Duba da yadda yanayin muhalli yake, zai  ba da dama wajen rage fuskantar sauyin yanayi tare da inganta kiwon lafiyarsu, abincinsu da kuma ingancin ruwan shansu.

2- Fashin Baki Kan Abin Da Zai Iya Afkuwa A Wajen Kiwon Su:

Ga wanda zai fara wannan kiwo, ana so ya zabi wajen da ya dace da kuma tsarin da zai yi, don guje wa abin da zai iya afkuwa a bangaren sauyin yanayi mai tsanani.

3- Raba Kafa A Yayin Kiwon: Masu iya magana na cewa, ‘Ba a zuba kwai a cikin kwando daya’, wato ma’ana, ana so ka raba kafa ta hanyar yin wata dabara a kan kayanka, don kaucewa yin asara.

Kazalika, raba kafa na taimakawa wajen kara bunkasa kiwo da kuma kara sama wa mai kiwon kudin shiga.

4- Amfani Da Gargadin Farko: Ana so masu kiwo su rika bibiyar bayanai a kan afkuwar sauyin yanayi, wanda hakan zai ba su damar daukar mataki a kan lokaci, domin su kauce wa yin asara.

5- Amfani Da Ingannatun Kayan Aiki Don Yin Kiwo:

Kwamin kiwonsu da ake ginawa a kasa da kuma wanda ake ginawa a kan tudu, ana so a ba su kariya daga afkuwar ambaliyar ruwa. Kazalika, ana so kwamin ya kasance mai zurfi, domin bayar da kariya daga fari da kuma yanayi mai zafi.

6 Ana So Mai Wannan Kiwo Ya Rika Tuntubar Sauran Masu Kiwo:

Akasarin masu kiwo, ba zai yiwu su tafiyar da komai su kadai ba, saboda haka, ana bukatar su rika tuntubar sauran kungiyoyin da ke kiwon Kifi; don samun shawarwarin da za su taimaka musu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Fish farming

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kwara Ta Horar Da Manoma Sama Da 500 Tare Da Basu Tallafi

Manoma sama da 500 daga gundumomi 15 na karamar hukumar Ifelodun ta jihar Kwara sun samu horo kan kiwon awaki na zamani da kuma yadda ake samar da abincin dabbobi, a wani yunƙuri na rage yawan rikici tsakanin manoma da makiyaya tare da inganta rayuwar al’ummar karkara.

An gudanar da wannan horo a Idofian karkashin haɗin gwiwar karamar hukumar Ifelodun da shirin Livestock Productivity and Resilience Support Project (L-PRES).

Da yake jawabi a wurin taron, mataimakin gwamnan jihar Kwara, Mista Kayode Alabi wanda Honarabul Ganiyu Afolabi, dan majalisar jihar mai wakiltar mazaɓar Omupo ya wakilta,  ya jaddada muhimmancin wannan shiri wajen magance matsalolin da manoman karkara ke fuskanta. Ya bayyana cewa shirin ba wai kawai zai rage rikici ba ne,  zai kuma ƙara yawan kudaden shiga ga manoma da kuma ƙarfafa cin gashin kansu.

Ya ja hankalin mahalarta da su yi amfani da damar wajen amfani da sabbin ilimin da suka samu domin faɗaɗa sana’arsu da kuma samar da abincin dabbobi cikin sauƙi ta hanyar amfani da shara daga amfanin gona.

Shi ma da yake jawabi, shugaban karamar hukumar Ifelodun, Honarabul Abdulrasheed Yusuf, ya bayyana cewa wannan shiri zai taimaka wajen samar da ayyukan yi da kuma rage kuɗin da ake kashewa wajen kiwon dabbobi ta hanyar samar da abincin dabbobi a cikin gida.

Ya kuma ƙara da cewa karamar hukumar tana aiki tare da masu ruwa da tsaki don samar da muhimman abubuwa kamar ruwa da wasu muhimman abubuwan raya ƙauyuka.

A nasa jawabin, sarkin Igbaja, Oba Ahmed Babalola (Elesie na Igbaja), ya yabawa wadanda suka shirya wannan horo, yana mai cewa an yi shi a  lokacin da ya dace. Ya tabbatar wa  mahalarta  cikakken goyon baya domin nasara da dorewar shirin.

A baya, shugaban shirin L-PRES a jihar Kwara, Mista Olusoji Oyawoye, ya ƙarfafa matasa da su rungumi dama a fannin noma domin su dogara da kansu maimakon jiran aikin gwamnati. Ya buƙaci mahalarta horon da su rungumi shirin da cikakkiyar niyya domin su samu ƙwarewa da za ta taimaka musu da al’ummarsu gaba ɗaya.

Wannan horo wani ɓangare ne na babban shirin L-PRES da ke ƙoƙarin ƙara yawan amfanin kiwo, rage rikice-rikice, da kuma inganta ɗorewar rayuwa a ƙauyuka a faɗin Najeriya.

Ali Muhammad Rabi’u

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata
  • NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja
  • Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 
  • Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150
  • Hizbullah: Amurka na hakoron taimaka wa ajandar Isra’ila ne a kan Lebanon
  • Sai Ƴan Siyasa Sun Haɗa Kansu Sannan Za Su Iya Tunkarar APC A 2027 – Lukman
  • Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo
  • Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana
  • Gwamnatin Kwara Ta Horar Da Manoma Sama Da 500 Tare Da Basu Tallafi
  • An Biya Diyyar Naira Miliyan 277 Ga Wadanda Aikin Ginin Masallacin Gumel Ya Shafa