Aminiya:
2025-05-11@04:05:03 GMT

Indiya da Pakistan sun cimma yarjejeniyar tsagaita wuta

Published: 11th, May 2025 GMT

Kasashen Indiya da Pakistan sun tabbatar da cimma yarjejeniyar tsagaita wuta bayan shafe kwanaki suna yi wa juna luguden wuta da makaman atilare.

Shugaban Amurka Donald Trump ne ya sanar da cewa ƙasashen biyu maƙwabta sun amince su cim ma yarjejeniyar tsagaita wuta nan take bayan shafe dare guda ana tattaunawa.

Matsalar Tsaro: Zulum ya haramta sayar da man fetur a Bama Gidauniya ta yi wa masu cutar gwaiwa dubu 12 tiyata kyauta a Katsina

“Bayan doguwar tattaunawa da Amurka ta yi na a cikin dare, ina farin cikin sanar da cewa Indiya da Pakistan sun amince da tsagaita wuta cikin gaggawa.

“Ina taya ƙasashen biyu murna a kan amfani da hankalinsu da kuma basira,” kamar yadda Trump ɗin ya bayyana a shafinsa na Truth Social.

Shi ma Ministan Harkokin Wajen Pakistan Ishaq Dar ya tabbatar da maganar Trump ɗin a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X inda ya ce “Pakistan da Indiya sun amince da tsagaita wuta da gaggawa. Pakistan a ko da yaushe tana kokarin tabbatar da zaman lafiya da tsaro a yankin, ba tare da ƙasa a gwiwa kan ƙarfin ikonta da maratabar ƙasarta ba!

Ita ma Ma’aikatar Harkokin Wajen Indiya ta tabbatar da batun tsagaita wutar inda ta ce yarjejeniyar za ta fara aiki ne a ranar Asabar da misalin 1700 agogon Istanbul.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Indiya tabbatar da

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Da Take Kula Da Nukiliyar Pakistan Za Su Yi Taron Gaggawa

Fira ministan kasar Pakistan Shahbaz Sharif ya kira yi Majalisar kasa wacce take kula da makaman Nukiliyar kasar  da su yi taro.

Wannan matakin da ake yi wa Kallon mai hatsari yana faruwa ne a daidai lokacin da kasar ta Pakistan take yaki da Indiya.

Ita  dai Majalisar  kasar Pakistan dake kula da makaman Nukiliya da kuma manufofin kasa na koli, ta kunshi manyan kwamandojin soja, da fararen hula, aikinta kuma  shi ne kula da manyan batutuwa da su ka shafi kasa daga ciki har da siyasar makaman Nukiliya da kuma makamai masu linzami.An kafa wannan majalisar ne dai a 2000.

Tashar talabijin din “Sama News” ta bayar da labarin dake cewa; Mahalarta taron za su yi bitar halin da ake ciki ne na yaki, da kuma tattaunawa matakan da za a dauka a fagen diplomasiyya da kuma hanyoyin tsaro da kare kai.

Ita dai kasar Indiya tana cewa ba za ta taba zama wacce za ta fara amfani da makamin Nukiliya ba, don haka ba za ta zama ta farko da za ta kai wa Pakistan hari ba. Ita kuwa Pakistan ta gina akidarta ta tsaro ne akan cewa za ta iya fara amfani da makamin Nukiliya da Zarar ta faminci cewa wanzuwar kasar tana fuskantar rushewa.

Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana aiki tukuru domin ganin ta shiga Tsakani da kawo karshen rikicin dake tsakanin kasashen biyu da suke makwabtanta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Amurka Ya Ce An Cimma Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Indiya
  • Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali
  • Jagora: Ma’aikata Su Ne Jari Mafi Girma Domin Cimma Manufar Bunkasa Tattalin Arziki
  • Majalisar Da Take Kula Da Nukiliyar Pakistan Za Su Yi Taron Gaggawa
  • Nijar da Iran sun cimma yarjejeniyar fahimtar juna a tsakaninsu
  • Aragchi: Muna Bukatar Rage Zaman Daradar Da Kuma Tabbatar Da Zaman Lafiya A Tsakanin Pakisatan Da Indiya
  • Amurka ta matsa wa ƙasashe da ke fuskantar haraji su amince da Starlink
  • Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah
  • Yemen Ta Jaddada Cewa: Idan Amurka Ta Kai Mata Hari, Tabbas Yarjejeniyar Kawo Karshen Bude Wuta Tsakaninsu Zata Ruguje