a bangaren hakar ma’adanai wanda ke bude hanya don kyakkyawar makoma mai kyau.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda ɓallewar ƙasashen AES ta illata ECOWAS
  • Borrell : Rabin bama-baman da aka jefa a Gaza sun fito ne daga Turai
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Gana Da Tokwaransa Na Kasar Saudiya A Jiya Asabar
  • Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari
  • Jagora Ya Jaddada Wajabci Daukan Matakan Kalubalantar Zaluncin ‘Yan Sahayoniyya
  • Matsalar Tsaro: Zulum ya haramta sayar da man fetur a Bama
  • ’Yan kungiyar asiri sun kashe masu shirin tafiya NYSC a Bayelsa
  • Nijeriya ta soke ba da tallafin karatu a ƙetare
  • AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa