Aminiya:
2025-08-11@06:11:29 GMT

Yaran Bello Turji sun ƙwace garin su tsohon Gwamnan Sakkwato, Bafarawa

Published: 12th, May 2025 GMT

’Yan bindiga da ake zargin yaran fitaccen jagoran ’yan bindiga Bello Turji ne, sun ƙwace yankin Bafarawa, garin su tsohon gwamna Attahiru Dalhatu Bafarawa.

’Yan bindigar sun kai harin tare da ƙwace wasu ƙauyuka huɗu ne a ranar Asabar a Ƙaramar Hukumar Isa ta Jihar Sakkwato.

Harin, wanda ake zargin wani kwamandan Turji mai suna Danbakolo ne ya jagoranta, ya kuma shafi ƙauyukan Gebe, Kamarawa, Garin Fadama da Haruwai.

Ana zargin harin da aka kai da kusan ƙarfe 11 na safe ran Asabar, martani ne ga ayyukan sojoji na baya-bayan nan da suka yi niyyar fatattakar ’yan bindiga a yankin.

NAJERIYA A YAU: Gaskiyar Tasirin Amfani Da Irin Noma Na GMO NDLEA ta kama matar da ta ɓoye hodar iblis a al’aurarta

Majiyoyi a yankin sun ce an kashe mutane uku—ciki har da wata mata da ɗanta—a lokacin harin, wanda wasu mazauna ke zargin na hannun Turji ne ya jagoranta.

Maharan sun yi wa Bafarawa ƙofar rago, inda suka zargi mazauna da bai wa sojoji bayanan sirri.

Wani mazaunin yankin ya shaida wa wakilinmu cewa maharan, “Sun tafi kai tsaye fadar Sarkin Gabas na Bafarawa, Alhaji Muhammad Dalhatu, wanda shi ne babban ɗan uwan tsohon gwamnan.

“Sun yi ta neman sa, sun tafi da kuɗinsa da wayoyinsa, kuma sun yi wa al’umma gargadi game da haɗa kai da jami’an tsaro.”

Mazauna ƙauyukan da abin ya shafa sun gudu zuwa garin Shinkafi da ke kusa domin tsira.

Sai dai rahotanni sun ce sojoji sun ƙarfafa musu gwiwa da su koma gida a ranar Lahadi, tare da ba su tabbacin ingantaccen tsaro.

Lokacin da aka tuntube shi domin jin ta bakinsa, kakakin ’yan sanda na Jihar Sakkwato, DSP Ahmad Rufa’i, ya musanta faruwar lamarin.

Ya ce, “Ba na tunanin akwai wani abu kamar haka saboda akwai jami’an tsaro da yawa a waɗannan yankunan.”

Duk da musantawar, majiyoyi da yawa sun tabbatar da cewa hare-haren sun faru kuma sun bar mazauna cikin tsoro.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Bafarawa Sakkwato

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta, Sun Kashe Ƴan Ta’adda A Borno

Rundunar Sojin Sama ta ƙasa (NAF) ta daƙile harin da ’yan ta’adda suka shirya kai wa sansanin Sojoji a Rann, jihar Borno, tare da kashe da dama daga cikinsu yayin da suke tserewa.

Mai magana da yawun NAF, Ehimen Ejodame, ya bayyana cewa dakarun saman ƙarƙashin Operation Haɗin Kai (OPHK) sun hana harin ne da safiyar 8 ga Agusta, 2025, ta hanyar samun bayanan leƙen asiri da kai farmaki daga sama.

Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

An gano tarin ƴan ta’adda da ke gudu bayan samun bayanan sirri, sannan aka fatattake su da makamai na musamman, inda aka hallaka da dama daga cikinsu.

Ejodame ya ce wannan matakin gaggawar da aka ɗauka ya dawo da zaman lafiya a yankin, yana kuma nuna jajircewar NAF wajen kare Sojoji da shawo kan barazanar ƴan ta’adda cikin hanzari.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun kama wasu kan zargin kitsa juyin mulki a Mali
  • Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara
  • ’Yan bindiga sun kashe gomman mutane a ƙauyukan Sakkwato
  • MDD za ta yi zaman gaggawa kan yunƙurin ƙwace Gaza
  • Ana Alhinin Tunawa Da Harin Nukiliyar Nagasaki Shekarau 80 Da Suka Gabata A Japan
  • Tinubu ya yi alhinin rasuwar tsohon shugaban PDP, Audu Ogbeh
  • Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi
  • Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta, Sun Kashe Ƴan Ta’adda A Borno
  • ’Yan damfara 2 sun shiga hannun ’yan sanda a Yobe
  • Ba Gaskiya Ba Ne Rahoton Da Ke Cewa An Yi Sulhu Da Bello Turji – Guyawa Isa