Najeriya ba za ta koma mulkin soja ba — Gowon
Published: 15th, May 2025 GMT
Tsohon Shugaban Ƙasa, Janar Yakubu Gowon (mai ritaya), ya ce Najeriya ba za ta sake komawa mulkin soja ba.
Ya bayyana haka ne a Babban Birnin Tarayya, Abuja yayin ƙaddamar da littafi mai suna “Military Factor in Nigerian History, 1960-2018”, domin murnar cika shekaru 70 da kafa ƙungiyar Tarihi ta Najeriya (HSN).
Gowon ya ce duk da irin gudunmawar da sojoji suka bayar a tarihin Najeriya, musamman a lokacin yaƙin basasa da kuma samar da ababen more rayuwa bai kamata su sake tsoma baki a siyasa ba.
Ya jaddada cewa dimokuraɗiyya, duk da kurakuran da ake samu a cikinta, ita ce hanya mafi dacewa don ci gaban ƙasa.
“Ya kamata zamanin mulkin soja ya ƙare a Najeriya. Duk da gazawar dimokuraɗiyya ita ce hanya mafi kyau wajen ci gaban ƙasa da kuma bai wa mutane dama su shiga harkokin mulki,” in ji Gowon.
Ya amince cewa a wasu lokuta a mulkin soja ya tauye ’yancin jama’a kuma ya hana dimokuraɗiyya ci gaba.
Sai dai ya ce, idan aka amince da kuskuren da aka yi a baya, za a samu ingantaccen tsarin siyasa a gaba.
“Mulkin soja ya zo da ci gaba da kuma raɗaɗi. Don mu samu ci gaba, dole ne mu karɓi gaskiya game da abin da ya faru a baya, mu gyara gaba,” in ji shi.
Gowon ya ƙara da cewa akwai buƙatar rundunar soji ta mayar da hankali wajen kare ƙasa, ta inganta fasaharta, sannan ta ƙara haɗin kai da hukumomin fararen hula domin samar da zaman lafiya da ƙarfafa haɗin kan ƙasa.
Shi ma tsohon Shugaban Hafsoshin Tsaro, Janar Lucky Irabor (mai ritaya), ya yabawa irin gudunmawar da sojoji suka bayar ta fuskar ginea hanyoyi, gadoji da wanzar da zaman lafiya.
Sai dai ya ce ba za a iya watsi da batun take hakkin ɗan adam a lokacin mulkin soja ba.
Littafin da aka ƙaddamar ya samu yabo daga masana da suka ce ya yi bayani dalla-dalla kan tasirin soja a siyasa, tattalin arziƙi da zamantakewar Najeriya.
An shawarci ɗalibai, masu tsara manufofi da jami’an tsaro da su karanta littafin domin ƙara samun ilimi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Najeriya Siyasa Yakubu Gowon
এছাড়াও পড়ুন:
An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK
Lee ya kara da cewa, fifikon musammam da Hong Kong ke da shi karkashin manufar “kasa daya mai tsarin mulki biyu’, ya ba yankin damar jan hankalin masu zuba jari na ketare domin su lalubo damarmakin kasuwanci a yankin da ma kasuwar babban yankin kasar Sin tare da taimakwa kamfanonin babban yankin shiga kasuwannin ketare.
Bugu da kari, ya ce kamfanonin waje da dama sun samu damarmakin kasuwanci a Hong Kong, kuma suna ci gaba da fadada harkokinsu. Su ma kamfanonin babban yankin kasar Sin sun aminta da karfin Hong Kong kuma suna hada gwiwa da tawagar dake Hong Kong wajen lalubo damarmakin dake akwai a kasuwanni masu tasowa na ketare. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp