Yayin da ake cika shekaru 10 da kaddamar da dandalin hadin gwiwar Sin da kasashen Latin Amurka watau China-CELAC Forum, kafar yada labarai ta CGTN da hadin gwiwar jami’ar San Martin de Porres da cibiyar nazarin siyasa da tattalin arzikin kasar Sin ta Latin Amurka da jami’ar Santiago de Chile, sun fitar da wani sakamakon nazari da aka yi kan mutane 2,500 a fadin kasashe 10 na Latin Amurka.

Sakamakon nazarin ya nuna cewa, masu bayar da amsa sun amince da manufa da nasarorin da aka cimma na zamanantar da kasar Sin, tare da gamsuwa da dangantakar Sin da kasashen Latin Amurka. Al’ummar Sin da Latin Amurka mai makoma ta bai daya na kara samun goyon baya daga mutanen yankin Latin Amurka.

Kasashen Sin da na Latin Amurka dukkansu masu tasowa ne kuma muhimman abokan hulda dake hadin gwiwa bisa daidaito da moriyar juna da neman ci gaba na bai daya. Manufar zamanantar da kasar Sin ta ba kasashe a Latin Amurka wani misali mai daraja yayin da suke kokarin neman ci gaba. Nazarin ya nuna cewa, galibin wadanda suka bayar da amsa na da kyakkyawan ra’ayi game da kasar Sin, inda kaso 94.8 ke ganinta a matsayin wadda ta samu nasara. Kaso 85.9 kuma suna sha’awarta, sannan kaso 94.8 na kallonta a matsayin wadda ke da karfin tattalin arziki, sai kaso 91 da suka yi imanin cewa, tattalin arzikin kasar Sin zai ci gaba da habaka cikin lokaci mai tsawo.

A matsayinta na mai ingiza hadin gwiwar Sin da Latin Amurka, tasirin shawarar Ziri Daya da Hanya daya a kasashen Latin Amurka yana karuwa, kuma yadda masu bayar da amsa suke fahimtar shawarar, shi ma yana karuwa. A bayanin shawarar, masu bayar da amsa sun bayyana ra’ayinsu game da muhimman batutuwa 3 dake cikin yarjejeniyar shawarar, inda matsayin shawarar na samar da wani tsari da kasashe za su runguma domin inganta tattalin arziki ya samu goyon baya da kaso 55. Matsayinta na wani muhimmin abu da Sin ta gabatar domin kyautata tsarin jagorantar harkokin duniya ya samu kaso 54, yayin da burin Sin na hada gwiwa da sauran kasashe ya samu kaso 52.6. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: bayar da amsa

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Amurka Ya Yi Barazanar Aikewa Ukraine Makamai Masu Linzami Kirar Tomahawk

Shugaban kasar Amurka ya yi barazana ga shugaban kasar Rasha na aike wa Ukraine makamai masu linzami kirar Tomahawk

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce: Zai gargadi takwaransa na Rasha Vladimir Putin cewa: Akwai yiwuwar Ukraine za ta iya samun makamai masu linzami kirar “Tomahawk” idan Rasha ba ta kawo karshen yakin Ukraine ba.

Da aka tambaye shi a cikin jirgin Air Force One da ke kan hanyarsa ta zuwa haramtacciyar kasar Isra’ila da Masar da yammacin ranar Lahadi ko shi da kansa zai tattauna da Putin kan batun, Trump ya ce, “Yana iya magana da shi. Yana cewa: Idan ba a warware wannan yakin ba, zai aika wa Ukraine da makamai masu linzami na Tomahawk.”

Trump ya kara da cewa shugaban kasar Ukraine Volodymyr Zelensky ya bukaci makamai masu linzami na Tomahawk lokacin da suka tattauna sabbin makamai ga kasar ke bukata ta wayar tarho a ranar Asabar.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Trump, da Al’Sisi za su jagoranci taron zaman lafiya kan Gaza October 12, 2025 ‘Yan Kamaru na kada kuri’a a zaben shugaban kasar October 12, 2025 Wata Kotu a Faransa ta yi watsi da rufe wata makarantar musulmi a birnin Nice   October 12, 2025 Gwamnatin Cuba ta yi watsi da zargin da Amurka ke yi na hannu a yakin Ukraine October 12, 2025 Arachi: HKI Ba Abar Amincewa Ba Ce, Falasdinawa Su Yi Hattara October 12, 2025 Iran Ta Yi Allawadai Da HKI Kan Hare-Haren Da Take Kaiwa Kudancin Lebanon October 12, 2025 An Gudanar Da Taron ‘Farkawar Musulmi’ A Nan Tahren Inda Aka Tattauna Batun Falasdinu October 12, 2025 Amurka Da Masar Ne Zasu Jagoranci Taron Rattaba Hannu Tsakanin HKI Da Falasdin A Sharm Sheikh October 12, 2025 China Ta Sha Alwashin Maida Martani Kan Harajin Trump A Kanta Na 100% October 12, 2025 An Yi Girgizar Kasa Mai Daraja 5 A Ma’aunin Richter  A Kasar Habasha October 12, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hada-Hadar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso 4% Cikin Watanni Tara Na Farkon Bana
  • Shugaban Amurka Ya Yi Barazanar Aikewa Ukraine Makamai Masu Linzami Kirar Tomahawk
  • Zuwa Kofin Duniya: Za A Yi Ta Ta Kare A Nahiyar Afirka
  • Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa
  • Amurka Da Masar Ne Zasu Jagoranci Taron Rattaba Hannu Tsakanin HKI Da Falasdin A Sharm Sheikh
  • An Yi Musayar Wuta A Tsakanin Masu Tsaron Iyakokin Kasashen Afghanistan Da Pakistan
  • Yanayin Sashen Samar Da Gidaje Na Sin Ya Kara Inganta Tsakanin 2021 Zuwa 2025
  • An Gudanar Da Taron Hadin Kai Na Raya Albarkatun Kasa Tsakanin Sin Da Mozambique
  • Li Qiang Ya Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Koriya Ta Arewa
  • Wani Dan Majalisar Dokokin Kasar Iran Ya Ja Kunnen Amurka Kan Taba Jiragen Dakon Man Kasa