Yadda matsalar wutar lantarki ke ajalin rayuka a manyan asibitoci
Published: 9th, May 2025 GMT
Matsalar wutar lantarki a asibitoci a Najeriya ta jefa marasa lafiya cikin halin ni-’yasu, lamarin da ke kara ta’azzara halin da majinyata ke ciki, har ta kai ga asarar rayuwa.
Rashin wuta ya yi sanadin mutuwar jariri a cikin wata mai juna biyu, wata ta yi awa 15 tana jiran a yi mata tiyatan haihuwa, wata kuma ta mutu sakamakon dauke wuta a yayin da ake tsada da yi wa mata tiyata, a Asibitin Jummai Babangida Aliyu, da ke jihar Neja.
’Yan uwa sun shaida wa wakilinmu cewa an shafe sama da kwana uku a jere babu wutar lantarki a asibitin gwamnatin, a yayin da rashin wuta da yanayi na tsananin zafi ya tilasta wa ’yan uwan majinyata amfani da fankoki masu amfani da caji domin samun iska a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano da ke Jihar kano.
Bincikine wakilanmu ya gano matsalar lantarkin na kawo tsaiko ga gudanar a tiyata da ayyukan karbar haihuwa da awon masu juna biyu a asibitoci.
Masan sun ƙalubalanci sojoji kan maharan ƙasashen waje NAJERIYA A YAU: Abin ya sa aka kasa kawo ƙarshen Tamowa a Arewa Maso GabasMajinyata a asibitocin da muka ziyarta sun bayyana cewa rashin wutar ta sa ana dage lokacin da aka shirya yi musu tiyata baya ga kawo tsaiko ga sauran nau’ikan aikin kula da lafiya.
Wannan matsala ta shafi asibitocin koyarwa, inda yawan kudin wutar da ake kamfananonin rarraba lantarki ke bin su ya yi yi musu katutu. Shugabannin asibitocin koyarwar sun bayyana cewa sun yi kokari biyan bashin, amma duk da haka sai sun kara neman wasu kudaden domin samar wa wata hanyar samun lantarki, saboda matsalar rashin samun wutar gwamnati da ta ki ci ta ki cinyewa.
A cikin wannan hali, a watan Fabrairu Ministan Lantarki, Adebayo Adelabu, ya sanar da shirin sake kara kudin wutar, bisa hujjar cewa gwamnati ba za ta iya ci gaba da biyan tallafin lantarki ba.
‘Dauke wuta ana yi wa matata tiyata ya yi ajalinta’A kwanan baya ne wani magidanci a Jihar Neja, Umar B. Shehu ya wallafa a shafinsa na Facebook, yadda dauke wutar da aka yi a yayin da ake tsaka da yi wa matsarsa tiyatar kabar ciki, ya yi sanadiyyar mutuwarta a Babban Asibitin Jummai Babangida da ke garin Minna, hedikwatar jihar.
Malam Umar ya ce, bayan minit biyar da fara yi wa matarsa, Ummi Yusuf Makusidi tiyata, “NEPA suka dauke wuta kuma babu mai a injin janareton bangaren aikin tiyatan da ke Asibitin Jummai Babangida Aliyu.
“Bayan minti biyar aka kawo mai, bayan an zuba kuma sai janareto ya ki tashi, sai da aka nemo makanike. Duk matata tana cikin dakin tiyata, wata mai aikin jinya ta ce kada in damu an ci gaba da aikin ba tare da wutar lantarki ba, suna amfani da abin haskawa — cocila — kamar yadda suka saba.
“Bayan da makaniken ya zo kuma, akwai abubuwan da dole sai ya je ya sayo a unguwar Ogbomosho da ke Minna. Duk dai matata tana cikin dakin tiyata.
“Bayan awa daya aka dawo da wuta, amma makaniken yana kan gyaran janareto. A haka a ci gaba da aikin tiyata. Aikin da bai wuci ya dauki awa daya da rabi ba, tun karfe hudu na yamma sai da ya kai karfe 7 da dare.”
A lokacin da wakilinmu ya ziyarci asibitin da misalin karfe biyar na yamma ranar Asabar, ya lura babu wutar lantarki a daukacin asibitin. ’Yan uwan ajinyata da ke asibitin sun shaida masa cewa kwanansu uku babu wutar lantarki a asibitin, likitoci sun tura wasu, musmman mata masu juna biyu da ke nakuda zuwa asibitocin kudi.
Awa 15 muna jiran tiyataWani magidanci mai suna Ali Isah, wanda ya shaida mana yadda ’yarsa ta shafe awa 15 tana jiran a yi mata tiyata bayan an biya kudin aikin a asibitin.
Ya ce, “an kawo nan ne da misalin karfe 3 na dare za ta haihu. Nas ta shaida mana cewa aikin CS za a yi mata, amma ga shi yanzu karfe biyar na yamma, ba a yi aikin ba, kuma mun biya N40,000 kudin aikin.
“Dan uwana ya ba mu shawara mu je asibitin kudi, amma mun riga mun biya kudi a nan asitin na Jummal Babangida.”
