HausaTv:
2025-06-24@21:44:33 GMT

 An Zabi Robert Francis  Dan Asalin Amurka A Matsayin Paparoma

Published: 9th, May 2025 GMT

A jiya Alhamis ne dai majami’ar Roman Katolika ta sanar da zabar Robert  Farncis wanda ya zabi sunan Leo 14,a matsayin shugabanta.

Zabar Robert Francis a matsayin Paparoma na 267 ya zo ne bayan kwanabi 2  da manyan malaman addinin majami’ar Roman katolika su ka dauka suna yin zaben.

 A bisa al’adar majalisar, farin hayaki yana fitowa daga saman majami’ar da yake nuni da cewa an zabi sabon Paparoman, da hakan ya sa a ka rika kada karaurawa a cikin maja’mi’un birnin Roma.

Sabon Paparoman  dan shekaru 69 ya zabarwa kansa sunan  Leo 14 domin sake dawo da aiki da kyawawan halaye a cikin harkokin tafiyar da majami’ar kamar yadda Leo na farko ya yi a 1878 zuwa 1903.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Nijeriya ta yi wa Amurka martani kan barazanar tsaro a Abuja

Gwamnatin Nijeriya ta ce babu wata barazanar tsaro a babban birnin ƙasar, Abuja, inda ta yi kira ga mazauna birnin su ci gaba da gudanar da harkokinsu na yau da kullum cikin lumana.

Nijeriya ta musanta batun yiwuwar kai hari kan ’yan Amurka da suke zaune a kasar, sakamakon rikicin da ke faruwa a yankin Gabas ta Tsakiya.

Mali ta ƙulla yarjejeniyar nukiliya da Rasha Trump ya soki Iran da Isra’ila kan saɓa wa yarjejeniyar tsagaita wuta

Gwamnatin ta bayyana haka ne a matsayin martani dangane da gargaɗin tsaro da Amurka ta aika zuwa ga ’yan ƙasarta da ke birnin Abuja.

A sanarwar da Ministan Watsa Labarai na Nijeriya, Mohammed Idris ya fitar, ya ce, “Gwamnatin Nijeriya ta samu labarin gargaɗin da Amurka ta aika wa ma’aikatan ofishin jakadancinta da ma ’yan ƙasarta da ke Abuja game da tsaro.

“Duk da Gwamnatin Nijeriya na girmama haƙƙin da ofisoshin jakadanci — ciki har da na Amurka — ke da shi na ba ’yan ƙasarta shawara ko gargaɗi game da matsalolin tsaro, yana da muhimmanci mu tabbatar da cewa babu wata barazanar tsaro da Nijeriya ke fuskanta, sannan mazauna birnin da masu ziyara babu wata barazana da suke fuskanta.”

Sanarwar ta ƙara da cewa babu dalilin wannan gargaɗi saboda akwai cikakken tsaro a Abuja, “domin jami’an tsaro suna aiki ba dare ba rana domin tabbatar da daƙile dukkan wata barazanar tsaro.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Nijeriya ta yi wa Amurka martani kan barazanar tsaro a Abuja
  • Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Mako 3
  • Iran ta ƙaddamar da hare-hare kan sansanonin sojin Amurka
  • Amurka ta roƙi China ta sa baki kada Iran ta rufe mashigar tekun Hormuz
  • Bio ya maye gurbin Tinubu a matsayin sabon shugaban ECOWAS
  • Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona
  • Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?
  • Matsalolin Rayuwa: Matasan Suleja Na Buƙatar Ƙarfafa Gwuiwa
  • Firaministan Singapore: Jama’ar Sin Suna Da Kwarewar Kirkire-Kirkiren Fasahohi
  • Amurka ta ƙaddamar da hare-hare kan Iran