Yayin da a wannan Litinin ake bikin ranar jami’an jinya ta Duniya ta shekarar 2025, hukumar lafiya ta Duniya WHO ta ce akwai kashi 42 cikin 100 na ma’aikatan jinya a Afirka, dake cike da burin ficewa daga nahiyar saboda rashin cikakkiyar kulawa da kuma albashi mara tsoka.

A jawabin da ya gabatar akan ranar ma’aikatan jiniya ta duniya, Daraktan riƙo na Hukumar ta WHO a Afirka, Chikwe Ihekweazu, ya ce ficewar tasu za ta nakasa harkokin kiwon lafiyar da ake riritawa a nahiyar.

Ihekweazu ya cigaba da cewa wannan ɓangare na masu aikin jinyar na da matuƙar muhimmanci ga ɗaukacin al’umma, don haka bashi kulawa, abu ne da ya dace, domin zai ba da gudunmawa ga cigaban ɓangaren lafiya, wanda kuma zai taka rawa wajen bunƙasar tattalin arzikin ƙasa da al’umarta.

Wannan rana na zuwa ne a yayin da jami’an jinyar da dama da na wasu sassan kiwon lafiya suka bar Najeriya, ƙasa mafi yawan al’umma a nahiyar Afirka, domin tafiya ƙasashen ƙetare da zummar samun kyakkyawar kulawa da tsarin da ya zarce wanda suke samu a kasarsu

rfi

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jami an jinya

এছাড়াও পড়ুন:

Yuan (RENMINBI) Na Ci Gaba Da Samun Farin Jini A Kasashen Afirka 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin
  • Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…
  • Gwamnatin Neja ta rufe Jami’ar IBB bayan ɓarkewar rikici
  • Gwamnatin Kano ta ba da hutun sabuwar shekarar musulunci
  • Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato
  • Arsenal za ta ɗauki ɗan ƙwallon Brentford Christian Norgaard
  • DHQ Za Ta Tura Dakaru Na Musamman 800 Yankunan Da Ke Fama Da Rashin Tsaro – CDS
  • Yuan (RENMINBI) Na Ci Gaba Da Samun Farin Jini A Kasashen Afirka 
  • Harin asibiti ya kashe mutum 40 a Sudan — WHO
  • Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump