HausaTv:
2025-11-08@20:14:09 GMT

Ministan harkokin wajen Iran zai Ziyarci Saudiyya da Qatar

Published: 9th, May 2025 GMT

A wani lokaci a gobe Asabar ne ake sa ran ministan harkokin wajen Iran zai fara wata ziyara a kasashen Saudiyya da kuma Qatar.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya bayyana cewa, ministan harkokin wajen kasar Abbas Araghchi zai ziyarci Saudiyya da Qatar a, bayan rahotannin da ke cewa akwai yiwuwar yin wata sabuwar tattaunawa tsakanin Tehran da Washington.

M. Baghai ya bayyana cewa ziyarce ziyarce da Araghchi zai yi na daga cikin manufofin Jamhuriyar Musulunci ta Iran na ci gaba da karfafa alakarta da makwabtanta.

“Ministan harkokin wajen kasar ta Iran, zai fara tafiya birnin Riyadh don ganawa da manyan jami’an Saudiyya, sannan kuma zai tafi Doha don halartar taron tattaunawa tsakanin Iran da kasashen Larabawa.”

Bayanin hakan ya biyo bayan rahoton da kafar yada labaran Amurka Axios ta bayar cewa, ranar Lahadi ne ake sa ran za a gudanar da zagaye na hudu na tattaunawar tsakanin Iran da Amurka a birnin Muscat na kasar Omani.

Tun da farko dai an shirya gudanar da taron ne a ranar 3 ga watan Mayu, amma aka dage.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: harkokin wajen

এছাড়াও পড়ুন:

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang, wakilin cinikayyar kasa da kasa na ma’aikatar kasuwanci kuma mataimakin ministan kasuwanci na kasar Sin, ya gana da tawagar cinikayyar kayan noma ta Amurka a birnin Beijing a jiya Talata 4 ga watan Nuwamb, inda bangarorin biyu suka yi musayar ra’ayoyi kan huldar tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Amurka, da cinikayyar kayayyakin noma, da sauran batutuwa masu alaka.

Li Chenggang ya bayyana cewa kyakkyawar alaka ta tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Amurka tana da alfanu ga kasashen biyu da kuma duniya baki daya. Tun daga watan Mayu na wannan shekarar, tawagogin tattalin arziki da cinikayya na bangarorin biyu sun tattauna har sau biyar bisa jagorancin muhimmiyar matsayar da shugabannin kasashen biyu suka cimma, wanda hakan ya karfafa daidaituwar alakar tattalin arziki da cinikayyar Sin da Amurka. Wannan ya tabbatar da cewa, Sin da Amurka suna da yakini a kan ci gaba da samun daidaito, girmamawa, da kuma cin gajiyar juna, kuma za su iya samun mafita a kan matsaloli ta hanyar tattaunawa da hadin gwiwa.

A nasu bangaren, membobin tawagar ta Amurka sun bayyana cewa kasar Sin muhimmiyar kasuwa ce ta fitar da kayan noma na Amurka, kuma manoman Amurka suna girmama hadin gwiwar da ke tsakaninsu da kasar Sin, kana suna da niyyar hada hannu don fadada hadin gwiwa da kasar Sin. Sun kara da cewa, dangantakar tattalin arziki da cinikayya mai dorewa tsakanin kasar Sin da Amurka tana da matukar muhimmanci ga cinikin kayan noma tsakanin kasashen biyu, kuma suna fatan ci gaba da samun kyakkyawan yanayin bunkasa huldar tattalin arziki da cinikayya tsakanin kasashen biyu. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin November 5, 2025 Daga Birnin Sin Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya November 5, 2025 Daga Birnin Sin An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou November 5, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Tabbatar Da Hannun Amurka Wajen Kaddamar Da Yaki Kanta
  • An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Wuce Gona Da Iri Kan Kasar Lebanon
  • Xi Jinping Ya Taya Paul Biya Murnar Tazarce a Kamaru
  • Mun fara tattaunawa da Amurka kan barazanar Trump – Gwamnatin Tarayya
  • Araqchi Ya Ce: Harin Amurka Kan Kasar Venezuela Ya Bayyana Karara Duniya Tana Gani
  • Shugabannin Iran Da Faransa Sun Yi Wata Tattaunawa Ta Wayar Tarho
  • Gharibabadi: Kyakkyawar Alaka Tsakanin Iran Da Saudiyya Na Da Babban Tasiri Ga Yankin Da Ma Duniya
  • Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro
  • Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka