Iran ta bayyana cewa tattauanwa ta hudu data wakana tsakaninta da Amurka tana da wahala amma kuma tana da amfani.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Esmaeil Baghaei ya ce zagaye na hudu na tattaunawar da Amurka abu ne mai wahala amma mai amfani ce.

M. Baghaei ya bayyana hakan ne a wani sako da ya wallafa a shafinsa na X a karshen zagaye na hudu na shawarwarin Tehran da Washington a babban birnin Muscat na kasar Omani yau Lahadi.

Ya kara da cewa Oman ne za ta sanar da lokaci da wurin da za a gudanar da shawarwarin na gaba.

A nata bangare Amurka ta bakin wani babban jami’inta da ya bukaci a sakaya sunansa ya bayyana cewa, sakamakon zagaye na hudu da aka yi da Iran kan shirin nukiliyar kasar ya karfafa gwiwar Amurka.

Tattaunawar da aka yi a birnin Muscat karkashin jagorancin wakilin Amurka a Gabas ta Tsakiya Steve Witkoff da ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi, ta dauki fiye da sa’o’i uku,” in ji jami’in.

“Sakamakon tattaunawar da muka yi a yau ya ba mu kwarin guiwa, muna kuma fatan haduwarmu ta gaba nan gaba kadan,” in ji shi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Nijeriya ta yi wa Amurka martani kan barazanar tsaro a Abuja

Gwamnatin Nijeriya ta ce babu wata barazanar tsaro a babban birnin ƙasar, Abuja, inda ta yi kira ga mazauna birnin su ci gaba da gudanar da harkokinsu na yau da kullum cikin lumana.

Nijeriya ta musanta batun yiwuwar kai hari kan ’yan Amurka da suke zaune a kasar, sakamakon rikicin da ke faruwa a yankin Gabas ta Tsakiya.

Mali ta ƙulla yarjejeniyar nukiliya da Rasha Trump ya soki Iran da Isra’ila kan saɓa wa yarjejeniyar tsagaita wuta

Gwamnatin ta bayyana haka ne a matsayin martani dangane da gargaɗin tsaro da Amurka ta aika zuwa ga ’yan ƙasarta da ke birnin Abuja.

A sanarwar da Ministan Watsa Labarai na Nijeriya, Mohammed Idris ya fitar, ya ce, “Gwamnatin Nijeriya ta samu labarin gargaɗin da Amurka ta aika wa ma’aikatan ofishin jakadancinta da ma ’yan ƙasarta da ke Abuja game da tsaro.

“Duk da Gwamnatin Nijeriya na girmama haƙƙin da ofisoshin jakadanci — ciki har da na Amurka — ke da shi na ba ’yan ƙasarta shawara ko gargaɗi game da matsalolin tsaro, yana da muhimmanci mu tabbatar da cewa babu wata barazanar tsaro da Nijeriya ke fuskanta, sannan mazauna birnin da masu ziyara babu wata barazana da suke fuskanta.”

Sanarwar ta ƙara da cewa babu dalilin wannan gargaɗi saboda akwai cikakken tsaro a Abuja, “domin jami’an tsaro suna aiki ba dare ba rana domin tabbatar da daƙile dukkan wata barazanar tsaro.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada
  • Gwamnatin Neja ta rufe Jami’ar IBB bayan ɓarkewar rikici
  • Za mu ci gaba da tattaunawa da Iran kan yarjejeniyar nukiliya — Trump
  • Isra’ila da Iran sun ci gaba da musayar wuta duk da sanarwar tsagaita wuta
  • Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba
  • Gwamnatin Nijeriya ta yi wa Amurka martani kan barazanar tsaro a Abuja
  • Iran ta kama ’yan leƙen asirin Isra’ila 6
  • Iyalan Kanawa da aka kashe a Uromi sun zargin gwamnati da yin watsi da su
  • Iran da Isra’ila sun amince da tsagaita wuta —Trump
  • Trump ta ce Iran da Isra’ila sun amince da tsagaita wuta bayan harin Iran kan sansanonin Amurka