Idan aka ga tana da tasiri, ana iya tsawaita ko kuma daidaita matakin.

Masana tattalin arziƙi sun bayyana cewa wannan ci gaba zai iya taimakawa wajen farfaɗo da cinikayya tsakanin manyan ƙasashen biyu, kuma zai taimaka wa ƙasashe masu tasowa da ke dogara da su wajen kasuwanci da kayan masarufi.

Rikicin kasuwanci tsakanin Amurka da China ya fara ne tun daga 2018 lokacin da kowanne ɓangare ke ƙara haraji a kan kayayyakin juna, lamarin da ya haifar da hauhawar farashi da rikicin masana’antu a duniya.

Matakin rage harajin da suka ɗauka yanzu na iya zama sabon shafi na fahimtar juna da haɗin gwiwa a tsakanin manyan ƙasashen biyu na duniya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Kayayyaki Rage Haraji

এছাড়াও পড়ুন:

Dubban mutane sun yi zanga-zangar goyon bayan Falasɗinu a Isra’ila da Pakistan

Dubban mutane ne suka fito kan tituna a birnin Tel Aviv na Isra’ila ranar Asabar, domin yin kira da a kawo ƙarshen yaƙin Gaza, kwana guda bayan da gwamnatin Isra’ila ta lashi takobin faɗaɗa rikicin tare da ƙwace birnin Gaza.

Masu zanga-zangar da ke riƙe da hotunan waɗanda har yanzu ake garkuwa da su a yankin Falasdinawa sun yi kira ga gwamnati da ta tabbatar da sakin su ’yan uwansu.

Al-Hilal ta ɗauki Nunez daga Liverpool ASUU na shirin sake tsunduma yajin aiki

’Yan jaridar AFP a wajen gangamin sun ƙiyasta adadin waɗanda suka halarci taron a matsayin dubbai, yayin da wata ƙungiya da ke wakiltar iyalan wadanda aka yi garkuwa da su ta ce mutane kusan 100,000 ne suka yi dafifi.

Hukumomin ƙasar ba su bada wasu alƙaluma mutane da suka shiga zanga-zangar ba, amma sun hakikance lalai ya, zarta duk wasu gangamin da aka yi a baya na adawa da yakin.

Masu zanga-zangar sun ƙarkare da aike wa Firaminista Benjamin Netanyahu saƙo da kakkausar murya.

Shahar Mor Zahiro, ɗaya daga cikin waɗanda aka yi garkuwa da ɗan uwansa, ya shaida wa AFP cewar: “Idan ka mamaye sauran sassan Gaza kuma aka kashe sauran ’yan uwanmu da ake garkuwa da su, za mu bi ka har cikin harabar dandalin Square, ko a lokacin yakin neman zaɓe ko a kowane lokaci ko waje.”

A ranar Juma’ar da ta gabata, majalisar ministocin tsaron Netanyahu ta amince da gagarumin farmaki na kwace birnin Gaza, lamarin da ya janyo cece-kuce da tofin Allah tsine daga cikin gida da ƙasashen duniya.

Wasu ƙasashen ketare, ciki har da wasu kawayen Isra’ila, sun yi ta matsa kaimi don ganin an tsagaita wuta domin tabbatar da dawowar wadanda aka yi garkuwa da su da kuma taimakawa wajen rage matsalar jin kai a yankin.

Zanga-Zangar Goyon Bayan Falasɗinu a Istanbul

Dubban masu zanga-zangar goyon bayan Falasɗinu sun taru a Dandalin Beyazit na Istanbul a ranar Asabar bayan sallar Magariba, domin nuna adawarsu ga kisan kiyashi da ƙaƙaba yunwa da Isra’ila ke yi a Gaza.

Gangamin, wanda ya haɗa da ƙungiyoyin ba da gwamnati da kuma jama’a da dama, ya ci gaba da tafiya zuwa Masallaci mai tarihi na Ayasofya.

Mahalarta sun yi ƙoƙarin jan hankalin duniya game da matsalar jin kai da ke faruwa a Gaza, tare da nuna goyon baya gare su, yayin da tashin hankali da ƙarancin abinci da magunguna ke ƙara ta’azzara.

Masu shirya zanga-zangar sun yi kira ga al’ummar duniya da su ɗauki matakan gaggawa don kawo ƙarshen wahalhalun.

Isra’ila Na Fuskantar Matsin Lamba Daga Duniya

Isra’ila na fuskantar ƙarin fushin duniya saboda kisan kiyashi da take yi a Gaza, inda ta kashe fiye da mutane 61,000 tun watan Oktoba 2023.

Haren-haren da soja ke kaiwa sun lalata yankin sosai kuma sun haifar da mutuwa ta hanyar yunwa da ƙunci.

A watan Nuwamba da ya gabata, Kotun Hukunta Laifukan Yaƙi ta Duniya ta bayar da sammacin kama Firayiministan Isra’ila Benjamin Netanyahu da tsohon Ministan Tsaronsa Yoav Gallant saboda laifukan yaƙi da laifukan cin zarafin ɗan adam a Gaza.

Haka kuma, Isra’ila tana fuskantar shari’ar kisan kiyashi a Kotun Duniya saboda yaƙin da take yi a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Ta Raba Naira Miliyan 50 Ga Mata Da Matasa
  • Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna
  • Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe
  • Direba ɗaya ya tsira a hatsarin tankokin dakon iskar gas a Zariya
  • Tankokin mai sun yi bindiga a Zariya
  • Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam
  • An ɗaure tsohon Firaminista Succes Masra shekaru 20 a Chadi
  • Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho
  • Dubban mutane sun yi zanga-zangar goyon bayan Falasɗinu a Isra’ila da Pakistan
  • Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027