Kashi 42 Na Ma’aikatan Jinya Na Niyyar Barin Afirka Saboda Rashin Albashi – WHO
Published: 12th, May 2025 GMT
Yayin da a wannan Litinin ake bikin ranar jami’an jinya ta Duniya ta shekarar 2025, hukumar lafiya ta Duniya WHO ta ce akwai kashi 42 cikin 100 na ma’aikatan jinya a Afirka, dake cike da burin ficewa daga nahiyar saboda rashin cikakkiyar kulawa da kuma albashi mara tsoka.
A jawabin da ya gabatar akan ranar ma’aikatan jiniya ta duniya, Daraktan riƙo na Hukumar ta WHO a Afirka, Chikwe Ihekweazu, ya ce ficewar tasu za ta nakasa harkokin kiwon lafiyar da ake riritawa a nahiyar.
Ihekweazu ya cigaba da cewa wannan ɓangare na masu aikin jinyar na da matuƙar muhimmanci ga ɗaukacin al’umma, don haka bashi kulawa, abu ne da ya dace, domin zai ba da gudunmawa ga cigaban ɓangaren lafiya, wanda kuma zai taka rawa wajen bunƙasar tattalin arzikin ƙasa da al’umarta.
Wannan rana na zuwa ne a yayin da jami’an jinyar da dama da na wasu sassan kiwon lafiya suka bar Najeriya, ƙasa mafi yawan al’umma a nahiyar Afirka, domin tafiya ƙasashen ƙetare da zummar samun kyakkyawar kulawa da tsarin da ya zarce wanda suke samu a kasarsu
rfi
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jami an jinya
এছাড়াও পড়ুন:
Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo
Sakamakon kama Mu’azu Ɓarga, yanzu haka abokan ta’asar tasa sai tsallakewa suke domin tserewa kamun rundunar ‘yan sanda, duk da gudun da suke rundunar na ci gaba da farautarsu har kuma an samu nasarar ƙara damƙe mutane biyu cikin sama da mutane arba’in da Ɓarga ya bayyana wa ‘yan sanda. Wannan tasa a ranar Juma’ar da ta gabata Al’ummar Sheka ƙarƙashin inuwar Ƙungiyar Muryar Jama’ar Sheka ta ziyarci Shelkwatar ‘yan sandan Kano da ke Bompai domin jinjina wa ƙoƙarinsu.
Cikin shahararrun mafaɗatan da suka gamu da ajalinsu alokacin arangama daban-daban akwai matashin da ya addabi al’ummar Unguwar Ɗorayi mai Suna Barakita, sai kuma wani mai suna Khalufa ɗan unguwar Ƙofar Mazugal Da kuma wani guda da ke tafka irin wannan ta’asa a unguwar Gwammaja duk a kwaryar birnin Kano.
Yanzu haka dai a iya cewa faɗan daba da ƙwacen wayoyin gannu na neman zama ruwan dare a Jihar Kano, sai dai kuma rundunar ‘yan sandan Jihar Kano ƙarƙashin Kwamiahinan da ke jagorantar operation ba sani ba sabo, ta bakin mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan na Kano Abdullahi Haruna Kiyawa na ci gaba da samun nasarar kakkaɓe mafaɗatan tare da shiga lungu da saƙo domin farautar maɓarna
tan
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp