Majalisar Zartaswa ta Tarayya ta amince da kashe naira biliyan 2 da miliyan 300 domin sayo  na’urar binciken cututtukan zuciya (cardiac catheterization machine) a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sakkwato.

 

Ministan Lafiya da Jin Daɗin Al’umma, Farfesa Muhammad Ali Pate, ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai bayan zaman majalisar da aka gudanar a fadar gwamnati da ke Abuja.

 

A cewar ministan, wadannan kayan aiki na zamani za su taimaka matuka wajen aikin gano cutar da kuma warkar da cututtukamasu alaƙa da zuciya.

 

Ya bayyana cewa hakan  wani mataki ne na  gwamnatin tarayya don ƙarfafa ayyukan kiwon lafiya na musamman a yankin Arewa maso Yamma da kuma rage bukatar zuwa ƙasashen waje domin neman lafiya.

 

“Asibitin koyarwa na jami’ar  Sakkwato yanzu zai samu damar ba da kulawa ta gaggawa da ke ceton rai ga masu fama da cututtukan zuciya”.

 

Hakan na da matukar muhimmanci ga  jihar Sokoto  da daukacin yankin Arewa maso Yamma baki ɗaya, wanda zai dakile zirga-zirgar fita ƙasashen waje domin jinya ta hanyar ƙarfafa cibiyoyin kiwon lafiyarmu na gaba,” in ji Pate.

 

Ya ƙara da cewa wannan matakin yana cikin jerin shirye-shiryen da ake aiwatarwa don samar da kayan aiki na zamani a asibitocin koyarwa na tarayya domin bincike, magani da horarwa, bisa tsarin sauye-sauyen da ake yi a fannin lafiya karkashin jagorancin Shugaba Bola TinuTinubu.

 

Daga Bello Wakili

 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Lafiyar Zuciya Sakkwato

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’in Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana Cewa: Iran Ta Cimma Matsayi A Yaki Kwanaki 12

Jami’in ma’aikatar harkokin wajen Iran ya jaddada cewa; Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta cimma babban matsayi a yakin kwanaki 12

Ali Baqiri Kani mamba a majalisar tsare-tsaren a ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta cimma babban matsayi a yakin kwanaki 12 da aka kwashe ana gwabzawa da yahudawan sahayoniyya.

Baqiri ya bayyana hakan ne a wata hira da aka yi da shi ta gidan talabijin a yammacin jiya Asabar cewa: Tabbas Iran ta cimma matsayi sosai a yakin kwanaki 12 da aka kwashe ana gwabzawa, yana mai jaddada muhimmancin diflomasiyya wajen tunkarar hare-haren da ake kai wa kasar, yana mai jaddada cewa: “Dole ne Iran ta mayar da martanin wuce gona da iri kan kasarta a fagen diplomasiyya zuwa wani lamari da duniya ta amince da shi.”

Har ila yau Baqeri Kani ya yi ishara da hadin kan kasa a matsayin mafi girman bayyanar da Iran ta taka rawa a wannan yaki yana mai cewa: Wannan hadin kai yana nuna irin gagarumin goyon bayan da jami’an diflomasiyyar Iran suka nuna.

Ya kara da cewa: Goyon bayan jama’a ga manufofi da matakan gwamnatin na iya taimakawa wajen cimma manufofin diflomasiyya. Har ila yau ya bayyana cewa: A halin da ake ciki yanzu, kasashen yammacin duniya, baya ga Amurka, sun taka rawa wajen tallafawa hare-haren da aka kai wa Iran.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Jami’an Tsaron Iran Sun Murkushe ‘Yan Ta’adda Kan Ofishin ‘Yan Sanda A Kudu Maso Gabashin Kasar August 10, 2025 Jefa Agajin Abinci Ta Sama A Zirin Gaza Ya Janyo Shahadan Falasdinawa 23 Tare Da Jikkata Wasu 124 August 10, 2025 Tehran Times: Mai Yiwuwa Iran da Amurka su koma Tattaunawa August 10, 2025 Tel Aviv: Dubban yahudawa sun yi zanga-zangar adawa da yakin Gaza August 10, 2025 Welayati: Makircin Amurka da Isra’ila na kwance damarar Hizbullah ba zai yi nasara ba August 10, 2025 Birtaniya: ‘Yan sanda sun kama akalla mutane 365 a zanga-zangar goyon bayan Falasdinu August 10, 2025 Venezuela: An dakile yunkurin kai wasu munanan hare-hare a cikin kasar August 10, 2025 Pezeshkiyan Ya Yabawa Yan Jarida A Ayyukansu A Yakin Kwanaki 12 August 9, 2025 Yansanda A Burtaniya Ta kama Mutane Fiye Da 200 Masu Goyon Bayan Falasdinawa August 9, 2025 Iran Ta Yi Maraba Da Sulhuntawa Tsakanin Armenia Da Azerbaijan August 9, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • UNICEF Da Gavi Sun Bada Na’urorin Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Ga Jihar Kano
  • U Reporters Sun Gudanar Da Taron Wayar Da Kan Jama’a Game Da Shayarwa A Kano
  • Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Kaddamar Da Tantance Malamai Da Ma’aikatan Lafiya
  • ’Yan bindiga sun kashe gomman mutane a ƙauyukan Sakkwato
  • Jami’in Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana Cewa: Iran Ta Cimma Matsayi A Yaki Kwanaki 12
  • Jami’an Tsaron Iran Sun Murkushe ‘Yan Ta’adda Kan Ofishin ‘Yan Sanda A Kudu Maso Gabashin Kasar
  • Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar
  • An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja
  • Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza