Majalisar Zartaswa ta Tarayya ta amince da kashe naira biliyan 2 da miliyan 300 domin sayo  na’urar binciken cututtukan zuciya (cardiac catheterization machine) a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sakkwato.

 

Ministan Lafiya da Jin Daɗin Al’umma, Farfesa Muhammad Ali Pate, ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai bayan zaman majalisar da aka gudanar a fadar gwamnati da ke Abuja.

 

A cewar ministan, wadannan kayan aiki na zamani za su taimaka matuka wajen aikin gano cutar da kuma warkar da cututtukamasu alaƙa da zuciya.

 

Ya bayyana cewa hakan  wani mataki ne na  gwamnatin tarayya don ƙarfafa ayyukan kiwon lafiya na musamman a yankin Arewa maso Yamma da kuma rage bukatar zuwa ƙasashen waje domin neman lafiya.

 

“Asibitin koyarwa na jami’ar  Sakkwato yanzu zai samu damar ba da kulawa ta gaggawa da ke ceton rai ga masu fama da cututtukan zuciya”.

 

Hakan na da matukar muhimmanci ga  jihar Sokoto  da daukacin yankin Arewa maso Yamma baki ɗaya, wanda zai dakile zirga-zirgar fita ƙasashen waje domin jinya ta hanyar ƙarfafa cibiyoyin kiwon lafiyarmu na gaba,” in ji Pate.

 

Ya ƙara da cewa wannan matakin yana cikin jerin shirye-shiryen da ake aiwatarwa don samar da kayan aiki na zamani a asibitocin koyarwa na tarayya domin bincike, magani da horarwa, bisa tsarin sauye-sauyen da ake yi a fannin lafiya karkashin jagorancin Shugaba Bola TinuTinubu.

 

Daga Bello Wakili

 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Lafiyar Zuciya Sakkwato

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Katsina ta amince da ƙidayar almajirai, makarantun Islamiyya

Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Radda ya bai wa Hukumar ƙididdiga ta jihar damar gudanar da ƙidayar almajirai da makarantun Islamiyya a jihar.

Babban jami’in ƙididdiga na jihar, Farfesa Saifullahi Sani wanda ya bayyana hakan a Katsina ranar Alhamis, ya ce maƙasudin gudanar da ƙidayar shi ne tsara dabarun inganta tsarin.

’Yan sanda sun kashe ’yan fashi da ƙwato makamai a Kaduna An tallafawa iyalan ’yan sanda da Naira miliyan N13.4m a Borno

Babban jami’in ƙididdigar ya bayyana hakan ne yayin wani muhimmin taro na yini ɗaya da masu ruwa da tsaki a jihar.

Sani ya ce, “Manufofin ƙidayar sun haɗa da samar da cikakkun bayanai na dukkan Makarantun Alkur’ani da kuma samar da cikakken tsarin yaran da ba su zuwa makaranta a jihar.

“Manufofin hakan su ne, a tabbatar da halin da ɗaliban suke ciki, don sanin halin da suke ciki, da samun cikakkun bayanai na malaman makarantun.

“Haƙiƙa wannan an yi shi ne don samun cikakkun bayanai na ɗalibai a fannin.

“Haka kuma don tabbatar da adadin ɗaliban da suka tsunduma cikin harkar bara a jihar da kuma taimakawa wajen fahimtar hanyoyin aiwatarwa a halin yanzu, gano giɓi da jagoranci wajen samar da matakan da suka dace.”

Ya bayyana cewa, sakamakon ƙidayar zai sanar da shiga tsakani da kuma fara ƙoƙarin da suka dace na sauya tsarin karatun Alkur’ani a halin yanzu.

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NDLEA ta kafa cibiyar kula da masu shaye-shaye a Yobe 
  • Gwamnatin Katsina ta amince da ƙidayar almajirai, makarantun Islamiyya
  • Gwamnatin Neja ta rufe Jami’ar IBB bayan ɓarkewar rikici
  • NAJERIYA A YAU: Yadda ‘Yan Najeriya Za Su Kula Da Lafiyar Jikin Su
  • Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC
  • Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci
  • Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato
  • Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida
  • Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba
  • Trump ya soki Iran da Isra’ila kan saɓa wa yarjejeniyar tsagaita wuta