Idan aka ga tana da tasiri, ana iya tsawaita ko kuma daidaita matakin.

Masana tattalin arziƙi sun bayyana cewa wannan ci gaba zai iya taimakawa wajen farfaɗo da cinikayya tsakanin manyan ƙasashen biyu, kuma zai taimaka wa ƙasashe masu tasowa da ke dogara da su wajen kasuwanci da kayan masarufi.

Rikicin kasuwanci tsakanin Amurka da China ya fara ne tun daga 2018 lokacin da kowanne ɓangare ke ƙara haraji a kan kayayyakin juna, lamarin da ya haifar da hauhawar farashi da rikicin masana’antu a duniya.

Matakin rage harajin da suka ɗauka yanzu na iya zama sabon shafi na fahimtar juna da haɗin gwiwa a tsakanin manyan ƙasashen biyu na duniya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Kayayyaki Rage Haraji

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Nasarawa ya sanya wa gadar sama sunan Tinubu

Gwamnan Jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya sanya wa sabuwar gadar sama da aka kammala a Lafia, Babban Birnin Jihar, sunan Shugaba Bola Tinubu.

Gwamnan, ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin ƙaddamar da aikin a Lafia.

’Yan bindiga sun kashe ɗan sanda, sun jikkata wasu 3 a Zariya An ɗaure mutum 6 shekaru 120 kan satar yara a Kano

Ya ce an gina gadar bisa tsarin Shugaba Tinubu, kuma an kammala aikin ne ba tare da ciyo bashi ba, sakamakon inganta amfani da kuɗin gwamnati.

Sabuwar gadar mai tsawon kilomita ɗaya, wadda ke da gadar sama da ƙasa, na ɗauke da sunan ‘Bola Tinubu Exchange Road’.

A wajen buɗe aikin, Shugaba Tinubu ya gode wa Gwamna Sule bisa jajircewarsa wajen aiwatar da ayyukan da ke taimaka wa rayuwar al’umma.

Haka kuma, ya nuna farin cikinsa da irin tarbar da ya samu daga mutanen Nasarawa.

Sannan ya yi kira a gare su da su ci gaba da mara wa gwamnati baya wajen bunƙasa tattalin arziƙin ƙasa baki ɗaya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tirela ta afka cikin kasuwa ta kashe mutum da raunata 5 a Taraba
  • Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas
  • An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome
  • Sheikh Dahiru Bauchi ya cika shekara 101 a duniya
  • ’Yan sanda sun kashe ‘yan fashi da ƙwato makamai a Kaduna
  • Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja
  • Gwamnatin Gombe za ta sayi takin N8.8bn don tallafa wa manoma
  • Gwamnan Nasarawa ya sanya wa gadar sama sunan Tinubu
  • Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida
  • Gwamnatin Nijeriya ta yi wa Amurka martani kan barazanar tsaro a Abuja