Gwamnati Kaduna Tace Zuba Jarin Da Ta Yi Na Euro Miliyan Dari Da Shadaya Zai Maganin Sufuri A Jihar
Published: 14th, May 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Kaduna ta ce zuba jarin Euro miliyan dari da goma sha ɗaya da tayi akan aikin samarda hanyoyi da motocin sufuri na zamani zai rage cunkoson ababen hawa da kuma inganta rayuwar al’ummar jihar.
Kwamishinan Ma’aikatar Ayyuka da Ababen More Rayuwa ta Jihar Kaduna, Ibrahim Hamza, ne ya bayyana hakan a taron masu ruwa da tsaki kan aikin samarda hanyoyi da motocin sufuri na zamani wato BRT da aka gudanar a Kaduna.
Aikin samarda hanyoyi da motocin sufuri na zamani yana da nufin inganta zirga-zirgar ababen hawa a birane, rage cunkoso, da kuma inganta rayuwar jama’ar Jihar Kaduna.
Kwamishina Ma’aikatar Aiyyuka da Ababen More Rayuwa, Ibrahim Hamza ya tabbatar da kudurin gwamnati na sauya fasalin harkar sufuri da nufin ƙara bunƙasa tattalin arziki da jin daɗin al’umma.
Ya bayyana cewa aikin BRT wani bangare ne na ƙoƙarin gwamnati na inganta harkokin sufuri a faɗin jihar.
A nasa jawabin, Darakta Janar na Hukumar Kula da Harkokin Sufuri ta Jihar Kaduna, Injiniya Inuwa Ibrahim, ya ce tsarin BRT wani babban ci gaba ne wajen magance matsalolin sufuri da ke addabar yawan jama’a.
Ya kuma shawarci mahalarta taron su yi nazari mai zurfi kan matsalolin da ake fuskanta tare da samar da mafita domin sauƙaƙa rayuwar fasinjoji.
A nasa ɓangaren, jagoran ƙungiyar Rebel Artic Joint Venture, Ted Regino, ya bayyana cewa kamfaninsu ne ke da alhakin kula da masu aikin, inda ya tabbatar wa al’ummar Kaduna da ingantaccen aiki mai sauri da nagarta.
Mai Kula da wannan taron Injiniya Emmanuel Oche John, ya ce suna tabbatar da cewa dukkan masu ruwa da tsaki sun samu cikakken bayani kan aikin.
Wani mahalarta taron, Shugaban Ƙungiyar Masu Motocin Haya ta Ƙasa reshen Jihar Kaduna (NARTO), Alhaji Babangida Jafaru, ya bayyana cewa aikin BRT zai taimaka wajen warware matsalolin sufuri da ake fama da su a jihar.
Taken taron shi ne: “BRT a matsayin Kayan Aiki don Sarrafa Yawan Jama’a cikin Dorewa a Zamanin Fasaha,” inda aka gayyato wakilai daga NURTW, FRSC, KASTELEA da sauransu.
Cov/Adamu Yusuf
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Gwamnati Jarin Jihar Miliyan Dari Da Shadaya
এছাড়াও পড়ুন:
Najeriya : Ana ci gaba da alhinin rasuwar Sheikh Dahiru Usman Bauchi
Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya bayyana jimaminsa kan rasuwar babban malamin addinin Musulunci Sheikh Dahiru Usman Bauchi, lamarin da ya ce ya kaɗu matuƙa da ya samu labarin.
Tinubu ya ce jagoran na ɗarikar Tijjaniya mutum ne mai daraja da ƙima, sannan ya bayyana shi a matsayin madubi wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen koyarwa.
Rasuwarsa za ta ba babban giɓi a Najeriya,” in ji shugaban.
Shi ma Tsohon ɗan takarar shugabancin Najeriya Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana rasuwar Sheikh Ɗahiru Usman Bauchi a matsayin rashi babba ga al’ummar Musulmi na Najeriya da ma Afirka baki ɗaya.
A wata sanarwa da Atiku ya wallafa a shafukansa na sada zumunta, ya bayyana marigayin da babban malami wanda ya koyar da addini da tarbiya.
Tsohon ɗan takarar shugaban Najeriya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya bayyana jimaminsa tare a miƙa ta’aziyya ga iyalai da ƴanuwan da makusantan Sheikh Ɗahiru Usman Bauchi bisa rasuwar malamin.
Kwankwaso ya bayyana malamin a matsayin uba, kuma babban malami wanda koyarsa ta zama madubi ga ɗimbin al’umma.
Gwamnonin arewacin Najeriya sun nuna alhinin su bisa rasuwar jagoran ɗarikar Tijjaniyya a Najeriya Shiekh Dahiru Usman Bauchi wanda ya rasu a yau alhamis.
Gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad ya bayyana marigayi Sheikh Dahiru Bauchi a matsayin mutumin da ya damu da harkokin addinin musulunci, mai son zaman lafiya, da samar da fahimta da juriya tsakanin musulmai da mabiya sauran addinai.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran ta yi tir da Australiya kan alakanta IRGC, da mai tallafawa ta’addanci November 27, 2025 Ramaphosa ya soki kalaman Trump na cewa ba zai gayyaci shi a taron G20 November 27, 2025 ECOWAS ta yi Allah wadai da juyin mulki a Guinea Bissau November 27, 2025 Faransa, Jamus, Italiya, da Burtaniya sun yi tir da “karuwar rikici” a yammacin kogon jodan November 27, 2025 Rasha A Shirye Take Ta Taimaka Wa Najeriya A Fada Da Ta’addanci November 27, 2025 Palasdinawa Sun Karbi Gawawwakin Shahidai 15 Daga ‘Yan Mamaya November 27, 2025 Makaman Iran Masu Linzami Ne Kandagarkon Dake Takawa Makiya Birki November 27, 2025 Najeriya: Allah Ya Yi Wa Babban Malamin Addini Shehu Dahiru Bauchi Rasuwa November 27, 2025 An Zabi Iran A Cikin Majalisar Zartarwa Ta Hukumar Yaki Da Makamai Masu Guba Ta Duniya CWC November 27, 2025 HKI Tana Amfani Da Tsagaita Wuta A Gaza Don Sake Shata Kan Iyakokin Yankin November 27, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci