Aminiya:
2025-06-29@08:56:03 GMT

Najeriya ba za ta koma mulkin soja ba — Gowon

Published: 15th, May 2025 GMT

Tsohon Shugaban Ƙasa, Janar Yakubu Gowon (mai ritaya), ya ce Najeriya ba za ta sake komawa mulkin soja ba.

Ya bayyana haka ne a Babban Birnin Tarayya, Abuja yayin ƙaddamar da littafi mai suna “Military Factor in Nigerian History, 1960-2018”, domin murnar cika shekaru 70 da kafa ƙungiyar Tarihi ta Najeriya (HSN).

JAMB ta ɗauki alhakin faɗuwar ɗalibai jarrabawar 2025, ta nemi afuwa Da muna kan mulki ni da Lamido da mun ƙalubalanci Tinubu — Amaechi

Gowon ya ce duk da irin gudunmawar da sojoji suka bayar a tarihin Najeriya, musamman a lokacin yaƙin basasa da kuma samar da ababen more rayuwa bai kamata su sake tsoma baki a siyasa ba.

Ya jaddada cewa dimokuraɗiyya, duk da kurakuran da ake samu a cikinta, ita ce hanya mafi dacewa don ci gaban ƙasa.

“Ya kamata zamanin mulkin soja ya ƙare a Najeriya. Duk da gazawar dimokuraɗiyya ita ce hanya mafi kyau wajen ci gaban ƙasa da kuma bai wa mutane dama su shiga harkokin mulki,” in ji Gowon.

Ya amince cewa a wasu lokuta a mulkin soja ya tauye ’yancin jama’a kuma ya hana dimokuraɗiyya ci gaba.

Sai dai ya ce, idan aka amince da kuskuren da aka yi a baya, za a samu ingantaccen tsarin siyasa a gaba.

“Mulkin soja ya zo da ci gaba da kuma raɗaɗi. Don mu samu ci gaba, dole ne mu karɓi gaskiya game da abin da ya faru a baya, mu gyara gaba,” in ji shi.

Gowon ya ƙara da cewa akwai buƙatar rundunar soji ta mayar da hankali wajen kare ƙasa, ta inganta fasaharta, sannan ta ƙara haɗin kai da hukumomin fararen hula domin samar da zaman lafiya da ƙarfafa haɗin kan ƙasa.

Shi ma tsohon Shugaban Hafsoshin Tsaro, Janar Lucky Irabor (mai ritaya), ya yabawa irin gudunmawar da sojoji suka bayar ta fuskar ginea hanyoyi, gadoji da wanzar da zaman lafiya.

Sai dai ya ce ba za a iya watsi da batun take hakkin ɗan adam a lokacin mulkin soja ba.

Littafin da aka ƙaddamar ya samu yabo daga masana da suka ce ya yi bayani dalla-dalla kan tasirin soja a siyasa, tattalin arziƙi da zamantakewar Najeriya.

An shawarci ɗalibai, masu tsara manufofi da jami’an tsaro da su karanta littafin domin ƙara samun ilimi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Najeriya Siyasa Yakubu Gowon

এছাড়াও পড়ুন:

2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya

Haka shi ma, shugaban ADC, Cif Ralph Okey Nwosu, ya karyata amincewa da ADA, yana mai cewa batun zama jam’iyya kawance lokaci ya riga ya shude. Ya ce sake bijiro da kawance a hukumance ya faru ne wannan makon, bisa ga shawarar daga dukkan masu ruwa da tsaki.

A cewar wani rahoto, NNCG ta yi rajistar ADA a hukumance ga INEC. Wasikar neman rajistar ADA daga INEC an sanya hannu a kai daga shugaban kungiyar na wucin gadi, Cif Akin A. Rickets, da sakataren kungiyar na wucin gadi, Abdullahi Elayo.

Hadakar ta kuma gabatar da takardu masu muhimmanci, daga cikin su akwai kundin tsarin mulkin jam’iyyar da aka bayar da manufifinra da tambari da kuma bayanan taron kafa ta.

Wasikar ta bayyana cewa alamar masara tana wakiltar juriya da tsafta da muhimman tunani da suke fatan inganta.

“Mun kara hadawa da manufofinmu wacce ta kunshi bayanai game da ra’ayin jam’iyyarmu da kundin tsarin mulkinmu wanda ke bayar da doka da ke bayyana ainihinmu, tsarinmu, da mamufarmu,” in ji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Monaco ta dauki Paul Pogba
  •   Ka’a’ni: Nasarar Da Mu Ka Samu Za Ta Ci Gaba Da Dorewa
  •  Iran: Babu Wani Alfanu A Ci Gaba Da Bai Wa IAEA Hadin Kai
  • Yadda na hannun daman ’Yar’Adua ya yi tuggun hana ni zama shugaban ƙasa — Jonathan 
  • Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai
  • Shugaban APC na ƙasa Ganduje ya yi murabus
  • 2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya
  • Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP
  • NAJERIYA A YAU: Ko Wadanne Dalilai Ne Ke Hana Mata A Arewa Koyon Ilimin Kimiyya?
  • Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji