HausaTv:
2025-09-24@11:17:04 GMT

Gaza:Falasdinawa 7 Sun Yi Shahada Da Safiyar Yau Asabar

Published: 10th, May 2025 GMT

Da safiyar yau Asabar Falasdinawa 7 sun yi shahada sanadiyyar harin da HKI ta kai a yankin Gaza.

Sojojin HKI sun kai harin ne a kan sansanin ‘yan hijira na unguwar ” al-Sabrah” a cikin birnin Gaza, da hakan ya yi sanadiyyar shahadar Falasdinawa 5 a iyalai daya na Dulaibh. Shahidan su nel Saqar Ahmad Fu’ad dulaibh, da matarsa Hindu, da ‘ya’yansu Ahmad, Hamzah, da Abdulazizi.

Haka nan kuma ‘yan sahayoniyar sun kai wasu hare-haren ta jirgin sama maras matuki a unguwar “Tuffah” dake birnin Gaza, da ya yi sanadiyyar shahadar mutum daya.

Su ma jiragen ruwan HKI sun kai wasu hare-haren munanan a garin Rafah da ya yi sanadiyyar shahadar Muhammad Sa’id al-Burudawil.

A tsakiyar birnin Gaza, ma dai ‘yan sahayoniyar sun kai wasu hare-hare da manyan bindigogi da ya yi sanadiyyar shahadar karamin yaron Bafalasdine guda.

A wani gefen hukumar Gaza ta sanar da cewa yunwa, tana barazana ga rayuwar kananan yaran da sun kai 65,000 saboda ci gaba da hana shigar da kayan abinci cikin yankin na Gaza, da HKI take yi, na tsawonn watanni 2 a jere.

Tsawon kwanaki 40 kenan da dukkanin gidajen burodi a cikin yankin na Gaza su ka rufe kofofinsu saboda rashin fulawa.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: ya yi sanadiyyar shahadar

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun Daƙile Hare-haren ISWAP, Sun Bai Wa Magidanta 10,000 Kariya A Borno

Haka kuma sun tabbatar da cewa manoma da suka koma gonakinsu kwanan nan sun samu kariya.

Babu wanda aka sace ko ɗaya, yayin da jama’ar yankin ke ci gaba da zama lafiya.

A ranar 19 ga watan Satumba, Birigediya Janar Ugochukwu Unachukwu, wanda shi ne muƙaddashin kwamandan rundunar sojojin 7 Division, ya kai ziyara Banki don yaba wa sojoji kan jarumtar da suka nuna.

Ya ce ‘yan ta’addan sun yi mummunan rashi kuma ya tabbatar wa jama’a cewa rundunar sojojin Nijeriya za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyi.

Sai dai rundunar ta tabbatar da cewa wani soja ya rasa ransa yayin kare mutanen, yayin da wasu suka ji rauni.

Sojojin sun ce wannan shaida ce ta jajircewar rundunar wajen tabbatar da zaman lafiya da kare ‘yan Nijeriya da suka koma gidajensu bayan gudun hijira.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Fiye Da Falasdinawa 900,000 Ne Su Ka Yi Hijira A Cikin Gaza
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Kama Masu Laifi
  • Xi Ya Bukaci Hada Karfi Da Karfe Wajen Gina Yankin Xinjiang Ya Zama Mafi Kyau
  • Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Guguwar Amincewa Da Kasar Falasdinu Ta Nuna Yadda Amurka Da Isra’ila Suka Zama Saniyar Waren Da Ba A Taba Gani Ba
  • Lebanon: A yau Ne Aka Yi Jana’izar Shahidan Bitij Bail Wadanda HKI Ta Kai Ga Shahada A Ranar Lahadi
  • Xi Jinping Zai Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 70 Da Kafuwar Yankin Xinjiang Na Uygur Mai Cin Gashin Kansa
  • Sojoji Sun Daƙile Hare-haren ISWAP, Sun Bai Wa Magidanta 10,000 Kariya A Borno
  • Bayan Sulhu  Da Ƴan Bindiga, An Saki Mutane 70 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina
  • Lokaci Yayi Da Shugabannin Arewa Za Su Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Yankin –  ACI
  • Hizbullah Ta Gayyaci Mutane Da Su Fito Domin Tunawa Da Zagayowar Shahadar Sayyid Hassan Nasrallah