Dan uwan wani mara lafiya a asibitin ya ce, “da ya mutu a cikin wata mai juna biyu ranar Juma’a bayan sun shafa awanni suna jiran a yi mata aiki, ba a yi ba. Dalilin da suka bayar shi ne rashin wutar lantarki da ruwa.
“Mijin matar da kansa ya sayo ruwa amma suka ce babu wuta. Kafin a tura matar zuwa Asibitin MI Wushishi, dan ya riga ya mutu. Yanzu kwana uku ke nan babu wuta a nan asibitin,” in ji shi.
Laifin lalacewar tiransufoma ne — Gwamnatin NejaMun tuntubi Gwamnatin Jihar Neja inda Kwamishinan Kula da Lafiya a Mataki mai Zurfi, Bello Tukur ya musanta cewa rashin wutar lantarki na kawo cikas wajen gudanar da ayyuka a asibitin.
Ya ce, “Ba gaskiya ba ne, tiransufoma ne ya samu matsala, kuma an kira Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na AEDC su zo su duba, bayan sun duba suka ce dole sai Kamfanin Samar da Wutar Lantarki na Kasa (TCN) ya zo ya duba layin wutar.
“Mun riga mun biya kudin da ake bukata kuma yanzu haka suna aikin. Muhimman sassan asibitin kamar bangaren haifhuwa da dakin haihuwa da bangaren masu jego suna da janareto.
“Ba za a iya kunna babban janareton da ke iya daukar asibitin gaba daya ba, saboda dole sai wutar ta bi ta babban layin, wanda shi ne ya lalace. Yanzu haka ma’aikatan AEDC da TCN na aikin gaya domin ganin ya ci gaba da aiki a asibitin.
Majinyata na zuwa da fankokinasu Asibitin Aminu KanoWani mara lafiya a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano da ya bayyana sunansa a matsayin Malam Umar, ya ce, “Marasa lafiya na amfani fankokinsu masu daukar caji a sibitin, saboda zafi, idan aka dauke wuta.
“Babu wutar sola, shi ya sa aka dauki lokaci idan aka dauke wuta kafina dawo da ita ko a kunna janareto.”
Wakilimu ya lura cewa an samar da wutar lantar mai amfani da hasken rana a dakin kula da lafiya na gaggaaw da wadanda suka yi hadari.
Dalilin da muka ninka kudin aiki — Asibitin AKTHShugaban Kwamitin Shawarwari na Asibitin, Farfesa Muhammad Abba Suwaid, wanda ya yi magana a madadin shugaban asibitin, Farfesa Abdurrahman Abba Sheshe, ya ce asibitin na shan man fetur na Naira miliyan 30 zuwa miliyan 100 a kowane wata, amma ba zai iya biyan abin da ya fi kashi 30% na kudin ba, shi ya sa a yanzu haka ake bin su bashi da ya kai naira miliyan 700 na kudin wuta.
“Wannan ya shafi yadda ake kula da majinyata, saboda dole ta sa asibitin kara kucin aiki da kashi 100% domin mu iya biyan kudin, amma hakan ma ya gagar.
“Hukumar gudanarwar asibitin na shirni sanya wuta mai amfani da hasken rana a wurare masu muhimmanci da suka hada da dakunan tiyata da wurin jinya mai tsanani da wasu dakunan majinyata.”
Jinkirin gwaji ya yi ajalin kawuna — LadiWata wadda aka garzaya da kawunta wani asibitin gwamnati ranga-ranga a bara, Ladi Adukwu, ta ce likitoci sun tura su a yi masa hoto ranar Asabar, amma ma’aikatan sashen suka ce a jira sai ranar Litinin da safe za a yi.
Ladi ta ce, washegari, ranar Lahadi da safe kawun nata ya rasu. “Da an yi masa a ranar, wata kila da an gano abin da damun an yi masa magani kafin hakan ta kasance.”
Daga Ojoma Akor (Abuja) Ahmad Datti (Kano) Adebyo Gbenga (Legas), Abubakar Akote (Minna).
Fassara: Sagir Kano Saleh
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: lafiya Tiyata wutar lantarki a rashin wuta
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna
“Mutanen duk sun manta da ‘yan garancin da suka yi gaba dayansu suka shiga wani sabon babi. Babban bango da ake ingina da shi ya fadi. Yanzu Kudancin Kaduna na jam’iyyar APC ne.”
Ya yi bayanin komawar manyan mutanen biyu zuwa APC wani kokarin ci gaba ne na shi Kakakin majalisar, ya ce SHugaban majalisar ya kara jadddad Sanata Katung da Honorabul. Amos “sun zabi lamarin kawo ci gaba ne. Sun zabi su ci gaba da kasancewa da Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ne da kuma APC. Wannan ba karamin sauya jam’iyya bane. Jirgizar kasa ce ta siyasa. Wani sabon babi ne ga siyasar Kudancin Kaduna, da kuma gaba dayan Nijeriya.”
