Indiya da Pakistan sun cimma yarjejeniyar tsagaita wuta
Published: 11th, May 2025 GMT
Kasashen Indiya da Pakistan sun tabbatar da cimma yarjejeniyar tsagaita wuta bayan shafe kwanaki suna yi wa juna luguden wuta da makaman atilare.
Shugaban Amurka Donald Trump ne ya sanar da cewa ƙasashen biyu maƙwabta sun amince su cim ma yarjejeniyar tsagaita wuta nan take bayan shafe dare guda ana tattaunawa.
“Bayan doguwar tattaunawa da Amurka ta yi na a cikin dare, ina farin cikin sanar da cewa Indiya da Pakistan sun amince da tsagaita wuta cikin gaggawa.
“Ina taya ƙasashen biyu murna a kan amfani da hankalinsu da kuma basira,” kamar yadda Trump ɗin ya bayyana a shafinsa na Truth Social.
Shi ma Ministan Harkokin Wajen Pakistan Ishaq Dar ya tabbatar da maganar Trump ɗin a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X inda ya ce “Pakistan da Indiya sun amince da tsagaita wuta da gaggawa. Pakistan a ko da yaushe tana kokarin tabbatar da zaman lafiya da tsaro a yankin, ba tare da ƙasa a gwiwa kan ƙarfin ikonta da maratabar ƙasarta ba!
Ita ma Ma’aikatar Harkokin Wajen Indiya ta tabbatar da batun tsagaita wutar inda ta ce yarjejeniyar za ta fara aiki ne a ranar Asabar da misalin 1700 agogon Istanbul.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Indiya tabbatar da
এছাড়াও পড়ুন:
Pezeshkian: Kasashen Da Ba Su Cika Alkawura Da Suka Dauka Ba Suke Zargin Iran Kan Rashin Mutanta Yarjejeniyar Nukiliya
Shugaban kasar Iran ya bayyana cewa: Kasashen da ba su cika alkawuran da suka dauka ba suke zargin Iran da rashin mutunta yarjejeniyar makamashin nukiliya
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya bayyana cewa: Kasashen da ba su cika alkawuran da suka dauka ba, a yanzu suke zargin Iran da kin mutunta yarjejeniyar makamashin nukiliyar.
A cikin wata hira da gidan talabijin na CCTV na kasar China, Pezeshkian ya ce, “Suna sa ran za a aiwatar da yarjejeniyar manyan tsare-tsare na shekaru 25 da aka tsara a baya tsakanin Iran da China.”
Pezeshkian ya yi ishara da gazawar Amurka da kasashen Turai wajen cika alkawuran da suka dauka karkashin yarjejeniyar makamashin nukiliya, yana mai cewa, a yau kasashen da ba su cika alkawuran da suka dauka ba, suna zargin Iran da kin mutunta yarjejeniyar makamashin nukiliyar.
Yayin da yake ishara da irin hadin gwiwar da Iran ke yi da hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa, ya ce, ba su da niyyar yin aiki ba bisa tsarin hukumar kula da makamashin nukiliya ba ta IAEA.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Dakarun IRGC: Iran Za Ta Tarwatsa Makiya Tare Da Mayar Da Martani Kan Duk Wani Zalunci September 22, 2025 Kungiyar Ansarullahi Ta Yemen: ‘Yan Koren Amurka Da Isra’ila Suke Neman Wargaza Hadin Kan Larabawa Da Na Musulmi September 22, 2025 Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Aiwatar Da Kisan Gilla Kan Fararen Hula 5 A Kudancin Kasar Lebanon September 22, 2025 Ministan Harkokin Waken Falasdinu Ta Yi Kira Ga Karin Kasashe Su Amince Da Samuwar Kasarta September 21, 2025 Iran Da Pakistan Sun Sake Tsara Dangantakarsu Ta Tattalin Arziki September 21, 2025 Trump Ya Bukaci Afganistan Ta Mayarwa Amurka Sansanin Jiragen Sama Na bagram September 21, 2025 Kasashen Ingila Da Canada Da Kuma Australia Sun Bayyana Amincewarsu Da Samuwar Kasar Falasdinu September 21, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya Yi Kira Ga Samar Da Tattalin Arziki Da Shugabancin Kwararru September 21, 2025 Arakci Ya Kore Cewa Ya Zanta Da Steven Witkoff Na Amurka September 21, 2025 Hizbullah Ta Yi Gayyar Tunawa Da Zagayowar Shahadar Sayyid Hassan Nasrallah September 21, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci