Iran ta ce tattaunawa ta hudu da Amurka tana da wahala amma tana da amfani
Published: 11th, May 2025 GMT
Iran ta bayyana cewa tattauanwa ta hudu data wakana tsakaninta da Amurka tana da wahala amma kuma tana da amfani.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Esmaeil Baghaei ya ce zagaye na hudu na tattaunawar da Amurka abu ne mai wahala amma mai amfani ce.
M. Baghaei ya bayyana hakan ne a wani sako da ya wallafa a shafinsa na X a karshen zagaye na hudu na shawarwarin Tehran da Washington a babban birnin Muscat na kasar Omani yau Lahadi.
Ya kara da cewa Oman ne za ta sanar da lokaci da wurin da za a gudanar da shawarwarin na gaba.
A nata bangare Amurka ta bakin wani babban jami’inta da ya bukaci a sakaya sunansa ya bayyana cewa, sakamakon zagaye na hudu da aka yi da Iran kan shirin nukiliyar kasar ya karfafa gwiwar Amurka.
Tattaunawar da aka yi a birnin Muscat karkashin jagorancin wakilin Amurka a Gabas ta Tsakiya Steve Witkoff da ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi, ta dauki fiye da sa’o’i uku,” in ji jami’in.
“Sakamakon tattaunawar da muka yi a yau ya ba mu kwarin guiwa, muna kuma fatan haduwarmu ta gaba nan gaba kadan,” in ji shi.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Amurka Da HKI Sun Kawo Karshen Hukumar GHF Mai Raba Abinci A Gaza
The Gaza Humanitarian Ffoundatin (GHF) a Gaza ta bada sanarwan kawo karshen ayyukanta a Gaza makonni 6 bayan an fara abinda suke kira tsagaita wuta a Gaza.
Shafin yana gizo na labarai ‘ArabNews’ na kasar Saudiya ya nakalto shugaban hukumar John Acree yana fadar haka ya kuma kara da cewa hukumar ta cimma manufar kafata na rarraba abinci tsakanin Falasdinawa a Gaza wadanda suke mutuwa saboda yunwa bayanda HKI ta hana shigowar abinci Gaza na tsawon kwanaki kimani 90 ko watanni 3.
Gwamnatin kasar Amurka ta da HKI ne suka kafa hukumar bada agajin bayan sun kori dukkan kungiyoyin bada agaji a yankin. Sannan sun yi amfani da hukumar don kissin Falasdinawa wadanda suke takawa da kafa zuwa cibiyoyin bada abinci da suka kafa a wuraren da sai sun wuta ta gaban sojojin HKI wadanda suke bude masu wuta. Amma Falasdinawan basu da zabi ko yunwa ta kashe su a cikin gaza ko kuma su je su karbi abincin da mai yuwa ba zasu dawo ba har abada.
Amurka da HKI sun kashe daruruwan Falasdinawa a cikin wannan lokacin. Acree yace sun raba kunshi miliyon uku dauke da abinci miliyon 187 ga falasdinawa a lokacin.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Babban Kwamandan Sojojin Sudan Ya Yi Watsi Da Tsirin Trump Na Zaman Lafiya November 25, 2025 Hamas Ta Ce Keta Hurumin Tsagaita Wutan Da HKI Take Yi Zai Iya Kawo Karshen Tsagaita Wutar November 25, 2025 Gwamnonin Kudu Maso Yammacin Najeriya Sun Ce Lokacin Kafa Yansandan Jihohi Ya Yi November 25, 2025 Hizbullah Ta na Juyayin shahadar Babban Kwamanda Haitham Ali Da Isra’ila Ta Kashe. November 24, 2025 Dubban Alummar Kasar Tunisia Ne Suka Gudanar Da Zanga-zangar Adawa Da Mulkin Kama Karya A Kasar November 24, 2025 Mutane 6 Ne Suka Mutu Sakamakon Harin Kunar Bakin Wake Da Aka Kai A Peshavar Na Kasar Pakistan November 24, 2025 Hamas Tayi Gargadi Game Da Rushewar Yarjejeniyar Bude Wuta Idan Israila Ta ci Gaba Da Kai Hare-Hare November 24, 2025 Amnesty International Ta Zargi Najeriya Da Gazawa Wajen Kare Rayukan Al’ummarta November 24, 2025 Wakilin MDD Ya Bukaci Goyon Bayan Iran Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya A Yamen November 24, 2025 Yara 50 Da Aka Sace A Najeriya Sun Tsere Daga Hannun Barayin Daji November 24, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci