Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara
Published: 14th, May 2025 GMT
Ya ce, “Samar da motocin aiki ga jami’an tsaron zai bayar da ci gaba wajen sawwaƙa masu zirga-zirga, kai ɗauki a kan lokaci da ƙara ƙarfafa masu gwiwa wajen samar da tsaro da bin doka da oda.
“Wannan taro na yau, wani ci gaba ne na ƙoƙarin gwamnatina wajen ƙarfagawa, tare da inganta ayyukan jami’an tsaron da ke aiki a duk faɗin jihar.
“Wannan kuma yana ɗamfare ne da alƙawuran da muka yi, tare da jajircewar mu wajen samar da duk abin da za mu iya don tunkarar dukkan nau’o’in rashin tsaro, samar da zaman lafiya, kare rayuka da dukiyar jama’ar jihar mu.
“Wannan ƙoƙari namu yana ƙara nuna hobbasan gwamnatin mu wajen ƙarfafa wa jami’an tsaron mu don su samu sauƙin samar da tsaron rayuka da dukiyar al’ummar mu.
“Muna sane da muhimmancin ayyukan su wajen tabbatar da bin doka da oda don a samu cigababbiyar jihar Zamfara da ma ƙasa baki ɗaya.
“Saboda haka gwamnatina ta yi tsayin-daka wajen ganin an samar wa da jami’an tsaron nan, da duk goyon baya don su samu damar gudanar da ayyukan su cikin nasara.
“Ta bangare mu, mun kafa jami’an tsaron mu na kan mu, waɗanda muka sanya wa suna Jami’an Kare Al’ummar mu, Askarawan Zamfara, wato ‘Community Protection Guards.’ Mun yi niyyar tallafa wa ƙoƙarin ku, mu yi musayar ra’ayi, mu jawo al’ummar mu don kare ƙasar mu.
“A wannan taro namu na yau, mun shirya raba motoci guda 140 sabbi dal ga rukunonin jami’an tsaron mu da ke aiki a jihar nan. Waɗanda suka haɗa da A-kori kura mai gida biyu da motocin tsaro na Buffalo, duk mun samar da su ne don ƙarfafa wa jami’an tsaron da suka amfana.”
Gwamnan ya ci gaba da cewa gwamnatin sa ta samar da motocin ba-bas sabbi guda 50 don inganta harkar sufuri a jihar.
“Wannan yana daga cikin tsarin mu na inganta harkar sufurin cikin gida da masu tafiya zuwa wajen jihar.
“Mun samar da kyakkyawan tsarin da zai tabbatar da kula da motocin, da kuma hana almubazzarancin da kuɗin da ake tarawa a harkar.
“Akwai na’urorin da aka sanya wa waɗannan motoci, waɗanda za nuna inda mota ta ke a kowane lokaci, an kuma sanya internet a cikin su domin fasinjoji.
“Kafin in kammala jawabina, zan girmama sadaukar da ran da Askarawan mu suka yi, waɗanda suka rasa rayukan su wajen kare martabar ƙasar mu, tare da iyalan da suka bari. Muna tuna ku a kowane lokaci, kuma muna girmama sadaukarwar ku.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: jami an tsaron
এছাড়াও পড়ুন:
An hana hawa babur da daddare a fadin jihar Gombe
A yayin da ake tsaka da bikin Ranar Dimokradiyya a Najeriya, al’ummar jihar Gombe sun wayi gari da sabuwar dokar takaita zirga-zirgar babura daga ƙarfe 7:00 na yamma zuwa ƙarfe 6:00 na safe a duk faɗin jihar.
Sanarwar da ta fito ne daga hannun Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar ’Yan Sanda ta jihar, DSP Buhari Abdullahi, ranar Alhamis, a madadin kwamishinan ’yan sandan jihar Bello Yahaya.
Sanarwar ta ce an kafa dokar ne don rage ayyukan ta’addanci a fadin jihar.
Guguwa ta hallaka mutum 6, ta jikkata 30 a Taraba An kashe mutum 41 cikin mako ɗaya a FilatoKafa dokar na zuwa ne kwana uku bayan wasu matasa da ba a tantance su wane ne ba suka kashe wani magidanci mai suna Ahmad Aliyu, wanda aka fi sani da Amadi Kasiran, a unguwar Hammadu Kafi da ke Gombe, a daren Lahadi.
Sanarwar ta ƙara da cewa duk wanda aka kama ya karya dokar zai fuskanci hukunci mai tsauri, ciki har da gurfanar da shi a gaban kotu.
Kazalika, sanarwar ta ce dokar ta haramta ɗaukar mutum fiye da ɗaya a kan babur domin rage matsalar rashin tsaro a jihar.
“Dokar hana hawa babur da goyon biyu ta fara aiki ne daga yau, Alhamis, ranar bikin Dimokradiyya, har sai wani lokaci da ba a kayyade ba,” in ji Kakakin ’yan sandan.
Rundunar ’yan sandan ta ce an ɗauki wannan mataki ne don magance matsalar bata-gari na ‘’yan kalare’ da sauran ayyukan ta’addanci.
A lokacin da wakilinmu ya kai ziyara kwaryar birnin Gombe, filin wasa na Pantami ya kasance a rufe ba tare da alamar wani biki ba.
Sai dai ya gane wa idanunsa cewa an jibge jami’an tsaro a sassa daban-daban, ciki har da ’yan sanda, jami’an tsaro na farin kaya (DSS), da kuma ’yan banga.
Wannan sabuwar doka ta ja hankalin mutane da dama a jihar, musamman mazauna yankunan da aka fi samun matsalar tsaro.
Sai dai wasu na gani za ta kara jefa jihar cikin kuncin talauci sakamakon rufe shaguna da kasuwanni da wuri saboda rashin abun hawa wanda dama can baburan aka fi hawa saboda tsadar rayuwa.