“’Yan ‘uwana maza da mata wannan sauay shekar wani sako ne, wanda yake nuna lokacin rarrabuwar kai ya kare. Sako ne da yake nuna al’ummar kudancin Kaduna sun shirya tsaf, su kara yin ci gaba saboda ciyar da ci gaban Nijeriya.Sako ne da yake nuna APC yanzu wuri ne na hadin kai, wurin sa kai, da kuma ci gaba.
“Shugaban kasa ya nuna cewar a shirye yake wajen ci gaban Kudancin na Kaduna. Ya saurari kukan da aka dade na yi na kada a manta da su a rika tafiya tare da su, ya kuma yi abinda ya kamata wajen share masu hawaye da, yin ayyukan da suka dace.
“Jami’ar kimiyya ta gwamnatin tarayya da aka yi a Kachia, da wannan mulkin na Tinubu yayi wata manuniya ce mai nuna cewar da akwai fata ta gari da kuma farfado da sha’anin ci gaba. Bada dadewa za ta budewa dalibai hanya domin a fara daidata hanyar data kamata wajen zakulo masu ilimin kimiyya a nan gaba kadan, wadanda za su rika bullo da abubuwan ci gaba da kuma tunanin da me da me suka kamata ayi.
“Kafa Asibitin gwamnatin tarayya a Kafanchan ya nuna cewa gwamnatin ta damu kwarai akan kowa da kowa lamarin kula da lafiyar al’umma. Wajen kawo saukin samun inda za aje domin kulawa da lafiya cikin sauki da kuma daukaka lamarin kula da lafiyar al’umma na Kudancin Kaduna.
“Hakanan ma kafa barikin sojoji a Samarun Kataf wani sabon babi ne na kokarin samar da zaman lafiya da tsaro aka sa a gaba. Yin hakan ya nuna matuka gwamnati ta shirya kamar yadda ya dace wajen kare rayuwar al’umma, da wuraren da suke zama, da kuma kwantar masu da hankali na nuna an damu da tsaron wurin da kwanciyar hakalin al’ummar da suke wurin.
“Duk wadannan suna ganin gaskiya da akwai adalci wajen tunawa da su al’ummar wajen.Hakan ya nuna Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu yana tafiyar da jagorancinsa na cika alkawari wajen yin abubuwan da suka dace. Shi Shugaba ne mai yin abinda ya yi kuduri a zuciyarsa kawo ci gaba wurin daya dace matuka.”
Shugaban har ila yau ya tabbatar da an sa ko kuma daukar ‘yan asalin wurin wato Kudancin Kaduna wuraren da za su kawo ci gaban wurin ta hanyar la’akari da menene muradin Shugaban kasa akan lamarin da ya shafi wurin.
“An nada Bishop Matthew Hassan Kukah a matsayin jagora kuam Shugaba na wadanda za su jagorancin tafiyar ta jami’ar kimiyya ta gwamnatin tarayya, Kachia. Farfesa Kurid Williams Barnabas shi ne mataimakin Shugaban jami’ar na farko.Wadannan nade- naden wata girmamawa ce ta Kudancin Kaduna. Don haka hakan ya nuna ana lura matuka ga lamarin daya shafi kwarewa da kuma aiwatar da gaskiya.”
Shugaban majalisar Wakilai Abbas yace maganar gaskiya Gwanan Jihar Kaduna Sanata Uba Sani“a matsayi wani mutum ne da yake bada gudunmawar ci gaba,”inda ya kara da cewa’ “yadda yake tafiyar da lamurran gwamnatinsa tamkar budewa kowa kofa ne ya shigo a tafi tare da shi, saboda ya daidaita kawunan al’umma wadanda a shekarun baya basu ga Maciji da juna. Ya daukaka ci gaba da nuna ya fi duk wani lamarin siyasa da kuma hada kai maimakon, maida hankali kan ita siyasar.”
A kowane lokaci Shugaban majalisa yana yiwa ‘yan kudancin Kaduna a matsayin ‘yan’uwansa ne maza da mata, “Irin soyayyar da yake yiwa yankin ta nuna lamarin ya dade tare da samun ranar cika kudurin. Abokantakar da yake da Shugabannin wurin wani abu ne wanda ya kunshi biyayya da kuma amana da mutunta juna.
“Aiki tare da Shugaban kasa Tinubu, mun tabbatar da cewa kasafin kudin 2025 da aka yiwa shi sashen na Kudancin Kaduna wani sabon babi ne mai nuna lalle ba a manta dasu ba. Kudancin Kaduna yanzu wani wuri ne na ci gaban kasa. Ayyukan da aka yi ba ayi su bane domin saboda yau kadai bane. Tamkar wani zuba jari ne aka yi saboda gaba. Saboda ayyukan za su ilimantar bunkasawa da daukakawa, da kuma samarwa al’ummar yadda za su san mutane domin ai kowa ya san sabo, da Maza ma jari ne saboda gaba.
Ya gode wa Shugaban majalisar Tajudden Abbas saboda yadda yake aiki tare da shi domin tabbatar da ba a manta da kowa ba wajen samar da ayyukan gwamnati, saboda kamar yadda ya ce sun samu nasarori cikin shekaru biyu da rabi da suka gabata.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA