Gwamnati Kaduna Tace Zuba Jarin Da Ta Yi Na Euro Miliyan Dari Da Shadaya Zai Maganin Sufuri A Jihar
Published: 14th, May 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Kaduna ta ce zuba jarin Euro miliyan dari da goma sha ɗaya da tayi akan aikin samarda hanyoyi da motocin sufuri na zamani zai rage cunkoson ababen hawa da kuma inganta rayuwar al’ummar jihar.
Kwamishinan Ma’aikatar Ayyuka da Ababen More Rayuwa ta Jihar Kaduna, Ibrahim Hamza, ne ya bayyana hakan a taron masu ruwa da tsaki kan aikin samarda hanyoyi da motocin sufuri na zamani wato BRT da aka gudanar a Kaduna.
Aikin samarda hanyoyi da motocin sufuri na zamani yana da nufin inganta zirga-zirgar ababen hawa a birane, rage cunkoso, da kuma inganta rayuwar jama’ar Jihar Kaduna.
Kwamishina Ma’aikatar Aiyyuka da Ababen More Rayuwa, Ibrahim Hamza ya tabbatar da kudurin gwamnati na sauya fasalin harkar sufuri da nufin ƙara bunƙasa tattalin arziki da jin daɗin al’umma.
Ya bayyana cewa aikin BRT wani bangare ne na ƙoƙarin gwamnati na inganta harkokin sufuri a faɗin jihar.
A nasa jawabin, Darakta Janar na Hukumar Kula da Harkokin Sufuri ta Jihar Kaduna, Injiniya Inuwa Ibrahim, ya ce tsarin BRT wani babban ci gaba ne wajen magance matsalolin sufuri da ke addabar yawan jama’a.
Ya kuma shawarci mahalarta taron su yi nazari mai zurfi kan matsalolin da ake fuskanta tare da samar da mafita domin sauƙaƙa rayuwar fasinjoji.
A nasa ɓangaren, jagoran ƙungiyar Rebel Artic Joint Venture, Ted Regino, ya bayyana cewa kamfaninsu ne ke da alhakin kula da masu aikin, inda ya tabbatar wa al’ummar Kaduna da ingantaccen aiki mai sauri da nagarta.
Mai Kula da wannan taron Injiniya Emmanuel Oche John, ya ce suna tabbatar da cewa dukkan masu ruwa da tsaki sun samu cikakken bayani kan aikin.
Wani mahalarta taron, Shugaban Ƙungiyar Masu Motocin Haya ta Ƙasa reshen Jihar Kaduna (NARTO), Alhaji Babangida Jafaru, ya bayyana cewa aikin BRT zai taimaka wajen warware matsalolin sufuri da ake fama da su a jihar.
Taken taron shi ne: “BRT a matsayin Kayan Aiki don Sarrafa Yawan Jama’a cikin Dorewa a Zamanin Fasaha,” inda aka gayyato wakilai daga NURTW, FRSC, KASTELEA da sauransu.
Cov/Adamu Yusuf
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Gwamnati Jarin Jihar Miliyan Dari Da Shadaya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jigawa Ta Raba Naira Miliyan 50 Ga Mata Da Matasa
Gwamna Umar Namadi na Jihar Jigawa ya ce yaki da talauci muhimmin mataki ne na hanzarta ci gaban tattalin arziki da samar da ayyukan yi.
Ya bayyana haka ne a lokacin shirin gwamnatin jihar mai taken “Gwamnati da Jama’a” wanda aka gudanar a karamar hukumar Ringim.
Malam Umar Namadi ya jaddada muhimmancin horas da matasa sana’o’in hannu da samar da yanayin kasuwanci mai kyau domin cimma wadannan manufofi.
Saboda haka, ya yi kira ga zababbun wakilai, masu rike da mukaman siyasa, shugabannin kasuwanci da sauran attajirai da su taimaka wa al’ummarsu domin kara bunkasa ci gaba da habaka tattalin arziki.
A yayin taron, Kwamishinan jin kai da harkokin musamman na jihar, Auwal Danladi Sankara, ya raba naira miliyan 50 a matsayin tallafin karfafa gwiwa ga matasa da mata sama da 250.
A cewarsa, wannan shirin tallafin kudi na musamman an kirkiro shi ne domin tallafawa kokarin Gwamna Umar Namadi wajen samar da ayyukan yi ga matasa, kirkiro sabbin ayyuka da kuma rage talauci a jihar.
Ya kara da cewa, an tsara tallafin kudin ne domin wasu su fadada kasuwancinsu, yayin da wasu kuma za su fara sabon kasuwanci na zabinsu.
Ya ce kowanne daga cikin wadanda suka ci gajiyar shirin ya samu naira dubu dari biyu da hamsin (₦250,000), tare da yin alkawarin ci gaba da mara wa shirin manufofi 12 na Gwamna Namadi baya, wanda aka tsara domin tabbatar da arziki da ci gaba a Jihar Jigawa.
Usman Mohammed Zaria