Yaran Bello Turji sun ƙwace garin su tsohon Gwamnan Sakkwato, Bafarawa
Published: 12th, May 2025 GMT
’Yan bindiga da ake zargin yaran fitaccen jagoran ’yan bindiga Bello Turji ne, sun ƙwace yankin Bafarawa, garin su tsohon gwamna Attahiru Dalhatu Bafarawa.
’Yan bindigar sun kai harin tare da ƙwace wasu ƙauyuka huɗu ne a ranar Asabar a Ƙaramar Hukumar Isa ta Jihar Sakkwato.
Harin, wanda ake zargin wani kwamandan Turji mai suna Danbakolo ne ya jagoranta, ya kuma shafi ƙauyukan Gebe, Kamarawa, Garin Fadama da Haruwai.
Ana zargin harin da aka kai da kusan ƙarfe 11 na safe ran Asabar, martani ne ga ayyukan sojoji na baya-bayan nan da suka yi niyyar fatattakar ’yan bindiga a yankin.
NAJERIYA A YAU: Gaskiyar Tasirin Amfani Da Irin Noma Na GMO NDLEA ta kama matar da ta ɓoye hodar iblis a al’aurartaMajiyoyi a yankin sun ce an kashe mutane uku—ciki har da wata mata da ɗanta—a lokacin harin, wanda wasu mazauna ke zargin na hannun Turji ne ya jagoranta.
Maharan sun yi wa Bafarawa ƙofar rago, inda suka zargi mazauna da bai wa sojoji bayanan sirri.
Wani mazaunin yankin ya shaida wa wakilinmu cewa maharan, “Sun tafi kai tsaye fadar Sarkin Gabas na Bafarawa, Alhaji Muhammad Dalhatu, wanda shi ne babban ɗan uwan tsohon gwamnan.
“Sun yi ta neman sa, sun tafi da kuɗinsa da wayoyinsa, kuma sun yi wa al’umma gargadi game da haɗa kai da jami’an tsaro.”
Mazauna ƙauyukan da abin ya shafa sun gudu zuwa garin Shinkafi da ke kusa domin tsira.
Sai dai rahotanni sun ce sojoji sun ƙarfafa musu gwiwa da su koma gida a ranar Lahadi, tare da ba su tabbacin ingantaccen tsaro.
Lokacin da aka tuntube shi domin jin ta bakinsa, kakakin ’yan sanda na Jihar Sakkwato, DSP Ahmad Rufa’i, ya musanta faruwar lamarin.
Ya ce, “Ba na tunanin akwai wani abu kamar haka saboda akwai jami’an tsaro da yawa a waɗannan yankunan.”
Duk da musantawar, majiyoyi da yawa sun tabbatar da cewa hare-haren sun faru kuma sun bar mazauna cikin tsoro.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Bafarawa Sakkwato
এছাড়াও পড়ুন:
Zaɓen Kamaru: Tchiroma Bakary na da kwarin gwiwa a yayin da ake jiran sakamako
An kammala kada ƙuri’a da yammacin Lahadi a zaɓen shugaban ƙasa na Kamaru, inda shugaban ƙasa mai shekaru 92, Paul Biya — wanda shi ne tsohon shugaban ƙasa mafi tsufa a duniya — yake neman wa’adi na takwas a mulki.
Biya, wanda ya shafe shekaru 43 yana mulkin ƙasar, ya fafata da ’yan takara 11, ciki har da tsoffin muƙarrabansa.
Ɗaya daga cikinsu shi ne Issa Tchiroma Bakary, tsohon ministan ma’aikata wanda ya yi murabus daga gwamnati a watan Yuni bayan fiye da shekaru 20 yana aiki tare da Biya.
Bakary, mai shekaru 79, ya zama babban abokin hamayyar Biya bayan Kotun Tsarin Mulki ta ƙi amincewa da takarar fitaccen ɗan adawa Maurice Kamto — matakin da ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan Adam ciki har da Human Rights Watch suke cewa ya rage sahihancin tsarin zaɓen.
Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku Yajin Aikin ASUU: Ba za mu biya duk wanda bai yi aiki ba — Gwamnatin Tarayya Matasa da dogon mulkiKamaru na da masu kaɗa ƙuri’a kusan miliyan takwas, yawansu matasa da ba su taɓa sanin wani shugaban ƙasa ba sai Biya, tun da ya hau mulki a 1982.
A cikin shekaru 20 da suka gabata, Biya yakan lashe zaɓe da sama da kashi 70 na ƙuri’u.
Bayan ya jefa ƙuri’arsa a kusa da fadar gwamnati a Yaounde, Biya ya ce wa manema labarai: “Ba a san komai ba tukuna. Mu jira mu ga wanda aka zaɓa.”
Wani jami’in hukumar zaɓe ta ƙasa, Jean-Alain Andzongo, ya shaida wa AFP cewa an gudanar da zaɓen cikin kwanciyar hankali da tsari a babban birnin.
Mai sharhi kan harkokin siyasa, Stephane Akoa, ya ce duk da cewa jam’iyyar mai mulki na da damar ganin ta sami nasara, wannan yaƙin neman ya kasance “mai ɗan ɗumi fiye da yadda aka saba,” yana nuna yiwuwar “samun wasu abubuwan mamaki.”
’Yan takara da yaƙin neman zaɓeBiya bai yi fitowa sosai ba a lokacin yaƙin neman zaɓe, inda ya bayyana sau ɗaya kacal a wani babban gangami a Maroua, a yankin Arewa Mai Nisa — inda akwai masu kaɗa ƙuri’a miliyan 1.2.
Sai dai wannan yankin da aka daɗe ana ɗauka matsayin ginshikin goyon bayansa, yanzu wasu tsoffin abokansa ne ke takara da shi daga yankin.
’Yan adawa sun gudanar da gangami a sassa daban-daban na ƙasar, suna alkawarin kawo sauyi ga al’ummar Kamaru.
A yayin da Biya ya tara ’yan ɗaruruwan mutane kaɗan a gangaminsa, Bakary kuwa ya samu tarbar dubban magoya baya a yankin da ya fito, suna ɗaga tutoci masu taken “Tchiroma Mai Ceto.”
Tattalin arziki da ƙorafin jama’aDuk da albarkatun ƙasar – musamman noma da ma’adinai – Kamaru na ci gaba da fama da talauci da rashin aikin yi.
Bisa ga rahoton Bankin Duniya (2024), kusan kashi 40% na ‘yan ƙasar na rayuwa ƙasa da layin talauci, yayin da rashin aikin yi ya kai kashi 35% a manyan birane.
Jama’a na ci gaba da koka kan tsadar rayuwa, ƙarancin ruwan sha mai tsafta, rashin ingantaccen kiwon lafiya da kuma matsalolin ilimi.
Matasa da neman sauyiAkoa ya bayyana cewa matasan Kamaru na ƙaunar ganin sauyi, amma har yanzu ba su kai matakin yin zanga-zanga kamar yadda ake gani a wasu ƙasashe na Afirka da Asiya ba.
Ya ce: “Yawancin matasa sun nuna niyyar kaɗa ƙuri’a. Wannan alama ce mai kyau, amma ba ta kai matakin tayar da gagarumin yunƙuri irin na Madagascar ko Tunisia ba.”
Sauran bayanai da sakamakon zaɓeGwamnatin Kamaru ta bai wa masu lura da zaɓe kusan 55,000 — ciki har da wakilan Kungiyar Tarayyar Afirka (AU) — damar sa ido kan zaɓen.
Kotun Tsarin Mulki na da wa’adin Oktoba 26 don fitar da sakamakon ƙarshe.
Sai dai wasu kafafen sada zumunta sun sanar da shirinsu na tattara sakamako da kansu — abin da gwamnati ta soki, tana zargin suna ƙoƙarin karkatar da ra’ayoyin jama’a.