Iran ta bayyana cewa tattauanwa ta hudu data wakana tsakaninta da Amurka tana da wahala amma kuma tana da amfani.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Esmaeil Baghaei ya ce zagaye na hudu na tattaunawar da Amurka abu ne mai wahala amma mai amfani ce.

M. Baghaei ya bayyana hakan ne a wani sako da ya wallafa a shafinsa na X a karshen zagaye na hudu na shawarwarin Tehran da Washington a babban birnin Muscat na kasar Omani yau Lahadi.

Ya kara da cewa Oman ne za ta sanar da lokaci da wurin da za a gudanar da shawarwarin na gaba.

A nata bangare Amurka ta bakin wani babban jami’inta da ya bukaci a sakaya sunansa ya bayyana cewa, sakamakon zagaye na hudu da aka yi da Iran kan shirin nukiliyar kasar ya karfafa gwiwar Amurka.

Tattaunawar da aka yi a birnin Muscat karkashin jagorancin wakilin Amurka a Gabas ta Tsakiya Steve Witkoff da ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi, ta dauki fiye da sa’o’i uku,” in ji jami’in.

“Sakamakon tattaunawar da muka yi a yau ya ba mu kwarin guiwa, muna kuma fatan haduwarmu ta gaba nan gaba kadan,” in ji shi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Ce Kafa Hujja Da ‘Yan Tawaye Kan Iran Yankewar Kauna ce Ga Makiyanta

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Amfanin da fira ministan gwamnatin mamaya ya yi da ƙungiyar ta’addanci babbar alama ce ta cikakkiyar yanke ƙauna

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya jaddada cewa: Matakin da fira ministan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila Benjamin Netanyahu ya dauka na yi amfani da wata karkatacciyar kungiyar ta’addanci ta “MKO” wato kungiyar Munafukai wajen yada labaran karya game da shirin makamashin nukiliyar Iran, don tsoratar da al’ummar duniya kan Iran, wata babbar alama ce ta yanke kauna.

A sakon da ya wallafa shafinsa na X ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya bayyana cewa: Yayin da ake ci gaba da zaman tattaunawa ba na kai tsaye ba tsakanin Iran da Amurka, ana ci gaba da fitar da karin “hotunan tauraron dan adam don yada tsoro da fargaba kan Shirin makamashin nukiliyar Iran na zaman lafiya, inda ake murguda gaskiya zuwa karya.

Ministan harkokin wajen na Iran ya kara da cewa: Fira ministan haramtacciyar kasar Isra’ila Benjamin Netanyahu, a matsayinsa na mai neman kawo cikas da zagon kasa, ya yi amfani da dukkan tsoffi da sabbin ma’aikatan da ya dauka a matsayin wani bangare na manufofinsa na “kayyade ayyuka ga Trump.”

Araghchi ya ce: A wannan karon, Netanyahu ya koma yin amfani da bayin Saddam Hussain ‘yan kungiyar ta’addanci ta “MKO” da suka kasance kaskantattu su na shirya masa karairayi kan Shirin nukiliyar Iran, inda dogaro da rahotonnin kungiyar “MKO” babbar alama ce ta yanke ƙauna.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Da Amurka Sun Fahinci Juna Sosai A Zagaye Na 4 A Tattaunawa A Mascat
  • Trump Ya Bukaci Ukraine Ta Amince Da Tayin Putin Na Bude Tattaunawa A Birnin Istambul
  • Kungiyar Hamas Ta Amince Ta Saki Fursinan Yaki Wanda Yake Da Jinsiyar Amurka Da HKI
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Ce Kafa Hujja Da ‘Yan Tawaye Kan Iran Yankewar Kauna ce Ga Makiyanta
  • Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu
  • Yemen Tana Bukukuwan Samun Nasara Kan Amurka Kuma Zata Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Gaza
  • Jami’ar Colombiya Ta Birnin New York A Amurka Ta Dakatar Da Karatun Daliban Jami’ar Fiye Da 65
  • Amurka da Iran zasuyi tattaunawa ta hudu a ranar Lahadi
  • Ministan harkokin wajen Iran zai Ziyarci Saudiyya da Qatar